Chapter 56
Chapter 56
sani ba, ko wani kallo za ta masa bayan wannan abun da ya faru?, Oho. Rhoda dake cikin farin ciki da ɓacin rai a lokaci guda ta dafa kafaɗarsa. Ta na cikin farin ciki jin yau Raja ya rabu da Uchechi, ya kuma bayyana sirrin zuciyarsa kan abun da yake ji game da Rabi'a, ranta kuma ya ɓaci ne saboda nasa ran ya ɓaci. A hankali ya sauƙe hannunsa daga kan fuskarsa, sannan ya juya bayansa da sauri, ya kalli Rabi dake a sanƙare a wurin, kamar wata mutum-mutumi, kamar wadda aka manne mata ƙafafunta da glue me ƙarfi, kuma kamar wadda ta cillar da hankalinta a hanya, haka take jin kanta, duniyar ta mata shiru, babu abun da take ji sai muryar Raja cikin faɗin “She is my wife to be!”, anya kuwa tana cikin hayyacinta?, kamar fa ta haukace ma, yau in ba wadda ta yi hauka ba, waye yake jin abunbda babu shi a zahiri, ko kuma dai iskokai ne suka shiga jikin Rajan?, Oho, a'a abun zai fi kyau ace jikinta suka shiga ba nasa ba. Kanta ta ɗaga ta kalli fuskarsa, jin yana kiran sunanta. Kallonta kawai yake, ya kasa cewa komai, don ya ma rasa abun da zai faɗa mata, sai kawai ya juya ya tsayar mata da mota, sannan ya kamo hannunta ya sakata a cikin motar, don ya ga kamar bata cikin hayyacinta. A kan idonsa motar da ya sakata ta bar wurin, sannan ya dafe kansa cikin neman sauƙi, a bisa tsautsayi idonsa ya sauƙa kan wata rumfar me ƙosai, wutar da ya yi arba da ita tana ci a cikin murhunta ta tuno masa ƙiyayyarsa da wuta. *2008.* *Gidan Maman Rhoda, Kano...* *08:30 PM.* “Zaid miƙo min kwanon can!” Cewar Maman Rhoda tana nunawa Zaid kwanon dake ɗauke da farfesun kifi, Zaid ya ɗauki kwanon sannan ya miƙa mata, zaune suke a kan carpet ɗin dake falo, Rhoda na daga gefen Zaid, yayin da Maman Rhodan ke facing ɗinsu, girkin ranar da suka yi ne zube a gabansu, yayin da suna shirin cin abincin dare. “Mom ni kifin nake so kawai” Cewar Rhoda tana shagwaɓe fuska, Maman Rhoda ta wurga mata harara. “An ƙi a baki kifin, da ci kike ?, Kifi na Zaid ne kawai” Zaid ya kunshe dauriyarsa ya na shafa kanta, kasancewar ta jingina da shi, Maman Rhoda ta zubewa Zaid gaba ɗaya kifin, sannan ta bawa Rhoda tata shinkafar babu kifi sai miyar kawai. Rhoda ta turo baki tana ture abincin, sannan ta miƙe ta bar falon da hawaye. Nan da nan Zaid ya shiga damuwa, don Allah ya sani ba ya son ɓacin ran 'yar ƙanwar tasa, don haka ya miƙe, hannunsa riƙe da kwanon abincin nasa. “Zaid ina za ka?” Ba tare da ya juyo ba ya ɗaga ƙafaɗarsa ta dama sannan yace. “Abincin zan je mu ci” “Da ka rabu da ita kawai” “Ba zan iya cin abincin ba tare da ita ba!” Ya amsa mata a lokacin da ya ke ƙarsa fita daga cikin falon, Maman Rhoda ta girgiza kanta tana murmushi, soyyayar Zaid da Rhoda sai kallo, ko ka shiga tsakaninsu kai ne za ka ji kunya. “I'm sorry Cuzie” Zaid ya faɗi a karo na biyu ya na kallon Rhoda, wadda ta cunkune tana wani kawar da kai, wai ita a dole an ɓata mata rai, tana zaune a bakin gadonta, yayin da Zaid ɗin ke zaune kusa da ita. Ya na murmushi ya aje kwanon abincin a kan cinyarsa yana buɗe kifin, ya guntsuro tsoka ya haɗa da lomar shinkafar, sannan ya kai mata saitin bakinta, kamar ba za ta karɓa ba, sai kuma