Chapter 5
Chapter 5
bata wuce wata biyar ba. Su ne zaune a kan danning table. Wanda ke shaƙe da kayan buɗe baki kala-kala.Da alama jiran kiran sallah suke, dan ƙiris ya rage a kira sallahr. Ƙofar ɗaya daga cikin ɗakunan falon ce ta buɗe, farko keken guragu ne ya fara bayyana, zaune a kan keken kuma, wata matashiyar yarinya ce, wadda ba za ta wuce 9yrs ba. Kallo ɗaya zaka mata ka ga nakasarta, dan bata da hannaye gaba ɗaya, sannan kanta a langwaɓe gefe guda, bakinta nazubar da yawu. Mishal ce ta biyo baya,wadda ita ce ke turo keken, sanye take da wata farar linen tunic dress, da kaɗan rigar ta sauƙo gwiwarta, ga kuma rigar ko hannu bata da shi, kanta babu ɗankwali kamar yanda ta saba zama, gashin kanta tifke cikin braid(kalaba) guda ɗaya, ta saka hair band daga sama. Gaba ɗayansu suka kalli wurin, kuma daga Hajjara har mijin nata basu ɗauke idonsu a kansu ba har suka ƙaraso danning area ɗin. Kujera ɗaya Mishal ta kawar ta mayeta da keken Firdaus, wadda take kira da Daala. Sannan ita ma ta samu kejera kusa da ita ta zauna, sai da ta ɗauki tissue ta gogewa Daalan yawun da ya zubo mata sannan ta juyo tana kallon mutanen dake kan danning ɗin. Hajjara ta kawar da kanta tana taɓe baki, Allah ya sani, har cikin zuciyarta bata san Mishal, wata ƙila dan igiyar aurenta da ta taɓa zama sanadiyyar tsinkewa ne, ko kuma dan rashin kunyar da take mata. Mishal ta kalli yayanta,wanda shi ma ita yake kallo, hannunta na dama ta ɗago, wanda ke riƙe da envelop, ta miƙa masa. Abubakar ya girgiza kansa, ya san duk yanda aka yi wani laifin ta aikata, ba yau ta saba kawo takardu irin wannan ɗin ba, hasalima suna nan tili guda yana ajewa, dan sun ma fi yawan report ɗin ta na makaranta da take kawowa. Abu ɗaya ne yasa ba zai cireta daga makaranta ba kwata-kwata, hazaƙarta ce tasa hakan, dan ba ma shi ba, hatta da makarantar suna tinƙaho da ita, gashi de ba wasu shekaru ne da ita ba, amma girman jikinta ne zaisa ka zaci wata babbace. “Me kuma kika yi ?” Ya tambaya yana karɓar envelope ɗin, kanta ta sunkuyar, tana wasa da yatsunta. Murmushi kawai ya yi a sanda ya buɗe ya karanta, dan bi da bi ya gama haddace kalaman da ke ciki, saboda a kullum abu iri ɗaya suke turo masa tun tana junior. Ya rasa irin abunda ke damun ta. “Hammad yace min yau baki yi azumi ba, bayan shi ma yau yana yi” Ta ɗago da kanta ta kalli Hammad ɗin dake gefen uw*rsa, kamar yanda bata san uwa*r yaron shi ma haka ta tsaneshi, dan kaf halayen uw*rsa babu wanda bai ɗauko ba. “Saboda makarantar da nake zuwa ne...” “Makaranta sai ta hanaki azumi?” Sai kawai ta miƙe tsaye tana faɗin. “Bari na je waje.....” Bayanta ya bi da kallo yana mamakin halin yarinyar, du-du-du ba za ta wuce 17-16 ba, har yau yana tuna yanda ya ɗauketa da hannayensa ranar da aka haifeta, da kuma irin maganar da mahaifiyarsu ta masa a wancan lokacin. _“Sadiq, ka kula da ita, nasan za ta tashi cikin maraici, bata da kowa sai kai, kada ka danƙa renonta a hannun kowa, ciki kuwa harda Amma (tana nufin mahaifiyarta), ka kula da ita, ka kula da ita......”