Chapter 72
Chapter 72
motar kai kace ce masa aka yi idan ya tafi a hankali duniyar ce za ta tashi ba tare da ya je ya cimmawa abun da yake san gani ba. Cikin wasu 'yan muntuna sai ga su sun iso 'Vinca Hospital'. “Sunanta Rabi'a!” Raja ya faɗi cike da ƙaguwa, yayin da suke tsaye a reception, sai kai kawo yake, Rhoda ta dafa kafaɗarsa cikin san kwantar masa da hankali ya fi a ƙirga, amma sam ba ya fahimtar me take shirin faɗi. “Zaid Aliyu!” Da sauri suka juya daga shi har Rhoda, don ganin mahaluƙin da ya kira shi da wannan sunan, bisa ga mamakinsu, sai ya ga wani abokinsa ne da su ka yi jami'a tare, ba course ɗaya suke offering ba, amma sukan haɗu a cikin makaranta. Duk da ya na cikin wani hali sai da ya yi wa abokin nasa murmushi, haɗi da miƙa masa hanu su gaisa. “Me ya kawoka asibitinmu?” Abokin me suna Huzaifa ya faɗa, Raja ya ɗan sosa kansa. “Wata mara lafiya muke nema...” Bai ko rufe bakinsa ba, receptionist ɗin tace. “Ku yi haƙuri ranka ya daɗe, amma babu mu da mara lafiya me wannan sunan...” Raja ya girgiza kansa. “Kuma an tabbatar muku da ta na nan?” Huzaifa ya tambayi Raja, Raja ya gyaɗa kansa a sanyaye. “Da ga masaniya me ƙarfi muka samu labarin, kuma an tabbatar mana da tana cikin asibitin nan” “Muje office ɗina, wata ƙila akwai wani temako da zan iya maka” Daga haka kuma suka ɗunguma zuwa office ɗin Dr. Huzaifa. Wuri ya nuna musu suka zauna, sannan shi ma ya zauna ya na tambayarsu. “Kamar yaushe kuke ganin an kawota nan?” “Sati uku baya haka...” Rhoda ta bashi amsa,sai ya gyaɗa kansa ya na ɗaukan wayarsa, kira ya yi, kuma bayan wani lokaci sai ga wata nurse ta shigo hannunta riƙe da files. Dr. Huzaifa ya karɓi fle ɗin ya na kallon fuskarta. “Ɗakin nan kika shiga ba?” Ya tambayeta saboda ganin yanda idonta ya yi jajir, alamun dai ta yi kuka, sai nurse ɗin ta sinkuyar da kanta ƙasa tana wasa da yatsunta. “Sakina!” Ya kira sunanta, hakan ya sa ta ɗago da kanta ta kalleshi. “Sau nawa zan faɗa miki ki dena shiga ɗakin nan, in har za ki riƙa shiga damuwa irin wannan, me nene amfani zuwa ganinta?” “Na kasa iya hana kai na Dr., a duk sanda zan shiga na dubata sai na zubar da ƙwalla...” Huzaifa ya miƙawa Raja file ɗin, wanda ya kafesu da kallo. “Ki je kawai za mu yi magana daga baya” Kanta ta gyaɗa sannan ta fita daga office ɗin. “Akan wa kuke magana?” Raja ya tambaya hannunsa riƙe da file ɗin da Huzaifan ya miƙa masa. “Wata mara lafiya ce aka kawota asibitin nan, sati uku baya, Wallahi abun tausayi, wasu ne suka mata fyaɗe sannan suka cillar da ita a hanya, mutanen kusa da mu ne suka kawota nan, sati uku kenan amma babu wani nata da ya bayyana... Wannan file ɗin ya na ƙunshe da bayanan kaf marasa lafiyar da aka karɓesu a asibitin nan, a tsakankanin sati uku da suka wuce, ku duba, wata ƙila za ku iya samun wadda kuke nema” Ya ƙarashe ya na musu bayani kan abinda ya sa suka biyoshi, amma sam Raja bai fahimci zancen nasa na biyu ba, wannan maganartasa ta farko ita ce ta sa hankalinsa a kwalba ta kulle, don zuciyarsa ce ta hango masa dacewar bayanen da aka basu, da kuma wanda shi Huzaifan yake faɗa, to ko de ita ce?, amma ta ya za ayi ta kasance ita?. “Ina ne ɗakin mara lafiyar?” Rajan ya