Chapter 18
Chapter 18
hankali. Amma sam hankalin nata bai kwanta ba. A duk sanda za ta ga yarinyar kusa da Raja wani irin baƙin ciki ne ke cika zuciyarta. Har addu'a take kan ubangijinta ya bata damar da za ta raba yarinyar nan da haukar dake kanta, don idan aka bata dama, tsaf za ta rabata da wannan rawar kan da take. “Babe Please ka rabu da waɗanan gajojin, kullum idan zan zo sai sun hana ni ganinka” Cewar Uchechin, yayin da suka shiga cikin gidan, har suka zauna a kan kujerar falo, sai wani mammane masa take. Shi kuma ya ci gaba da kallonta da waɗanan lumsassun idanuwansa nasa. Amma bai ce mata komai ba. “Babe magana fa nake” Ta faɗi tana ƙara maƙalƙale shi. Hannunsa na dama ya saka ya tallafo fuskarta. “Gobe zan wuce Abuja” Wannan innocent muryar tasa ta faɗi, yayin da yake kallon idanunta. Shi kansa ya sani abun da yake ba dai-dai ba ne, yasan cewa hatta da taɓa jikinta da yake haramun ne, tunda ba maharramarsa ba ce. Sai dai yana iyaka bakin ƙoƙarinsa ganin basu wuce hakan ba, bayan taɓe-taɓen juna basa ƙetare iyaka. Duk kuwa da yanda Uchechin ke nuna masa cewar hakanfa ba komai ba ne, sai dai shi yasan cewa hakan komai ne. Dan kuwa ba zai taɓa yafewa kansa ba idan har ya aikata abinda take so ɗin, sai dai kuma yana san Uchechi, shi yasa ya kasa rabuwa da ita. Duk da yanda take nuna masa zalamarta a fili. “Shi kenan, ni ma akwai abinda nake yanzu, idan na gama zan biyoka Abujan...” “Sure?” Ta gyaɗa masa kai. Kafin ta ci gaba da tattaɓa sassan jikinsa, ganin kamar suna shirin yin nisa ne yasa shi saurin raba jikinsa da nata. Ya miƙe tsaye yana riƙe kansa. Da sauri Uchechi ta miƙe tana rungumarsa ta baya. “Please Babe, yau kawai, just once....” “Uchechi, get out!” Ya faɗi a ruɗe. “Babe...” “I say get the hell out of here!.....” Ya maimaita mata wannan karon cikin ɗaga murya, kamar ba shi ba, don abu ne mayuwaci ransa ya ɓaci. Nan take Uchechi ta fara hawaye, ta rasa me za ta masa ya fara santa, a ganinta kamar santa ne ba ya yi, dole ne ta koma wurin yayarta Chisoma, dan su san ta yanda zasu ɓullowa lamarin. Jakarta kawai ta ɗauka sannan ta fita. Tana fita Raja ya koma da baya yana kwanciya a kan kujerar. “Astangafurullah, Astangafurullah...” Ya shiga faɗi a hankali. Ya rasa wannan wata iriyar masifa ce haka, daga can ƙasan ruhinsa ba ya san hakan, amma kuma wani abu a cikin kansa na faɗa masa cewar ya aikata. “Rho, ki share mana...” Cewar Zuzu, yana ci gaba da lallashin Rhoda da ta ƙuntume fuska. Ganin fitowar Uchechi da gudu daga cikin gidan yasa suka miƙe da sauri. Dan suna cikin wata rumfa ne dake harabar gidan. Har wata ajiyar zuciya ta yi, tana bawa zuciyarta da kanta haƙuri. “Geti losh!” Cewar Alandi, a ƙoƙarinsa na ganin ya kwaciɓa turanci. Dariya ta kama Rjida, ta juyo ta kalleshi. “Ba geti losh ba, get loss!” Ya sosa kai ya na ɗaga hannu kamar me kai wa duka. “Sai ni Wallahi!... Hhhhh hajiya Rhoda ai kece ba ki gaɗa dai-dai ba, ki bar gani na a hakan nan, masters gareni a fannin kai sara suka!” Rhoda ta kwashe da dariya, ranta fes. *No. 213, Naf Belly Estate, Asokoro, Abuja* KULIYA POV. Zaune yake a ɗakin Anna, tun bayan da aka sauƙo a idi ya yi wa gidan dirar mikiya, a