_ Kuma kalamanta na ƙarshe kenan, a kan idonsa a ka shiga da ita ɗakin tiyata. sai kawai fito masa aka yi da jairiya, aka ce ta haihu, amma ta rasu sai dai babyn da ta haifa. “Wai haka za'a zuba ido ana kallon yarinyar nan tana abinda take so?.....” Hajjara ta faɗi a ƙufule, dan Allah ya sani ta gaji da halin yainyar, kuma da ma tun sanda ta ɗora idonta a kan yariyar ta washeta. “Me ta yi ?” Ya furta hakan cikin halin ko in kula, yana ninke takardar da Mishal ɗin ta bashi. “Jiya fa na yi baƙi, baka ga rashin kunyar da ta min a gabansu ba” “Yarinta ce take damunta, idan ta girma za ta dena” Haushi kamar ya kashe Hajjara, dan dama abin da ya saba faɗa mata kenan, a duk sanda ta kawo masa ƙarar Mishal ɗin, yau ɗin ma tsautsayi ne yasa ta kawo ƙararta, a ranta ta yi ƙwafa, Allah ya kawo ranar da za ta ga bayan yarinyar nan. Idonta ya sauƙa a kan Daala dake ta zubar yawu, ita ma yarinyar Hajjaran take kallo. Tawarta ɗaya kenan a duniya, wannan yariyar da Allah yasa ta haifota a nakashe, kuma nakasar yariyar yasa ta gujeta, babu wani abu dake shiga tsakaninta da yariyar irin na uwa da 'yarta, Mishal da Naani ɗin da Abubakar ya ɗauko su ne ke kula da yarinyar har wa yau. Mishal na fita daga falon gidan BQ ta wuce, dan bata da wurin zama a gidan da ya wuce BQ ɗin, in baka sameta a BQ ba zaka sameta tare da Daala suna wasa, dan Allah ya ɗora mata ƙauna da tausayin yarinyar. Ganin yanda Hajjara ke bagarar da lamarin yarinyar saboda nakasar dake tare da ita, ita kuma Allah ya hallici zuciyarta da wani irin tausayi, kuma tausayin ne ke sakawa bata da aminan hira a gidan sai masu aikin gidan. A bakin ƙofar BQ ɗin ta tsaya, tana ƙare musu kallo. Mutum biyar ne zaune a kan bujukura. Ladi, wadda ita ce ke kula da Daala sai mijinta Malam Audu, wanda ke musu gadi, sannan Khalifa, ɗan Mama Ladin na farko, wanda shi ne yake musu sharar garden da ta compound da ma aike idan ya taso, sai Shatu 'yar Mama Ladin ta biyu, sai autar Mama Ladin wato Ummul. A taƙaice de duka ahalin Mama Ladin ne, waɗan da suka kasance ahalinta ita ma, dan bata da wurin zuwa da ya wucenasu, Shatu kuma ita ce wadda zata iya kira da ƙawarta, Mama Ladi ta zame mata uwa. “Ah-ah, Hafsatu, ƙaraso mana” Sai ta yi murmushi har ƙarafunan braces dake saman haƙwaranta na bayyana, tana ci gaba da kallonsu, su ma sai hadaniyar haɗa kayan shan ruwansu suke, a hankali ƙafafunta da babu takalmi suka ci gaba da takawa har zuwa kan bujukurar. Guri ta samu kusa da Shatu ta zauna. “Yau kin yi azumi ?” Mama Ladi ta tambaya, yayin da take juye tiyara a cikin wata doguwar roba, Mishal ta girgiza kanta. “Ban yi ba” “Haba uwata, sau nawa zan faɗa miki cewar kin isa azumi ?, bai kamata ace ki na shan azumu ba gaira ba dalili ba” Cewar Malam Audu yana aje radion hannunsa. “Rabu da ita Baba, ai kullum gaya muku nake cewar yarinyar nan raguwace, amma bakwa yarda” Cewar Khalifa. Mishal ta turo baki gaba tana sosa kanta. “Allah ni ba raguwa ba ce, a class ɗin Kungu fu ɗinmu fa kullum ni nake zuwa a farko, kuma watan da ya auce ma saida na karya wani malamin mu....” Hannunta ta kai ta rufe bakinta, sakamakon suɓul da bakan da ta tuna cewar ta yi, dan tasan yanzu Mama Ladi za ta shiga mata faɗa. “Kema kin san cewa ba dai-dai kika yi ba kenan, shi yasa kika rufe baki” Cewar Mama Ladin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112