tambaya ya na kallonsa, har Huzaifa zai ce wani abu, sai kuma hoton fuskar yarinyar ya haska a cikin kansa, rannan da ya shiga ɗakin don dubata ya kalli fuskarta, a lokacin ya ga kamar ya san fuskar tata a wani wuri, duk da ɗinkin da aka mata a gefen fuskarta, amma ta masa kama da wani wanda ya sani, a yanzu da Raja yake zaune a gabansa, sai fuskarta ta haska a cikin kansa, haɗi da tasa fuskar. “Nan ne!” Huzaifa ya faɗi ya na nuna musu ƙofar ɗakin, Raja ya juyo ya kalli Rhoda, zuciyarsa na dokawa a kunnuwansa, ƙafafunsa suka masa nauyi, don ji yake kamar abun da yake zargi shi ne zai tabbata. Kamar mara lafiya haka ya kai hannunsa ya kama ƙofar ɗakin ya murɗa, tura ƙofar ciki ya yi, sannan ya shiga. Idonsa ƙyam a kan yarinyar dake kwance a kan gadon marasa lafiya, wasu na'urori ne ɗaure a jikinta, kuma babu sautin dake tashi a ɗakin sai na na'urorin. Duk da wani irin fari da ta yi, duk da wani ƙaton yanka da ya gani a gefen fuskarta, duk da gashin kanta da ya yi alamar kamar an yanke, duk da yanda fuskarta ta yi wani irin fayau kamar wadda ta mutu, duk da yanda idanuwanta ke a rufe kamar gawa, bai hana shi gane taba. Kuma ƙwaƙwalwarsa na ganeta, ta hankaɗo masa bayanan Huzaifa na ɗazu. _“Wata mara lafiya ce aka kawota asibitin nan, sati uku baya, Wallahi abun tausayi, wasu ne suka mata fyaɗe sannan suka cillar da ita a hanya, mutanen kusa da mu ne suka kawota nan, sati uku kenan amma babu wani nata da ya bayyana...”_ Nan take ya ji wata ƙara a ƙirjinsa kamar ta tashin bomb, a sanda kalaman suka tsaya, a lokacin ne ƙafafunsa suka ɗauki rawa, haka ma hannayensa, hatta da bakinsa rawa yake, duniyar ta masa. Wani irin shiru, sannan duhu ya mamaye injinan ganinsa. Fyaɗe!?, fyaɗe!?, fyaɗe!?, Ita ma?, kenan ita ma sai da aka samu wani ya aikata mata wannan zalincin?, me ya sa haka?, me ya sa ƙaddararsa take zuwa a haka?, me ya sa tarihi yake shirin maimaita kansa?, me ya sa?, me ya sa?, me ya sa?!... #Labarinsu #SalmaAhmadIsah #TaurariWriters ••••••••••• *LABARINSU* *©SALMA AHMAD ISAH* *TAURARI WRITERS* *19* ~~~ *Love is; when you hug someone and they feels like home...* *** *No.234, Efab Estate, Gwarinfa, Abuja.* A fusace Jadda ta shigo cikin gidan tana famar bambami, kamar wadda ta zauce. Hajjara na zaune a kan kujera tana taunar chewing gum, haɗi da latsa wayarta, wani ɗan iskan kallo ta bi Jaddan da shi, kafin ta ci gaba da kallon wayarta, daga gefen ta kuma Fahima ce zaune ta na wasa, yayin da Hammad ke zaune a kan dinning ya na cin abinci. “Wallahi wannan yaron da aka aurawa Hafsat ya ɓatata, yo in ba haka ba ta ya za ayi na je na ce ta taho mu tafi, amma ta ce ba za ta zo ba?, wata ƙila ma shanyeta ya yi!...” Haka ta dinga sambatu, har ta kai ɗakin da ke a mazaunin nata, ta riga ta yanke shawarar barin garin a yau, don babu abun da za ta zauna ta yi a Abuja, tun da wadda take zaune don itan ta ƙi yarda ta biyota, duk da wahalar da ta sha kafin ta samu adireshin gidan nata. Kuma ta riga da ta yamie shawarar datse ko wace alaƙa dake tsakaninta da Mishal ɗin, tun da ita ba ta da mutunci, wai ita 'yar daɗi miji, tun da ta zaɓi zama da shi ga
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112