Skip to content

Chapter 66

Chapter 66

Labarinsu Book 1 Complete Hausa Novel 1,216 words 0 views Progress saved
Download Book

nasu suka yi ɗaki. Kamar da Annan take jira, ta samu guri ta zauna tana musu kallon tuhuma, ganin yadda ko waccensu ta kafa inda-inda ne ya tabbatar mata da gaskiyar abun da suka aikata, duk kuwa da ta san Kuliya ba zai mata ƙarya ba. “Yanzu ke Karima a matsayinki na babba, ya kamata a ce kin aikata abun da kika aikata?, Ko za'a kira abun da Siyama ta yi a matsayin yarinta naki ba za a ce yarinta ba ce, saboda kin fita shekaru da sanin ya kamata. Amma saboda ke babbar kwabo ce, kika wanki ƙafa kuka je gidan matar mutane kuka rufa mata duka ko?!” Da sauri Siyama ta girgiza kanta, hawaye na ciko mata ido, musamman da ta tuna abun da ya faru a wacan ranar. “Anna Wallahi. Wallahi ba mu...” “Ƙarya kuke!, Idan ba ku ne kuka daketa ba za ta buga kanta da kanta a jikin bango ne, ta zo tace ku ne kuka mata dan kawai ta muku ƙazafi?” Da sauri Karima ta gyaɗa kai. “Wallahi Anna ba mu daketa ba, hasalima ita ce ta dake mu, duba ki gani...” Ta ƙarashe tana nunnuna mata tabon raunikan jikinta. Anna ta yi dariya, irin kun rena min hankalin nan. “Karima ko ƙur'ani za ki dafa kan wannan maganar taki ba zan yarda ba, jibe ki fa, yadda kike rusheshiyar nan da ke sai na yarda waccan 'yar fingilar yarinyar ita tai miki wannan raunin?, saboda ga Annan mahaukata ko?, to ni ba ma wannan ne ya kawo ni ba, zuwa na yi na ja muku kunne, babu ku babu gidan Aliyu, sannan babu ruwanku da sabgar matarsa, idan kuma ba ku ji ba ku je ku yi, Wallahi ni da kai na zan sa Aliyun ya hukunta ko waccenku, har ke Karima, tun da ba wani fikon arziƙi kika masa ba, in kun ce bakwa ji sai ku gwada mu gani!” Tana ƙarashewa ta miƙe ta fita, don da ma abin da ya kawota kenan, Siyama ta zube a kan kejera tana fashewa da kuka. “Kin ga inda kika kai mu ko Anti, yanzu ga shi bayan dukan da muka sha Anna ma ta ƙara mana da nata kashedin” Karima ta matse ƙwalla, tunawa da irin dukan da suka sha da ta yi. “Da ma ni sam soyyayar Kuliya ba ta karɓeni ba, ban da wahala babu abun da nake sha” Ta ƙarshe tana miƙewa, tare da nufar ɗakinta da gudu. Karima ta yi tagumi tana jinjina sharri da kissa irin na wannan 'yar mitsitsiyar yarinyar da suka rena, ko dan ai an ce ɗan hakin da ka rena. ____________________ _Gani nan na yi tagumi hannu bibbiyu_ _jama'a!, wai ina Rabi ta shige ne?, wani ya temaka ya nemo mana ita_ _Ku ni fa na kasa gano abun da ya faru tsakanin su Karima da kuma Mishal_ _Salmanians, shin kuna kusa?_ #Labarinsu #SalmaAhmadIsah #TaurariWriters ••••••••••••••••••••••••• *LABARINSU* *©SALMA AHMAD ISAH* *TAURARI WRITERS* *16* ~~~ *Don't be afraid of falling apart. Some of the must beautiful heart are built from tragedy.* *** Follow my Wattpad account 👇 https://www.wattpad.com/user/Salma_Ahmad_Isah?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends ~~~ *Bayan sati uku...* *No.181, Guzape, Abuja...