Chapter 33
Chapter 33
suka saba kwana, ya zaunar da shi a bakin katifarsu, sannan ya koma bayan gidan ya ɗauko ledar ƙosan da Allah ya temakesu bai zube ba, ya haɗo da wani plate da suka saba cin abinci a ciki, sannan ya ɗebo masa ruwa. Ya dawo ya zauna kusa da shi, ya juye masa ƙosan a plate, tare da tura masa shi gabansa. “Ka ci Aliyu” Aliyu ya kalli ƙosan, sannan ya kalli yayansa, ƙwarin gwiwarsa, farin cikinsa, uwa, ubansa duka a halin yanzu Zaid ne. Sai ya kai hannu ya ɗauko ƙosan guda ɗaya, me makon ya kai bakinsa, sai ya kai setin bakin Zaid. Zaid ya kalli ƙosan, sannan ya kalli Aliyu, wata ƙwalla me ɗumi ta sauƙo masa, a hankali ya buɗe bakinsa, Aliyun ya ƙarasa saka masa ƙosan, yana taunawa hawayen na ƙara kwaranyo masa. Ya kai hannunsa ya ɗauko ƙosan shi ma, sannan ya kaiwa Aliyun baki, Aliyu ya karɓa ya na murmushi, da haka suka cinye sannan suka sha ruwa. Sai kuma suka zauna suna biya tilawar islamiyyarsu, dan bayan faruwar iftila'in nan sun ɗan je. A lokacin biyan kuɗin wata ne malaman suka korosu, makaranatar safe kuwa l ba su kusanceta ba, dan sunsan babu me barinsu su shiga basu da uniform, kuma ga shi term ya kawo ƙarashe. Karatun ƙur'anin dai shi suke ɗan taɓawa da ka. Bayan sun yi sallahr azahar, Zaid yace zai fita ya nemo musu abin da za su ci na rana. “Zaid ka tafi da ni... Ba na san zama ni ɗaya” Cewar Aliyu ya na miƙewa, Zaid ya ɗaga ƙafaɗarsa ɗaya, sannan yace. “To muje” Aliyu ya ɗaga ƙafaɗarsa ɗaya yana kama hannun Zaid. Har suka fito daga cikin gidan, Zaid ya ɗauki wani ƙyallen tsumma ya ɗaure ƙofar gidan, kana suka kama hanyar bakin titi. Idan daga nesa ka gansu za ka ce mutum ɗaya ne, kasancewar komai nasu kala ɗaya ne, farin fatar, kyan fuskar, hatta da takunsu iri ɗaya suke, na Zaid ne kawai yafi nutsuwa. Idan wannan ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, sai ka ga wannan ma ya ɗaga, abun nasu gwanin ban sha'awa. A sanda suka fita titin, Zaid ya nunawa Aliyu wuri yace masa ya zauna, shi kuma zai je ya na barar. Aliyu ya zauna yana kallon yayansa, yanda yake miƙa hannu yabna barar sai da ya sa shi kuka. Wai yanzu su ne rayuwarsu ta koma haka, su ɗin da suke da gata, suke da uwa, wadda ta ɗauke musu kewar uba, su ɗin da ba su nemi komai sun rasa ba, amma cikin ƙiftawar ido, komai ya sauya, LABARINSU ya sauya, rayuwar ma baki ɗayanta ta sauya. “A taimaka mana sadaka fi sabillilahi...” Cewar Zaid yana miƙawa wani me shago hannu, mutumin ya miƙe a fusace. “Kai! Ba ɗazu ma ka zo ba?!...” Kafin ya ƙarasa yaron shagonsa yace. “Jiya ma sai da ya zo” “Sh*ge, da ma da irinku ake haɗa baki ana mana sata, bar nan wurin!” Ya ƙarashe yana hankaɗashi, har sai da Zaid ɗin ya faɗi ƙasa, da yake hakan ba komai ba ne a wurinsa, sai ya miƙe yana bawa mutumin haƙuri, don ba yau aka fara masa irin hakan ba. Kamar wucewar walƙiya haka ya ga tahowar Aliyu da gudu, kuma kafin ya fahimci abun da Aliyun ke ƙoƙarin yi, har Aliyun ya yi tsallen albarka, ya kifawa me shagon nan mari. “Kut!, Babbar buhun ub*ncan!, kayyasa! Ni ka mara yaro ?!” Cewar me shagon yana kama baki. Aliyu da ya gama fusata a sanda ya ga an hankaɗa masa ɗan uwa yace. “Eh ɗin, na mareka, ko akwai abun da