Chapter 24
Chapter 24
ba a tawagarsa kake ba, to fa shi babu ruwansa da kai. Elevator ya shiga, wadda ta kai shi zuwa floor ɗin office ɗinsa. Ya fita daga ciki, kafin ya shiga office ɗinsa, kujerarsa ya ja ya zauna, sannan ya kunna desktop, ya shiga danne-danne. Kafin bayan shuɗewar wasu lokuta, ya ɗauki wayar land line ɗin dake kan table ɗinsa ya aika kira, kuma kalamai biyu kawai ya faɗi sannan ya katse kiran. Bayan ɗan wani lokaci, aka ƙwanƙwasa ƙofar office ɗin, gyaran murya ya musu kamar kullum, kafin ƙofar ta buɗe. Sharon, Abubakar da Symon suka shigo, nuni ya musu da kan set ɗin wasu sofa da ke tsakiyar office ɗin, alamin su zauna a can. Zama suka yi, a sanda shi ma ya taso daga kan tasa kujerar, hannunsa riƙe da wasu takardu ya zauna a kusa da su. ya shi ga musu bayani akan abun da ya sa ya kirasu. “Kamar yanda muka riga muka fara wannan binciken, tun farko na sanar muku da rukuni garesu... Sunan ogansu Tomes, yana da yara shida, sannan akwai mace ɗaya a cikinsu... Kuma ana zarginsu da fasaƙwaurin miyagun ƙwayoyi, kisa...” Sai kuma ya yi shiru, yana tauna maganar da zai faɗa ta gaba, dan har wa yau kalmar na masa nauyi a bakinsa, musamman ma idan ya tuna cewa wannan hanyar ita ce silar samuwarsa, ita ce silar zuwansa duniya, ita ce silar raba mahaifiyarsu da farin cikinta. Wannan hanyar ita ce ta sa bayan rasuwar mahaifiyarsu aka rasa wanda zai bawa rayuwarsu agaji, har ta kai ga ya rasa yayansa, ɗan uwansa, mafi soyuwa a ransa. Kafaɗarsa ya ɗaga yana ci gaba. “...Fyaɗe, sai kuma saye da siyarwar miyagun ƙwayoyin... A halin yanzu na yi magana da Ram, ya na tricking location ɗinsu, kuma daga zarar ya gano inda suke, kai tsaye farmaki za mu kai... Ko a mutu ko a yi rai!” Abun da bai sani ba shi ne,wasu lokutan abubuwan da mukan furta su ne ke faruwa, wasu ƙaddarorin kan faru kamar yanda muka ayyana a zukatanmu. Wannan kalaman nasa na da alaƙa da wata ƙaddara da Allah ya hukunta faruwar ta 'yan lukuta ƙalilan da za su zo. Wata ƙaddara da za ta tarwatsa komai, sannan ta saita wasu lamura. A yammacin wannan ranar, bayan lokacin tashinsa a aiki ya yi, yana tuƙi cikin baƙar motarsa ƙirar honda elevate. Hannunsa na dama kan sitiyari, yayin da ɗayan kuma yake kan bakinsa. A hankali ya ɗaga kafaɗarasa ta dama, yana tsuga gudu a motar tasa, dan dama can shi haka tuƙinsa yake, ba ya tafiya a hankali, kuma hakan ne ke sawa suke raba gari idan za su yi tafiya shi da Anna, don haka take cewa; ita tabna san rayuwarta, ba ta shirya mutuwa ba. Tunanin hakan yasa shi yin murmushi a cikin ransa, a fili kuwa babu komai a kan fuskar tasa, ba fushi yake ba, ba fara'a yake ba, haka kuma ba ƙunci yake ba. Duk ƙwaƙwaffin mutum ba zai iya tsintar abun da ke kwance a kan fuskar tasa ba. Kamar daga sama wata motar ɗiban yashi, ta daki motar tasa daga gefe. Motar tasa ta yi ta dungurawa tana sakewa a kan titin, hakan ya sa ta yi kwatsa-kwatsa tun kafin ta tsaya da dunguwarawar da take. *No.234, Efab Estate, Gwarinfa, Abuja* MISHAL POV. Tsaye take a cikin kitchen, sanye cikin uniform, a hankali hannayenta ke jera kayan abincin da ta gama girkawa a cikin lunch box ɗinta. Ƙofar kitchen ɗin ta buɗe, Hajjara ta shigo tana mata murmushi kamar wancan karon, kuma a yanzun ma