Chapter 108
Chapter 108
kiran nurses. Tare da nurses guda uku suka dawo, su suka dakatar da shi a waje, su kuma suka shiga ɗakin. Jim kaɗan ɗaya daga cikinsu ta fito, bayan ɗan wani lokaci kuma sai gata ta dawo ita da likitan da ya duba Aliyun. Sun jima sosai a ɗakin, dan har sai da ya ƙagu. Sai ga su sun fito, da sauri ya shiga tambayar likitan jikin Aliyun. Likitan ya sanar masa da komai lafiya, dan har sun saka masa arm sling, gudun kada ya cika yawan motsa hannun. Amma kuma sun masa wata allura, wadda ta sa ya koma bacci, amma daga lokacin zuwa ƙarfe bakwai na safe zai iya farkawa. Da haka hankalinsa ya kwanta, har ya dawo ɗakin ya zauna ya ci gaba da gadinsa, har zuwa lokacin da ya farka. “Ya... Ya kake?” Cewar Kuliya, dan be ma san me ya kamata ya tambayi ɗan uwansa ba, wanda Allah ya haɗasu bayan shuɗewar shekaru masu yawa da rabuwarsu. A ɗazun da ya farka cewa ya yi Zaid ɗin ya ara masa wayarsa, akwai wanda zai kira. Bayan da Zaid din ya ba shi wayar, sai ya kira Anna ya sanar mata halin da yake ciki. Kuma tun bayan wannan maganar, wata magana bata ƙara shiga tsakaninsu ba. Zaid ya juyo ya kalleshi, me makon ya amsa tambayar da ya masa, sai ya ja ɗan uwan nasa ya rungumeshi. Duk cikinsu babu wanda be zubar da ƙwalla ba, dan faɗar kalar kewar juna da suka yi ma ɓata baki ne. “Wannan ne abun da ya kamata ace ka tambayi yayanka bayan kun haɗu?!” Cewar Zaid yana shafa kansa bayan da suka saki juna. Kuliya ya share hawaye. “Ban... Ban san me ya kamata na ce ba ne?” “Dama kai kana rasa abun faɗe ne?” Sai suka yi dariya. “Ina Mishal?” “Wa? Ko matarka ?” Sai Aliyu ya sunkuyar da kansa yana faɗin. “Eh ita” “Suna gidana, ɗazu na ga kiran matata, na san nan da anjima za ka sun iso...” Daga nan kuma sai aka buɗe babin hira, suka shiga bawa juna labaran abubuwan da suka faru a rayuwarsu bayan rabuwarsu, daga Zaid har Aliyun, Allah ne kaɗai ya san kalar farin cikin da suke ciki, bayan shuɗewar tarin shekaru, yau sai ga su a tare da juna,me ya fi wannan daɗi?. Ba su ɓoye juna komai ba, wani zancen su yi dariya, wani kuma su matse ƙwalla. Kuma cikin hirar tasu ne, Zaid yake sanarwa da Aliyu cewar ya haɗu da dangin Momma, kuma su ne ma suka aura masa matarsa, dan ita ce 'yar anti Maryam da Momma ke basu labarinta. Sosai suka tattauna kan matsalolin da suka faru da su, da kuma nasarorin da ko wannensu ya yi a rayuwa. “Ni da ma na san baka mutu ba, dan ce mana aka yi ka gudu, ba cewa aka yi ka mutu ba... Kawai de na haƙura na fawallawa Allah ne, fon na san ko ba daɗe, ko ba jima idan har Allah ya hukunta haɗuwar mu da juna za mu haɗu...” Zaid ya ci gaba da kallon ƙanin nasa cike da alfahari. Ji yake kamar ya buɗe cikinsa ya saka shi ya kulle, gudun kada wani abu ya ƙara zuwa ya shiga tsakaninsu. Ƙofar ɗakin aka turo, Mishal da Rabi suka bayyana a bayan ƙofar. Daga Zaid ɗin har Aliyu suka juyo suna kallon bakin ƙofar. Mishal na arba da Kuliya, zaune da rai, wata ƙwalla ta silalo daga idonta. Ba ta san ya ka yi ba, amma ita de ta san kowa dake ɗakin ya ɓace a idonta, ba ta ganin kowa sai Aliyuj da ke zaune a