za ka iya?” Ya faɗi idonsa ƙyam a kan mutumin, babu wani alamun tsoro tare da shi, ji yake ma kamar zai iya kikkifa masa marin da ya fi haka, ga shi dai ba shekaru gareshi masu yawa ba, amma zafin zuciyarsa ya fi na ɗan shekara ashirin, ji yake a kan yayansa babu abun da ba zai iya ba. Ko dan sunansa Aliyu ne ?, Oho. Zaid ya kamo hannunsa ya na jansa baya. “Zo mu tafi Aliyu...” “Rabu da ni Zaid, sai na nuna masa martaba da kimarka a wajena” Nan fa me shagon nan ya shiga zage-zage yana masifa, har maƙotan shagunansa suka fito. Ɗaya daga cikin masu shagunan ne ya kamo hannunsu Zaid, ya ja su zuwa gefe. “Ni kuwa yara ku ba 'ya'yan wannan likitar ba ne ta bayan layi ?” Mutumin ya tambaya, yana ganin kammanin customern tasa a fuskar kowannensu. Aliyu bai iya bashi amsa ba, kasancewar zuciyarsa na tafarfasa, har yanzu ji yake marin da ya yi wa me shagon nan bai wadatar ba, kamar ya na buƙatar a ƙara masa, soboda abinda ya yiwa Zaid ɗinsa. Zaid ne ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, sannan yace. “Eh, mu yaranta ne” “Kwana biyu ba na ganinta, fatan dai lafiya ?” Zaid ya sunkuyar da kansa ƙasa. “Yau wata biyar kenan da rasuwarta, gobara ce ta kama a gidanmu, kuma a lokacin da gobarar ta kama tana cikin gidan...” “Innallillahi wa inna ilaihi raji'un... Wallahi yara ban sani ba.... To yanzu ku da wa kuke zaune?” “Ba mu da kowa, mu kaɗai ne” “Subhannallahi, shi yasa kuke bara ?” Zaid ya gyaɗa masa kai, don da ma shi ne yake bashi amsar. “To kunga, ku zo ku zauna a shagona, na sai muku abinci ku ci, da yamma idan Allah ya kaimu, zan kaiku gidan marayu, ai za ku iya zama a can ko ?” Da sauri suka kalleshi, sannan kuma suka kalli juna, ba musu suka gyaɗa masa kai. Mutumin me suna Ila ya yi murmushi, har wa yau ya na tuna irin alkairin mahaifiyarsu gareshi. Domin akwai wata rana da ta taɓa zuwa shagonsa ta iskeshi ya yi tagumi, ta tambayarsa; lafiya? shi ne ya shaida mata da matarsa ce ta shaihu, ga shi ko na yanka ba shi da shi. Har wa yau ya na iya hango murmushin da ta yi a lokacin, sannan ta lale maƙudan kuɗaɗe ta damƙa masa, tare da faɗin a sha hidumar bikin suna lafiya. Har da kukansa a lokacin, don Allah ya sani yanda yake a cikin buƙatar kuɗi. Da ma jarin nasa ma bai taka kara ya karya ba. * “Na ji buƙatarka Malam Ila, sai dai a gaskiyar batu, ba mu da gurin zaman mutum biyu, yaro ɗaya kawai za mu iya karɓa, saboda yanzu haka ma gidan nan a cike yake da yara, yaro ɗayan ma za mu karɓeshi ne kawai dan ka dage” Cewar shugar gidan marayun da Malam Ila ya kai su Zaid, zaune take a kan kujera, yayin da take kallon Malam Ila dake tsallaken kujerarta, Zaid da Aliyu kuma na tsaye daga bayansa. A yau sun ci abincin da rabonsu da cin irinsa tun watanni biyar da suka wuce, wato ranar da Mommansu ta rasu, Malam Ila sai da ya tabbatar da sun ci sun ƙoshi, sannan ya kawo su nan wurin. Cike da fatan zuwansu wurin zai sauya rayuwarsu, amma maganar da matar ta yi ita ta murmushe wannan fatan nasu har garinsa. “To yara kun dai ji... Yanzu mecece mafita ?” Cewar Malam Ila yana juyowa ya kallesu. “Malam Ila mun gode da temakonka.... A gaskiya ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112