Chapter 51
Chapter 51
a cikin jikinsa, da yanda damuwa a kulawa suka bayyana ƙarara a cikin muryarsa, abun ya burgeta ya kuma bata mamaki, ba ta taɓa ɗaukan cewa Kuliya na ɗaya daga cikin irin waɗanan mutanen ba. Kuliya ya juyo ya kalli side ɗinta a hankali, akwai wani abu da yake buƙata a tare da ita, ba komai ba ne face son sanin alaƙarta da wannan me kama da shi ɗin, ya na son ya san inda ta san yarinyar, amma idan ya tambayeta kai tsaye ba lalle ta ba shi amasa ba, ya zama dole ya yi taka tsan-tsan wurin samun bayanen da yake buƙata a wurinta. “Wani irin ciwo ne ke damunki?” Tambayar ta fito daga bakinsa, bayan ta ratsa ta tsakanin mayaƙan dake san hanata fita daga bakin nasa. A hankali Mishal ta juyo da dubanta gare shi, kafin ta juya ta ci gaba da kallon windown, sannan muryarta ta fito a hankali cikin shirun motar. “Hysteria!... na gamu da ita ne sakamako wani bad memory da na taɓa samu” Sai ya yi shiru ya na san ganr inda kalaman nata suka dosa, a hankali ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, yayin da yake juya kan motar zuwa wata kwana. “Wani bad memory kika samu haka?” A wannan karon shi kansa sai da ya jinjinawa kansa na iya jefo mata tambayar, don shi ba ya surutai barkatai irin haka, idan ka ga hirsara da mutum na tsayi to a kan aikinsa ne, bayan nan kuma ba ya wata doguwar hira da kowa sai da Anna, ita ma sai su shafe tsawon wattani ba'a samu hakan ba. “Wani cousin brotherna ne, ya... Yi attempting min... Fyaɗe!...” Duk da ita yarinya ce ta san cewa sam kalmar 'Fyaɗen' ba ta da daɗin saurare, musamman ma ace miji za'a faɗawa faruwarsa a kan matarsa, abun akwai ƙona rai. Kuma sai da ta lura kamar kan motar na shirin ƙwacewa daga haannunsa, kafin ya seta kan motar da ƙyar, ya juyo ya kalleta na wasu 'yan sakkani, amma kuma ya kasa cewa komai. “A lokacin mun je hutu Maiduguri hutun Sallah... Sai ɗaya daga cikin cousins ɗina ya aike ni ɗakinsa, kasancewar tare suke kwana da shi Yazid ɗin ya sa a sanda na shiga ɗakin na gashin kwance a kan gado... Ban masa magana ba, dan da ma can Allah bai haɗa jinina da nasa ba, na nufi lokar Mu'ammar, wato shi wanda ya aikeni ɗin... Ban za ta ba na ji ya tura ƙofar ɗakin... Na tsorata amma ban nuna masa tsoron ba, na dake har na ɗauki abun da na zo dominsa, a sanda na juya sai na iske shi tsaye a jikin ƙofar... Ban ƙara masa kalo na biyu ba na nufi ƙofar dan na fita, ina zuwa kusa da shi ya kamo tsintsiyar hannun, ya finciko ni da ƙarfi zuwa baya... Ba shiri na faɗa kan gadonsa, ni kuma sai na shiga ƙoƙarin tashi, a lokacin ne ya daka min wata tsawa da har na koma ga Ubangijina ba zan manta da ita ba. A kan idona ya shiga cire kayan jikinsa. Ba ni da tsoro amma na tsorata a lokacin, ban ankara ba har ya iyo kaina ya danne ni, kuma cikin ikon Allah sai aka bankaɗo ƙofar daga waje. Aki Abubakar da Aki Arman suka shigo ɗakin, ganin na jima ban dawo ba ya sa suka biyo baya na. Ko a sanda aka fita da ni daga ɗakin ba na hayyacina. Tun daga lokacin na gamu da Hysterianan!” A lokacin da ta kai ƙarshen maganar hawaye har ya wanke mata fuska,duk da ita ba ta gama mallakar hankalin ba, amma