Chapter 16
Chapter 16
MISHAL POV. Zaune take a ɗakin da yake a matsayin nata. Don ba yau suka saba zuwa Maidugurin ba, hasalima suna zuwa akai-akai. Kuma idan sun zo ɗin a babban family house ɗinsu suke sauƙa. Duk da kasancewar gobe sallah, amma gidan har yanzu be rabu da zuwan baƙi ba. Tun daga hayaniyar dake tashi a gidan za ka gane hakan. Ba su dameta ba, Don Kullum ba ta fita, tana ɗaki, bata san ta fita su haɗu da Yazid. Yazid?, wani mutum da ya so lalata mata rayuwa, wannan mutumin da duk duniya bata tsani wani mahaliƙu kamarsa ba. Shi ne wannan mutumin da a sanadiyyarsa ta gamu da ciwon hysterian da take da shi a yanzu. Kuma dan abun a family ya faru, haka aka rabu da shi ya ci gaba da yawonsa. Yana shiga cikin 'yan uwa kansa ɗage a sama, kamar bai aikata komai ba. Ita kuma da aka yi ƙoƙarin cutarwa ita ce ke ɓuya, ita ce ke ɓoye kanta da barin shiga dangi, har yanzu gani take kamar idan ta idan ta shiga cikinsu suna ganin wannan tabon a jikinta ne. Duk da Allah bai sa ya haike matan ba, amma tana jin zafin abinda ya mata a ranta. A duk sa'ar da za ta ganshi ji take kamar ta fasa ihu, a wasu lokutan ma ganin nasa kawai shi ne ke tada mata ciwonta. Ta ɗan ja gutun tsaki tana ci gaba da buɗe littattafanta. Ita ta tsani aikin makaranata, dan de ba ta san ɗan uwanta ya yi asarar kuɗin da yake kashewa a kan makarantar ta a banza, amma da ba za ta na maida hankali ba. Gashi dai hutun sati ɗaya a ka bayar, saboda ba ƙarshen term ba ne, a tsakiyar term aka basu hutun, amma sai da suka haɗo su da holiday project. Kuma tun barowarsu Abuja abun da take ta ƙoƙarin yi kenan. Amma har yanzu ta kasa gamawa. Ta kuma jan wani tsakin tana ture littatafan, duk aikin ya gundureta, fita take san yi, bata san zaman gidan gaba ɗaya. To amma ta fita ta je ina ?, ta san in ma fitar ce ba za'a barta ta fita ita ɗaya ba, dole za'a haɗata da wani. “Baby!” Kamar daga sama ta ji muryarsa yana kiran sunanta, sunan da kaf duniya babu me kiranta da shi sai 'yan gidansu. Tasan da cewa za su zo, amma ba ta san cewa yau za su zo ɗin ba. Da sauri ta miƙe ta fita daga ɗakin, a falo ta same shi yana ta nemanta. Yana ganinta ya sakar mata wani kyakkyawan murmushin. Da gudu ta ƙarasa kusa da shi, kuma tana zuwa jikinsa ta ɗale shi, duk tsayinsa amma saida ta riƙe masa wuya. “Tun sanda muka zo nake ta nemanki” Wannan dakakiyar muryar tasa ta faɗi. Ta yi kewarsa da ma duk wani ɗan gidansu, dan za ta iya cewa duk familynsu babu wanda take so kamar 'yan gidansu, duk da su ma a Abuja suke da zama,amma bata gajiya da ganinsu. Sunansa Arman, ɗa ne a wurin cousin ɗinta Nimra, wadda ta kasance soja me riƙe da muƙamin general na nigeri. Yaranta uku Arman, Iqra sai Ijaz, kuma gaba ɗaya yaran nata sojoji ne. Wani abu dake ƙara burgeta da gidansu kenan. “Ina Iqra da ijaz?” Ta tambaya tana sakinsa. Kanta a sama wurin kallon fuskarsa, sbd tsayin da ya fita. Kasancewar shi dogo ne, ita kuma gata ba wani tsayi gareta ba. “Suna waje, har da su Ammy muka taho” Zuciyarta kamar ta fito waje don murna, Allah ya dubeta yasa ba za ta yi bikin sallah