ta buɗe bakin ya saka mata. “Story time!...” Sai ta juyo tana kallonsa da kyau, ta harɗe ƙafafunta a kan gadon, tana buɗe duka kunnuwanta dan ta ji labarin da zai bata. Ta san labaran Zaid, babu na yarwa. “Wani Gayene ya zo Wajen Budurwarsa. Saiya Kira Yaro Yace mai; Kai je Gidannan Kace Sani Striker Na Kiran Hassana. Yaro Ya Antaya,yace wai Ana kiran Hassana. Babanta Yace waye Ke Kiranta? Yaro Yace Sani Striker. Sai Babanta Yace; Je Kace Isah Defender Yace Bata Zuwa” (Labaran musha dariya). Yana ba ta labarin yana kai mata lomar abincin haɗi da kifin, yana kaiwa ƙarshen labarin Rhoda ta tintsire da dariya. Abincin ya ci gaba da bata ya na bata wasu labaran, sai da ta ga ta kusa cinyewa, sannan ta karbi kwanon, ita ma ta shiga ba shi a baki. Kamar daga sama suka ji an banko ƙofar falonsu, hakan yasa ba shiri suka miƙe suka bazama zuwa cikin falon. Abun da suka gani ya bala'in gigita duniyar ko wannensu. Maman Rhoda ce yashe a ƙasa, Bala ya danne mata kai, ga sauran yaransa su Garuje tsaye a bayansa. Bala wani me kuɗi ne a unguwar kusa da ta su Maman Rhoda, ya na bawa mutane bashin kuɗi, musamman ma mata, sannan ya kan ƙawarawa mutane da kuɗin ruwa me yawa, idan kika ka sa biyan bashin kuma sai ya nemi ya fanshe a kanki, ga shi da tara yara 'yan daba, kasancewarsa ɗan uwan sanata ya sa ake ɗaga masa ƙafa ya na cin karansa babu babbaka. Lokacin da Maman Rhoda za ta biyawa Zaid kuɗin makaranta gaba ɗaya har zuwa lokacin da zai gama, kuɗaɗen hannunta ba su da yawa, hakan ya sa ta karɓi bashi a hannun Bala, suka yi da shi kan za ta riƙa biyansa da kaɗan-kaɗan. Kwana nan kuma sai ya bijiro mata da maganar ta ba shi kanta kawai, ita kuma sai ta nuna ƙin amincewarta, harda marinsa a yammacin jiya. Shi ne kuma yau ya iyo musu dirar mikiya a wannan daren. A cikin wannan daren Bala ya yiwa Maman Rhoda fyaɗe a kan idon Zaid da Rhoda, waɗanda ke riƙe a hannun yaransa su Garuje, sai da Zaid ɗin ma ya yi ƙoƙarin kaiwa Balan farmaki amma Garuje ya riƙe shi tare da buga kansa a jikin bango, hakan ya haddasa masa jiri da fashewar goshi. * Sosai Maman Rhoda take kuka, Zaid da Rhoda rungume a jikinta, yayin da suke tsaye a harabar police station, bayan da ta kawo ƙara kan zalincin da aka mata, faɗar sunan wanda take ƙara ya sa 'yan sandan korarta har da haɗa mata da duka. Babban tashin ha kalinta shi ne yanda Rhoda da Zaid ke cikin damuwa, ba za ta iya ɗaukan baƙin ciki irin wannan ba, hakan yasa ta fita wajen police station ɗin, ta siyo fetir da ashana, ta ture Zaid da Rhoda gefe, sannan a kan idon Zaid da Rhoda da kuma sauran jama'ar station ɗin. Maman Rhoda ta ɗaga jarkar fetir ɗin nan ta tittila a jikinta, sannan ta kunnawa kanta wuta, Rhoda na kuka tana fisge hannunta daga ruƙon da Zaid ya mata, yayin da wannan wutar ke ci a kan idon Zaid, komai na cikin kansa ya taɓu, tsoron wuta ya kama shi, ya zamana ba shi da wata abokiyar gaba kamar wuta. Don a lokacin suma ya yi, 'yan san dake da imani a wurin ne suka temaka musu, ita kam Maman Rhoda babu abun da ya yi saura a gawarta, ta ƙone ƙurmus, Zaid kuma ya suma, Rhoda kuma sai kuka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112