Chapter 68
Chapter 68
ke cikin wannan raunnaniyar zuciyar tasa, a hankali ya lumshe idonsa, hakan ya sa ita ma Mishal ɗin lumshe nata idon. “Hafsat!” Ya kira sunan nata a hankali. “Umm... um... umm” Ta amsa idon nata a lumshe, hannunta na dama dake cikin nasa ya ɗora a saitin zuciyarsa, kusan a tare suka buɗe idanuwansu. “Kin ji yanda take bugawa ba?... Da ko wani bugu da take ta na bugawa ne da sunanki, da kowani bugu da take tana bugawa ne da sanki, Hafsat... I... Love... Youuuu!” Ba shiri Mishal ta matse gaban rigarsa da hannunta dake kan setin zuciyarsa, saboda yanda kalaman suka saka jikinta rawa. Ba ta za ta ba ta ji hannun Kuliya ya kewaye waist ɗinta ta baya, sannan ya matso da ita jikinsa sosai, hakan ya sa ta buɗe idonta ba shiri. “Answer me Hafsat, did you love me?!” Ya tambaya ya na goga lips ɗinsa a kan nata, hakan ya sa Mishal ɗago ɗayan hannun nata, tare da ƙara matse gaban rigarsa. Sakan ɗay... Biyu... Uku... *Washe gari...* *07:10 AM.* Mishal ta rufe lunchbox ɗinta, bayan da ta gama jera abincinta a ciki, sanye take da complete uniform ɗinta, ta juya za ta fita daga kitchen ɗin idonta ya sauƙa a kan flask ɗin abincin Kuliya. Kuliya?!, Sunan ya maimaita kansa a cikin ranta, nan take abun da ya faru a jiya ya dawo mata. A jiyan bayan shuɗewar sakan uku, muryarsa ta katse shirun dake wanzuwa a falon. “Na ba ki daga yanzu zuwa gobe da safe, ki yi tunani a kai” Abun da yace kenan, kafin ya saketa a hankali, ya ɗauki plate ɗin da ya ci abinci ya nufi kitchen, hakan ya bata damar faɗawa ɗakinta da gudu, ta sakawa ƙofar sakata. har gari ya waye ta na saƙawa da kuncewa. Ko da safe da ta tashi ayyukanta ta shiga yi cikin gaggawa, don so take ta yi sauri ta kammala abun da za ta yi don ta bar gidan kafin ya fito, hakan da ta tuna ne ya sa ta zabura za ta bar kitchen ɗin, sai dai kuma fatan ta bai cika ba, don a dai-dai lokacin ƙofar kitchen ɗin ta iyo ciki, Kuliya ya shigo, kamar kullum sanye cikin baƙaƙen kaya. Kallonta yake cikin wata iriyar siga da Mishal ba ta san ta inda za ta mata fasarra ba, hancinta ta ja, sakamakon murar da ta kamata a jiya, ta haɗiyi yawu da ƙyar. Numfashinta ya kusa ɗaukewa a sanda ya tsaya a gabanta. “Har kin shirya?” Ya tambaya ya na kallon hancinta da ya yi jajir, da alama dai mura take. “Eh” Ta amsa masa cikin muryar me mura. “Ba ki da lafiya?” Ya tambaya ya na duban yanayinta, da sauri ta girgiza masa kai, sai kuma ta gyaɗa kan nata tana shaƙar ƙamshin turarensa da duk murar da take ba ta hanata jinsa ba. Wani sauti ta ji me kama da na murmushi, hakan ya sa ta kalli fuskarsa da sauri, kuma sai ta ga da gaske ne, Kuliya ne yake mata murmushi, wani abu sabo, wani abu da za ta cewa ba ta taɓa ganinsa a zahiri ba. Kuma murmushin da ya yi sai ya ƙara bayyana mata kamarsa da Adawiyya, haka zalika murmushin nasa ya ƙara bayyana kamar da suke da ɗan uwansa... Tunaninta ya katse a sanda ta ji sauƙar tafin hannunsa a kan fatar wuyanta, wannan sanyin ya shiga bi ta jijiyon jikinta, hakan ya sa ta ɗan ɗauke numfashinta na wasu sakkani, kafin ta dawo da shi ta na jansa da sauri-sauri. “Har da zazzaɓi kenan?” Ya tambaya ya na dawo da hannun nasa goshinta. “Zan bawa Ibrahim (Drivernta) maganin