Chapter 29
Chapter 29
da sakan ɗaya idanuwanta sun kasa barinsa ya huta, tunani barkatai yake a kanta. Ya kasa gane kan marsalar da ta samesa, yasan cewa shi bai taɓa samun kansa a cikin irin wannan halin ba. Bai taɓa so ba, bai san ya yake ba, bai taɓa kusantar inda yake ba, bai taɓa budurwa ba ma, balle yace ya taɓa sanin kalar yanda so yake. Amma a kallon farko da ya mata wani abu a kanta ya samu gu ya yi zaman darshan a zuciyarsa. Kuma sam ba ya jin zai bar hakan ta faru, zai yi duk yanda da zai yi wurin ganin hakan ba ta faru ba. Haba!, Shi ne fa?, ALIYU ZAID BICHI?, Shi ne KULIYA manta sabo, wanda ba ya ɗaukar raini duk ƙanƙantarsa. Abun da tai masa rannan ya dawo tunaninsu, yanda wutar masifa ke ci a idonta, a lokaci guda kuma sai ya ga mamaki ya maye wannan masifar, bai san mamakin me take ba, wata ƙila ganin girmansa ne ya sa ta shiga mamakin, ko kuma wani tunani ne ya haska a cikin kanta, amma dai koma menene shi ba zai bar abun da ke kai kawo a cikin kansa ya auku ba, don ya sani, hakan shi ne zai zame masa babban kuskure a rayuwarsa. Soyyaya tsakaninsa da ƙanwar abokinsa, no way!. Abinda bai sani ba shi ne, ɗan adam ba shi da dama, ko iko na sauya ƙaddararsa zuwa yanda yake so, Allah shi ne wanda yake jujjuya ko wani irin lamari. Sannan kuma wannan ƙaddarar dake shirin faruwa kwanaki kaɗan, ita ce za ta ƙaryata wannan zancen nasa, ta murmushe zancen nasa har garinsa. #Labarinsu #SalmaAhmadIsah #TaurariWriter ••••••••••• *LABARINSU* *© SALMA AHMAD ISAH* *TAURARI WRITERS* *08* ~~~ *You deserve a love that goes to war alongside you, not against you* -Heart spekeaks- *** KULIYA POV. _🎶What should i do?_ _What should I do when we come face to face?_ _Should I cut my fingers while admiringly glancing at your beauty,_ _Like Qibdiyyat when the greatly admired Joseph?_ _Or Should I abnegate your humanhood by saying that you're a noble angel and exalt your creator?_ _How should I be in that day?......🎶_ A hankali waƙar what sould i do? ke tashi daga mpn motar Sharon, wadda Nura Ismail Abou Othaymeen ya rera. Tayoyin matar na garawa a kan titi, yayin da Sharon ke zaune a mazaunin driver, shi kuma Kuliyan na zaune a gefenta yana kallon hanya. “Ina muka yi sir?” Ya juyo ya kalleta, sannan a hankali ya ɗaga kafaɗarasa ta dama. Yana mayar da dubansa gefen hanya. “Gidan Anna” Ya amsa mata a taƙaice, kuma daga hakan bai sake cewa komai ba, har suka iso gidan. Ita ta zaune a mota shi kuma ya fita ya shiga cikin gidan. Babu kowa a falo, dan haka kansa tsaye ya nufi ɗakinta. Tsaye take a jikin loka, ba zai iya cewa ga abinda take ba, amma ya ga sanda wani abu mai kama da farin ciki ya wulƙa ta cikin idonta, a sanda ta yi arba da shi. Kansa ya sunkuyar ƙasa, kafin ya ci gaba da takawa zuwa gabanta. Yana ƙarasawa ya rungumeta. Anna ta rintse idonta, tana jin ƙwalla na shirin zubo mata, ba ƙaramar azabtuwa ta yi ba da hana kanta zuwa duba shi, sai dai ta yi hakan ne kawai don ta ganar da shi kuskurensa. Ba wai dan ba ta san ganinsa ba. Dan Allah ya ɗora mata san Kuliya tun ranar da ta fara ɗora idonta a kansa. Ranar ita ce ke da dutyn yamma. Ta na shara a gidan marayun da ta samu