bakin gado, sanye cikin wasu bluen riga da wando, hannunsa na dama saƙale cikin arm sling, ya kafeta da idamuwansa ya na kallo. Dan haka ta taka da gudu ta yi kansa, kuma tana zuwa kusa da shi ta faɗa jikinsa ta rungume mijinta. Kuliya ya ɗan cije lips ɗinsa na ƙasa, saboda zafin famun da Mishal ta masa, amma haka ya ɗago da hannunsa na hagu, ya ɗora avkan gashinta dake cikin hijabi. “Abu Aswad... Abu Aswad ɗina... Abu Aswad... Da ma na san ba za ka mutu ka barni ba...” Faɗi take tana ƙara ƙanƙameshi. Hakan ya sa Zaid miƙewa daga bakin gadon ya ja hannun Rabi zuwa waje, tare da rufo musu ƙofar. Mishal ta ɗago da kanta daga ƙirjin Kuliya, ta shiga dudduba jikinsa, hawaye ya jiƙa mata fuska. Hannunsa ya ɗago ya kama fuskarta. “Abu Aswad ɗina!” “My Teddy Bear” Kuliya ya furta a hankali yana share mata hawayen. “Da ma ai na faɗa maka cewar ba za ka mutu ka barni ba...” Fuskarsa ya kara da tata ya na faɗin. “I love you Mishallyn Aliyu, i love you to the moon and back... I love you my Boo, my last love, my babe, my other half, my treasure, my honey bun...” Kafin a hankali, ya haɗe bakinsa da nata, suka shiga musayar yawu. Sakinta ya yi yana zaunar da ita a gefensa. Sai kuma ya kalleta sosai. Idonta har wani ƙyallin murna yake na ganin ya samu sauƙi. ”Kin yi kyau, wa ya baki hijabi kika saka?” Sai ta kalli hijabin jikin nata tana faɗin. “Anti Adawiyya ce ta bani” “Ya miki kyau sosai” Matsawa ta yi kusa da shi, kamar me shirin komawa cikinsa, ta maƙalƙale hannunsa na hagu. “Abu Aswad! Jiya fa na ɗauka cewar ka mutu. Na yi tunanin ka mutu ka barni.Na ɗauka cewar wani maraicin zan sake shiga” Kuliya ya yi murmushi ya na sumbatar kanta. “Insha-Allah zan ci gaba da zama da ke, har zuwa lokacin da zaki kawo mana babynmu!” Sai ta ɗago da kanta ta kalli fuskarsa. “Kenan zan samu baby?” Sai ya yi dariya. “Haka nake zato, ina da yaƙinin cewa mun kusa samun baby soon” Sai ita ma ta yi dariya tana kwantar da kanta a kafaɗarsa. “Ka san suna wa za'a sa masa?” Dariya shi ma ya yi, har jikinsu na jinjiga a tare. “Wai an tabbatar ne?” Ta ɗago tana fadin. “Me ɗin?” “Babyn mana. An tabbatar kina ɗauke da shi?” Nan take ta haɗe rai tana kai masa duka a damtsen hannunsa. “Auuchhh! Teddy Bear irin wannan duka haka?” Ta turo baki gaba tana faɗin. “To ba kai ka ce min na samu baby ba, kuma sai ka dawo kana min wani ƙauli da ba'adi” Ta faɗi idonta na ciccikowa da ƙwalla, dan ita har ga Allah ta riga da ta yadda da cewar ta kusa samun babyn, ya riga da ya sa mata rai, kuma sai ya zo yace ba haka ba?. “Wasa fa nake miki, amma idan kina so sai an ƙara!...” Ta san me yake nufi da sai an ƙara ɗin, dan haka ta ƙara ɗaka masa wani dukan, wannan karon a cinyarsa, ya dafe wurin yana dariya. “Ki yi haƙuri, kin ga fa ba ni da lafiya, ya kamata ace an raga min ai” Mishal ta share ƙwallar da ta silalo mata, dan ita ta mamanta da ba shi da lafiyar. “To ka yi haƙuri” “Ke!” Ta kalleshi. “Me ya sa kika yi laushi ne?. Abu kaɗan sai ki masa kuka, bayan na san da ba haka kike ba” Ya tambaya jin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112