mura ya kawo miki” Da sauri ta gyaɗa masa kai tana jan hanci. “Ban manta ba... Mecece amsata?” Ta kalli fuskarsa, amma sai ta kasa cewa komai, bakinta ya mata nauyi, kamar wanda ta haɗiyi dutse. A hankali Kuliya ya ƙara matsawa kusa da ita, sannan ya saka hannunsa na dama ya kewaye ƙuginta, ya haɗeta da jikinsa ya na ɗaga kafaɗarsa ta dama, hakan ya sa Mishal rintse ido tana kawar da kanta, hannunsa na hagu ya sa ya kamo haɓatar ya juyo da fuskarta. “Look at me!” Sai ta buɗe idon nata tana kallon fuskarsa. “Did you love me?” Saboda abun da Mishal take ji ba ta san sanda ta shiga gyaɗa masa kanta da sauri ba kuma ta gyaɗa ya fi sau biyar. “Kin tabbatar?” “E... Eh!” Kalaman sun yi wa Kuliya daɗi, hakan ya sa ya yi wani irin murmushi da sai da ya bayyana haƙoransa, kafin ta ɗauke hannunsa daga kan haɓarta, ya dawo da shi gefen fuskarta, yana shafawa a hankali. “I love you Teddy Bear!” Ya na kaiwa ƙarshen maganar, ya raba leɓensa biyu, sannan ya sa nata na ƙasa a tsakiya, kafin ya haɗe bakinsa da nata gaba ɗaya. Abun da ya yi ya sa Mishal ɗaga ƙafarta sama, sannan ta dunƙule hannayenta a kan ƙirjinsa. Ba ta san ma me yake faruwa ba, ba ta san me ake yi a duniyar ba, ba ta san me yake wakana a kitchen ɗin ba, abu ɗaya ta sani, shi ne ita ce riƙe a hannun Kuliya, yayin da hannunsa na hagu ke riƙe da gefen fuskartsa na dama, bakinsa kuma cikin nata, ya na aika mata da wani laffiyayyen kiss. A lokacin ne aka ƙwanƙwasa ƙofar falon ta can compound, sannan muryar Ibrahim ta biyo baya. “Ranki ya daɗe lokaci na ƙurewa, ki fito kar mu makara!”.😁 #Labarinsu #SalmaAhmadIsah #TaurariWriters ••••••••••• *LABARINSU* *©SALMA AHMAD ISAH* *TAURARI WRITERS* *17* ~~~ *Time moves slower when you miss somebody.* *** *T.O.C Douglas Crescent, Kaura District, Game Village, Abuja* RAJA POV. Yau zaune yake a tsakar gidan, ya na kallon yanda iska ke busawa ta na kaɗa bishiyoyin farfajiyar gidan, a zahiri kenan, amma a baɗini sam ba su yake kallo ba, tunaninsa na can wata uwa duniya, yayin da shi kuma yake wannan duniyar, sati uku kenan rabonsa da farin ciki, sati uku kenan rabonsa da walwala, sati uku kenan rabon da wani abu na fara'a ya gifta a fuskarsa, sati uku kenan da shigar yaruwarsa cikin yanayin tashin hankali da zullumi, sati uku kenan da komai na rayuwarsa ya yi juyin waina a tanda, kuma a cikin wannan satin ukun ne rayuwarsa ta shiga kwale-kwalen katako, wanda ke tangal-tangal a cikin kogin da ke cike da yunwatattun kadogi, a cikin sati ukun nan komai ya cakuɗe masa. Kuma duk hakan ya samo asali ne ta sana diyyar ɓatan Rabi'a, don zuwa yanzu ya na da tabbacin Rabi'ar ba kawai makarantar ta dena zuwa ba, ɓata ta yi, amma abun tambayar a nan shi ne, ina ta je?, ta na ina ?, shin ta na hannu na gari?, ko a'a, idan ya yi zurfi a tunani irin wannan sai kansa ya kulle, kamar wata ƙofar da aka garƙame da makulli. “Raja!” Ya ji muryar Jagwado na kiran sunansa, amma sai ya ƙi juyawa bare ya amsa. “Raja!” A wannan karon muryar Alandi ce ta yi kiran, kuma a yanzun ma bai amsa ba. Kusan a tare suka zauna a kusa da shi, Zuzu a ɓangaren dama, Alandi a kusa da Zuzu ɗin, Rhoda ta zauna a gefensa na
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112