lami ba, dan tunda har duka mutanen gidansu suka zo, to shikenan, matsalarta ta zaman kaɗaici ta yanki. *Unguwar Madallah, Suleja, Niger State* *07:44am* RABI'A POV. Ba ƙaramin farin ciki take ciki ba, kallo ɗaya za ka mata fahimci hakan, saboda daga kun haɗa ido za ka ga ta maka murmushi, duk da dama ita gwanarsa ce. Amma na yau ya fi na kullum. Jin kanta take kamar kowa, yau Allah yasa ita ma ta saka sabon kayan da za ta tafi idi da shi. Saɓanin sauran shekarun da ta shafe a gidan, a da sai dai Saratu ta bata kunce ta saka. Amma yau ita ma gata da nata sabon kayan, sai dai duk da haka bata da takalmin sakawa, shi yasa Saratu ta bada ɗaya daga cikin nata, Da murnarta ta zangari takalmin ta saka. Tun da ta fito daga wanka ta saka kayan Mama ke binta da kallo, amma ba ta ce komai ba, har suka shirya suka fito dan tafiya wurin idi. Rabi ba ta san sanda Mama ta dawo gidan ba, ita dai kawai ta farka ta ganta. Kuma ba ta ce komai ba, ta ja bakinta ta yi shiru, tun da har uw*rta tasan abin da take. A bakin ƙofar ɗakinsa suka ga babansu, kowa a cikinsu ya wani ɗauke kai babu ma mai shirin gaishe da shi, sai Saratu da ita, kuma shi ma bai wani amsa musu da mutumci ba, sama-sama ya amsa su. Ita kuma Rabi ba ƙaramin mamakinsa take ba, kusan kwanansa huɗu baya gidan, ko jiya har suka kwanta ba ta ga dawowarsa ba, wata ƙila ma da asuba ya dawo, don ba ƙaramin aikinsa ba ne. Mutumin da ya taɓa kawo karuwa cikin gidan matarsa ta auren sinnah, ai fiye da haka ma zai aikata.. “Ah-ah, Karfa, a ina kuma kika samo sabon kaya ?, in ji dai ba sata ki kai ba?” Muryar Habiba ta katseta, hakan yasa ta juyo da sauri ta kalleta. Rabi ta tsorata, dan jiya basu san an bata wani kaya ba, tana shigowa da ahi ɗaki ta shige, Anti Saratu kawai ta nunawa. “Saurayinta ne ya kawo mata, ba sata ta yi ba” Saratu ta bata amsa. “Sh*iya munafuka! Ashe jiya da kika je siyan katin tsayawa ki kai a lungu ya gama lalube ki sannan ya baki kaya?” Habiba ta faɗi cikin kama baki. “Ai ni na jima banga baƙar munafuka irin wannan yarinyar ba, kin ga fa jiyan da ta dawo, ɓoye kayan ta yi a cikin hijabinta, dan kada mu gani” Mama ta faɗi tana aika mata harara. “Ya isa haka dan Allah, to duk sharrinku a ƙofar gida ya bata, da za ku ɗorawa marainiyar Allah shari, dan Allah Umma ku riƙa duba baya, idan an giram a san an girama” “Kan abu ta kaza-kazacan!, Saratu! Ni ki ke faɗawa irin waɗanan maganganun ?.....” Sararu ta juyar da kanta gefe daga barin kallon Umman, ta kalli Rabi wadda hawaye suka wanke mata fuska tun a sharin farko da aka laƙa mata. Hannunta ta ja suka fita daga gidan, dan ta ga kamar su basu da niyyar zuwa idin, su da suke da niyya gwara su yi sauri, don kada su rasa. Da sauri Ɗan Lami ya bi bayansu, dan ko ba komai yasan akwai 'yan kuɗaɗe a hannun Saratu, shi kuma kuɗaɗen da ya ara sun ƙare kaf, bai ta shi da ko sisi ba. Kuma gashi yana san zuwa idin, ko ba komai Saratun za ta masa kuɗin babir. “Umma da alama fa sai kin ɗau mataki...” Cewar Mama. “Ni kuwa na ga hakan, kada
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112