* *09:30pm* MISHAL POV. Kwance take a falo, ta duƙunƙuna cikin blanket, idanuwanta sun yi ja saboda kukan da ta ci, ta kunna tv ta tsura mata ido amma ba kallon take ba. Damuwa da ruɗani ne suka saka rayuwarta a gaba, yau kusan sati uku kenan, amma Antinta Adawiyya ba ta zuwa makaranta, tun ta na ganin abun kamar fashi ne, har fashin nata ya zo ya soma bata tsoro, dan zuwa yanzu ma an kawo wata sabuwar me yim shara a makarantar, kullum sai ta yi kukan rashin sanin halin da Adawiyyan ke ciki, ga kuma kaɗaici da yake damunta a yanzu, ga shi dai ba wani jimawa suka yi da Adawiyyan ba, amma haka kawai take jinta cikin kaɗaici, yanzu haka ta hana idonta bacci ne dan jiran dawowar Kuliya, tun da shi ɗan sanda ne wata ƙila zai iya yin wani abu akan case ɗin yayar tata. Ta na kwance a wurin har goma ta wuce, kuma sai a lokacin Kuliya ya shigo gidan rai a ɓace, wanda ya samo asali daga wurin aikinsa, Mishal na jin shigowarsa ta miƙe da sauri ta sha gabansa, kallonta ya yi na 'yan wasu sakkani, sannan ya shiga ƙoƙarin raɓata ya wuce, amma sai ta ƙara tare masa hanya. “Abu Aswad.Yayata ce ba ta zuwa makaranta. Kuma ban san meke faruwa da ita ba, dan Allah ke nemo min ita” ta faɗi hawaye na mata zuba. “Ke me ya sa baki san abinda ya kamata ba?, Yanzu na dawo gida da ɓacin rai, me makon ki bari na huce shi ne za ki tarbeni da wannan maganar?!” Kamar de wancan karon haka ya mata magana cikin hargagi, Mishal ta fashe da kuka sannan ta naushi ƙirjinsa. “I hate you Abu Aswad!” Ta na kaiwa nan ta juya da gudu ta faɗa ɗakinta. “Zan iya shigowa?” Kuliya ya tamabaya ya na turo ƙofar ɗakin Mishal, wadda ke zaune a kan gado ta na kuka, sai bayan da ya je ya yi wanka sannan ya samu sauƙowa, shi ne ya taso ƙafa da ƙafa don ya nemi yafiya. Saboda ya san ba laifinta ba ne, shi kansa yabna bincike a kan yarinyar me suna Rabi'a, amma har yanzu babu abun da ya samu. Ya je makarantar Brickhall yafi sau biyar a cikin sati ukun, amma sam sun ƙi su ba shi adireshin Rabin, ga kuma wani renin hankali da suke masa na cewar ai jiya ma ya zo, bayan shi kuma ya san bai zo a ranar ba. Zama ya yi a bakin gadon ta setinta, ya na kallon gefen fuskarta da ta kawar, fuskarta ta yi jajir, alamun dai ba ƙaramin kuka ta sha ba, shi ya rasa wannan wata iriyar ƙauna ce tsakaninta da wannan yarinyar. “Hafsat” Ya kira sunata a tausashe, sai ta ƙara haɗe rai ta na kumbura baki. “Ki yi haƙuri ba zan sake ba!” Juyowa ta yi suka haɗa ido, ta wurgar masa harara, ta ƙara kawar da kan nata, sai ta bashi dariya, hakan ya sa ya murmusa a ransa. “Yanzu ba za ki yafemin ba?” Ta kuma juyowa ta kalleshi. Jin yanda ya yi maganar kamar maraya. “I hate you, ka fita min daga ɗaki” “In dai yayarki ce zan nemo miki ita, yanzu ma na zo dan ki bani wasu bayanai a kanta ne, ta yanda zan yi saurin samo miki ita!...” Kallonsa take tana son tabbatar da kalamansa, can kuma sai ta matso kusa da shi. “Ka yi alƙawarin za ka nemomin ita?” Sai ya gyaɗa mata kai ya na ɗaga ƙafaɗarsa ta dama, shi kansa bai san haka yake da laushi ba sai a kan Mishal, ita ce zai ɗagawa murya daga baya kuma ya zo ya na bata haƙuri. “Ni dai ki yafemin!” Ya faɗi murya ƙasa-ƙasa, kuma amon muryar tasa ya sa Mishal ɗin lumshe ido sannan ta buɗe. “To ba na ce maka ba na san tsawaba.Amma kullum idan ka fusata sai ka min...” “Daga yau ba zan sake ba, na miki alƙawari” Ya katseta tun kafin ta rufe bakinta, sai ta yi murmushi tana share hawayenta. “Ina

Table of Contents

Chapters

112 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112