sai da ta tsorata, dan ba ta san da me ta zo ba wannan karon. Ƙarasowa ta yi gabanta ta tsaya tana mata wani irin kallo. “Ya akabyi Tsaka?!” Mishal ɗin ta tambaya, tana maida dubanta kan kayan da take jerawar. Sunan ya daki gangar zuciyar Hajjara, amma da ta tuna abin da ya kawota sai kawai ta basar. “Tsaka ba?, za kuwa ki ga ma'anar tsaka” “Ai babu kalar tsakar da ban ga ba... Me haɗa mutum da mutum ai tsaka ne Hajjara!... ko babu wanda ya taɓa baki labari cewar kaf tarihi babu wanda ya kai tsaka iya munafirci?” Ta kira sunanta kai tsaye, kuma tana kallon cikin idonta. Dan ba ta shakkarta ko tsoronta, tsoron sharrinta kawai take. “Yaro man kaza... Ke a tunanin ki za ki iya raba ni da mijina kuma na zauna ina kallonki ?” Mishal ta ɗan yi murmushi tana harɗe hannayenta a ƙirji. “Hajjara... Ke ce kika ɗauke ni a matsayin kishiya, ko da wasa ba na kishi da ke, saboda ban ga dalilin yin hakan ba, na ga kamar jahilcinki na san taɓa miki ƙwaƙwalwa, babu aure tsakanina da mijinki... Kuma kafin ya fara saninki ni ya fara sani... Amma ba zan yi mamaki ba dan kina kishi da ni, tun da 'yar da kika haifa ma kin ƙita saboda tana da nakasa... Me zai sa na ji haushi dan ni kin ƙini?” A wasu lokutan duk da ƙarancin shekarun Mishal da kuma yarintarta tana da hankali, dan wani zubin takan yi magana ta hankali. “Wata ƙila daga yau ba za ki ƙara ɗaga yatsarki a fuskata ba...” Hajjara ta faɗa tana kallonta. Mishal ba ta fahimci abin da take nufi ba, sai da ta ga ta shiga waige-waige a cikin kitchen ɗin, sannan ta gane me take nufi. Kuma ba ta ƙara tabbatar da abin da kanta ke gaya mata ba, sai da ta ga Hajjaran ta rarumo wuƙa. Abubakar na zaune a falo yanawa Daala wasa, sai ji ya yi an ƙwalla wata razannaniyar ƙara, wadda yake jin tana fitowa daga kitchen. Tsabar tsoratar da ya yi, ya kasa gane ƙarar waye. Ba shiri ya miƙe, ya nufi kitchen ɗin gadan-gadan. Ba ƙaramin tashi hankalinsa ya yi ba, a sanda ya yi arba da abinda ke aukuwa a kitchen ɗin. Mishal ce zaune a kan marbles, hannaunta na dama riƙe da na hagu. Yayin da tsintsiyar hannunta na hagun ke zubar da jini, sai kuka take tana hawaye. Dubansa ya kai kan Hajjara dake tsaye a kanta, hannunta riƙe da wuƙa. A tsorace Hajjara ta kalli Mishal sannan ta kalleshi, sai kuma ta cillar da wuƙar, idanta ya cika da ƙwalla, ta ci gaba da kallon Abubakar tana girgiza masa kai, alamun a'a. “Innallilahi wa inna ilaihi raji'un, Hajjara, kashemin ƙanwa kike san yi?” Abubakar ya tambaya a kiɗime, yayin da ya ƙarasa gaban Mishal yana duba hannun nata. Hajjara ta shiga girgiza masa kai, tana san ganar da shi gaskiyar abin da ya faru. Ita fa ba ta yi komai ba, ba ta san ya aka yi komai ya auku ba. Cikin muryar kuka ta shiga faɗin. “Abubakar Wallahi... Walahi ban mata kom...” “Ki min shiru!, Kada ki sake min magana. Na ɗauka tsanarta kawai kika yi, ahse har kasheta ma za ki iya yi!” Abubakar ya katseta a zafafe, bayan da ya ɗago daga duba Mushal ɗin da yake. Ya ƙara tsugannawa kan Mushal da ke ta kuka kamar zata fasa gidan. Yasan ƙanwarsa da dauriya, ba komai takewa kuka ba tun tana ƙarama, tana iya jure komai duk zafinsa, dan haka tun da take kuka, dole ciwon nata ba ƙarami ba ne.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112