ganinsa nan ne kawai zai iya zuwa ba tare da ya yi tunanin aiki ba. Sai dai a yau gidan nata cike yake da mutane, wanda suke zuwa mata barka da sallah, shi kuma na ɗaya da ga cikin ɗabi'arsa, ba ya san zama a cikin mutane. Shi yasa ya dawo ɗakin nata ya zauna, yana karatun wasiƙar jaki. Ƙofar ɗakin aka turo haɗi da sallama. Jin muryar da ba ta Annaa ba yasa bai ko kalli inda ƙofar take ba, ya ci gaba da kallon inda yake kalla wato jikin taga, har yarinyar da Annan ta aiko kawo masa abincin ta aje a kan side drawer. “Me ki ka kawo ?” Kamar daga sama yarinyar ta ji muryarsa ta furta, wannan masifaffiyar muryar tasa, me sa cikin mutum murɗawa lokaci guda. Kuma nan take ita ɗin ma jikinta ya shiga rawa, saboda tsabar abar tsoro. “A... Anna, ce... ta... tace na kawo... maka abinci...” “Fita da shi!” “Amma ta...” “Ki fita da shi na ce, bana buƙata!” Cike da bala'i ya katseta, kuma har zuwa lokacin bai kalleta ba. Sum-sum ta ɗauki kayan abincin ta fita da su. “Gaskiya Anti Karima ba zan iya ba, na gaji da masifar bawan Allahn nan, shi kullum kamar bai san mutane ba, shekara nawa na shafe a gidan nan?, amma ko sunana ma bana jin ya sani...” Yarinyar ta faɗi rai a ɓace, yayin da ta iske yayarta a kitchen. Wadda take kitsa mata yanda za ta shawo kan Kuliya da ya daɗe a cikin ranta, tun sanda ta zo gidan Annan ta shafe shekaru kusan shida ta faɗa sansa, amma shi ko kallonta ma ba ta jin ya taɓa yi. “Ke dai Wallahi an yi wawuya, yanzu kina ga na miji irin wannan, za ki na wani cewa kin gaji?... ta ya zabki gaji ?... Namiji irin Kuliya ko yankar naman jikinki yake haƙuri za ki yi ki ci gaba da binsa...” Yanrinyar mai suna Siyama ta juyar da kanta gefe, har ga Allah ita ta gaji, tun shekaru uku baya take ta fama, amma ya kasa ganewa. Abu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa, ya kukan uwa mara amfani. “Ke ba ki ga irin yanda yake hidima da Anna ba ?, to ita da take marainiyarsa kenan, ke kuma idan ki ka zama matarsa ai sai yanda ki ka yi da shi kansa ma ba dukiyarsa ba!” Antin ta kuma faɗi, murya ƙasa-ƙasa. “Ke dai kawai ki ci gaba da dagewa, na tabbatar da za ki same shi... Kuma batun rashin sabo za ku saba, ba ki ji sunan sa ba ne ?, Kuliya manta sabo, ko ya san sabon ma mantawa da shi yake. Bare kuma ke da kunnenki ki ka ji Anna ta ce bai taɓa yin budurwa ba!” Kuliya dake zaune a ɗakin Anna yana kallo da kuma sauraren abun da suke ta cikin wayarsa, wani abu ne me kama da murmushi ya yi playing a cikin ransa. Amma ba za ka gane hakan ba idan ka kalli fuskarsa. Don tana nan cikin yanayinsa na shanu, babu fara'a bare annuri, fuska kamar kunun da ya so gardama. Wato shi za'a yi wa haka ?, bari su saka ido su gani, ko ƙoƙarin Siyaman zai yi aiki. *Unguwar Shuwarin, Maiduguri...* “Wallahi Kalisa nake faɗa miki... Kwata-kwata ba na samun kansa, amma tun da na yi amfani da maganin da Fati ta bani, sai na ga ya yi aiki, amma kuma bai jima ba ya wargaje... Ni na rasa yanda zan yi” Muryar Hajjara ta faɗi cikin damuwa, yayin da take bayyanawa ƙawarta Kalisa sirrin cikinta. Zaune suke a ɗakin gidan Kalisan, don bayan an sauƙo daga idi ta silale ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112