tasan ciwon kanta, mace ta zauna ta na baka labarin yanda aka haike mata ba ƙaramin abun baƙinciki ba ne. Kuma ita kanta ba ta ce ga dalilin da yasa take ba shi labarin ba, wata ƙila don zuciyarta na faɗa mata cewar a yanzu shi ne gatanta, ba ta da wani gata nan duniya bayan shi, tun da ba ta da uwa, ba uba, ba ɗan uwa. Tun da ta fara bawa Kuliya labarin wani abu me kama da mashin ɗin yankan katako yake dagargaza zuciyarsa, ji yake ina ma ya na da damar da zai iya ganin bayan wannan mutumin, ko a baki ya tsani kalmar, bare kuma a ce matarsa aka yi kokarin aikatawa hakan. “Wani hukunci aka ɗauka a kansa?” Ya zaɓi da ya tambayeta ko zai ji salama game da yanda zuciyarsa ke masa zugi, ji yake kamar ya kurma ihu, ko raɗaɗin tsagewar zuciyar tasa zai ragu. Mishal ta share hawayenta da gefen gyalenta. “Cewa suka yi ai abun na gida ne, dan haka sai dai ayi haƙuri. Wani abun takaicin ma shi ne; kakarmu Jadda ita ce tace babu wani wanda ya isa ya taɓa mata jika, kamar ni ɗin ba 'ya ba ce, ko wata ƙila dan ba ni da iyaye a raye ne, kullum ba ta da abun faɗi da ya wuce tana sanmu, amma ni sam ba na ganin son!...” Ta ƙarshe tana sakin kuka me sauti a hankali. Ashe kallon kitse Kuliya yakewa rogo, wasu abubuwan idan ta yi sai ka ce 'yar shekara 10 ce, amma idan ta yi wani abun kuma sai ka zaci ta kai 20, wani lokacin yarinta ce fal a zancenta, wani lokacin kuma sai ta yi maganar hankali, kamar ba daga bakinta take fita ba, hannunsa yasa a cikin aljihunsa, ya zaro mata hanki, sannan ya miƙa mata. Mishal ta karɓa tana share hawayenta. “Wannan na ɗaya daga cikin matsalolin societynmu. Sai ki ga mutum ya aikata laifi, amma a ƙi ɗaukar mataki a kai, saboda ana ganin me laifin na gida ne, idan aka ɗaga maganar zumunci zai iya rabuwa. Wannan zai bawa me laifin damar ci gaba da aikata laifukansa yana fakewa da kasancewarsa na gida. Haka abun zai ci gaba da ƙaruwa kamar wutar daji” Cewar Kuliya. Mishal ta juyo ta kalleshi, ita kam yau ya na bata mamaki, bata taɓa ɗaukar cewar yana magana cikin sanyi irin haka ba, kuma ta ɗauka cewar maganganunsa basu da tsayi kamar yanda ta saba jinsu daga bakinsa, amma yau da banbanci. * “Maraba Lale!” Cewar Anna a sanda suka iso gidanta, tsaye take daga cikin falonta tana ta zabga murmushi, ta kasa gaskata abun da idonta ke gane mata, wai yau ita ce take ganin matar Aliyunta?. Suna ƙarasa shigowa cikin falon ta kama haannun Mishal ta zaunar da ita a kam kujera, sannan suka gaisa, fara'ar matar ya sa Mishal sakewa da ita. “Ni ce surukar ki 'yata, fatan ba za ki riƙa min ɗanyen tuwo ba” Anna ta faɗi tana dariya, hakan ya sa Mishal ma yin dariya, banda Kuliya da ya haɗa girar sama da ta ƙasa, kamar baƙin hadarin dake shirin zubar da ruwa, don shi bai ga wani abun dariya a maganar ba. “Kenan ke ce mamarsa?” Ta tamabaya tana kallon Kuliya. Anna ta gyaɗa mata kai. “Ni ce nan mamarsa” Mishal na murmushi ta ci gaba da ƙarewa fuskar Anna kallo, wai ko za ta tsinto wani abu guda da ya haɗa kamarta da ta Kuliyan. amma har ta gama yawo da idonta a kan fuskar Annan ba ta gani ba. “Sunana Anna.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112