aiki, wanda ke garin kano, a lokacin tana cikin matsananciyar buƙatar kuɗi. Hakan yasa a sanda aka mata tayin aikin ta karɓa ba tare da wani tunani ba. A garden ta ga wani yaro zaune kan duwatsu, ya ba ta baya, hakan yasa ba ta kalli fuskarsa ba. Kuma ganinsa a wurin ya ba ta mamaki, don a lokaci irin wannan yaran gidan ba sa zama a ko ina da ya wuce islamiyya, don lokacin ɗaukar darasi ne. Kuma tasan da cewa sauran yaran yanzu haka suna can, amma to wannan me yake a nan. “Kai yaro!, me kake a nan ?” Ta tambayi abun da ke yawo a cikin kanta, a sanda ta ƙarasa kusa da shi, ɗagowa ya yi da kansa ya kalleta. A kallo ɗaya da ya yiwa matar ya ji cewar zai iya yarda da ita. Saboda tun bayan zuwansa gidan marayun bai ƙara yarda da kowa ba, ba ya shiga cikin sauran yaran gidan, ba ya cin abinci tare da su, ba ya walwala, ba ya komai, sai tunanin ɗan uwansa da ya cika zuciyarsa. “Ka na jin yunwa ne ?” Annan ta kuma tambaya a wancan lokacin, sai ya girgiza mata kai. Ita kuma sai ta gyaɗa kanta, don ta fahimce shi, da alama sabon zuwa ne, kasancewar ba ta taɓa ganinsa a gidan ba, kuma rashin sakewa na faruwa da sabbin zuwa gidan. Hakan yasa ta zauna kusa da shi, ta na jingine tsintiyar hannunta a jiki wata bishi. “Kana ji ko!, ban san me yasa ka zo nan gidan ba, amma ina fatan ka ɗau haƙuri, ka dangana da rashin da ka yi, dan nasan duk wanda ya zo nan to ya yi wani rashin ne... Idan ka kwantar da hankalinka, ka saba da kowa a nan ka ji?” Maganarta da shi ke nan a wancan lokacin. A yanzu kuma sai ta ɗago shi daga jikinta tana kallon fuskarsa. “Anna i am so sorry, ba zan sake ba...” Ya zaɓi ya bata haƙuri, dan yasan fushi take da shi, Annan ta kai hannu ta riƙe fuskarsa. “Ka kiyaye Aliyu, kasan da cewa ba mu da kowa sai junanmu...” Ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, sannan ya gyaɗa mata kai. Daga bakin ƙofar ɗakin, Siyama ta saki murmushi, haɗi da ajiyar zuciya, jin cewar masoyinta na cikin ƙoshin lafiya, a cikin kwana huɗun duk sanda za ta tambayi Anna game da shi ba ta bata amsa, sai dai ta yi banza da ita. Ita kanta ta san cewar ta na cikin tashin hankali, dan har watq ƙwarya-ƙwaryar rama ta yi, ramar rashin sanin halin da abun santa ke ciki. Ta kuma yin wani murmushin, ta na karanta wasiƙar jaki, kanta take hangowa a tsakiyar hannayen Kuliya, wani mafarki da ta saba yinsa a farke. Hannunta na dama ta kai ta ɗan daki goshinta, sannan ta bar ƙofar ɗakin, ranta wasai. *No.234, Efab Estate, Gwarinfa, Abuja* MISHAL POV. Zaune take a falon gisansu, ta na rubuta assignment ɗin da aka basu yau, yayin da Daala ke zaune a gefenta, ta na yi ta na ɗan yiwa Daalan hira. Takun da ta ji daga kan stairs yasa ta kalli wurin, ganin Hajjara ce yasa ta sakar mata murmushin mugunta, irin wanda take mata a duk sanda za su haɗa ido a kwanakin nan. Sannan ta ci gaba da rubutunta. Wani malolon baƙin ciki ya tokare maƙoshin Hajjara, tun bayan ranar da suka dawo daga asibitin nan Abubakar ya hau fushi da ita. Sai da ta haɗa shi da kawunsu sannan ya saurareta, ba su shirya ba sai da ya bar mata kakkauran warning a kan Mishal. A ranta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112