Skip to content

Chapter 75

Chapter 75

Labarinsu Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

da ta yi kowanne a cikinsu ya na cire tufafin jikinsa, basu damu da ko kallonta ba, ballantana su saurari abun da take faɗi. kukanta ta ƙarawa ƙarfi ta na rintse idonta._ _“Wai me ya sa mutane ba su san Allah ba? An haɗasu da Allah amma sai ka ce da wani sheɗan aka haɗasu, me makon mutum ya bar abun da yake sai ma ya ƙarawa abun ƙaimi, dan Allah na roƙeku...”_ _Ta ci gaba da roƙonsu, a lokacin da Usee yace._ _“Kai duk ta bi ta cika mana kunne, dallah kusa ta yi shiru!”_ _Jaz ne ya ɗauko ƙarfen abun shisharsu me kauri, ba tare da Rabi ta ankara ba, saboda idanuwanta da suke a kulle, ta ji sauƙar yankan wani abu me kaifi a gefen fuskarta, hakan ya sa ta buɗe idonta da sauri, wani kalar raɗaɗin azaba ya ziyarci ƙwaƙwalwarta, nan take ta ƙwala wani uban salatin da sai da gidan ya amsa, gefen fuskar tata ya yanku ba kaɗan ba._ _“Kai dallah mahaukaci! Cewa na yi ka sata ta yi shiru ba wai ta ƙara volume ba!”_ Cewar Usee ya na rarumar wata vase, sannan ya ɗaga ta sama, ya bugawa Rabi a tsakiyar kanta. Nan take Rabi ta ji wani dimmm, kamar injinan da suke aiki a kanta sun dena, komai ya tsaya cak, babu wani abu dake aiki, kan kace me, jini ya wanke mata fuska. Babu shiri ta faɗi a ka gadon._ _Duk da idonta a lumshe yake, ta na jin sanda suke rabata da tufafin jikinta, hakan ya sa ta buɗe idonta a wahalce, sai dai hoton abun da take gani ya koma ja, saboda jinin da ya wanke mata fuska, ba sosai take cikin hayyacinta ba, amma ta na ji ta na gani haka suka shiga haike mata ɗaya bayan ɗaya._ _Duk da irin raɗaɗin azabar da take ji, ba ta da damar yin ihun neman agaji, ta na kwance ne a wurin kamar gawa, amma da ko wace azaba da suke mata jikinta ya na amsawa, ko wanne a cikinsu sai da ya haike mata sau biyu, tun tana buɗewa idonta fa lumshe har sai da komai na kanta ya ɗauke, ji da ganinta suka yi nisa, numfashinta ya yi sama._ _“Usee kamar yarinyar nan fa ta mutu”_ _Usman ya ɗan karkato da kansa kaɗan ya kalli kan gadon, inda Rabi ke kwance malale cikin jini, babu tufafi a jikinta. Sai ya zuƙi sigarinsa, ya furzar ya na faɗin._ _“Ku ɗauketa ku cillar da ita, idan abun sha ya ƙare, me za ayi da kwalba?”_ _Ba tare da ɓata lokaci ba suka cika umarninsa, a cikin blanket ɗin dake kan gadon suka nannaɗe, sannan suka ɗauketa suka saka a mota, suka fita daga gidan. Sun ɗan yi tafiya me tsayi daga gidan Usman ɗin, kafin suka samu gefen titi, suka faki ido, duk da dare ne ,babu kowa a layin, suka cillar da ita a wurin kafin suka ƙara mai._ (Ya Ilahi ya Allah!...). A hankali wata siririyar ƙwalla ta zubo daga idon Rabi wada ke kwance a kan gadon marasa lafiya, tana nan kwance kamar gawa, kuma idanuwanta a lumshe. Wata ƙwallar ce ta sake gangarowa daga idonta ta shiga kunnenta. Sannan a hankali bakinta ya buɗe, cikin wata dasasshiyar murya ta fara faɗin; “Da... Dan... Dan A... Allah, kad... Kada ku... Kada ku min... Ka... Kar ku... Cutar... Cutar da ni... Ni...” Haka bakinta ya ci gaba da faɗi, kafin kuma jikinta ya fara jijjiga, da alama duk abun da ya faru a waccan ranar take gani a cikin mafarkinta. Cikin abun da bai wuce daƙiƙa ɗaya ba, ta wangale idanuwanta tar, ta na maida numfashi kamar wadda ta yi wani aikin ƙarfi, idonta ta ƙara lumshewa, sannan ta buɗe su tar. Kafin ta miƙe zaune, ta na ta dube-dube, sai kallon ɗakin take, kafin dubanta ya dawo jikinta, tabbas ta na asibiti ne, to duk yanda aka yi ɓacin ran da Raja ya saka mata ne ya sa ta suma, shi ne aka samu wani bawan Allahn ya kawota asibiti, har ta yi mafarkin an mata fyaɗe. Wanna hasashen da zuciyarta ta yi ne ya sa ta sauƙe ajiyar zuciya, haka ne ma, haba!, da ma in ba haka ba ta ya za'a yi ace an mata fyaɗe?!. Hannunta ta kai ta ciccire na'urorin da aka saka mata a jikinta, sannan ta shiga ƙoƙarin sauƙo da ƙafacunta ƙasa, ta daddafa har ta samu ta iya sauƙa daga kan gadon. Sai de me?, miƙewar tata ke da wuya ta ji ƙasanta ya yi wata irin amsawa, ba wai amsawa ta zafi ba, a'a, ji ta yi kamar an saka wani abu an ɗaure wurin, duk da haka ba ta karaya ba, wannan hasashen da zuciyarta ta yi shi ne ya ba ta ƙwarin gwiwa da kuma na zuciya, haka ta tattaka cikin wani irin taku me kama da na 'yan koyon tafiya, ta nufi banɗaki. Daɗewar da ƙafafunta suka yi ba su yi tafiya ba ya sa suke amsawa idan ta na taku, ƙofar bayin ta tura, sannan ta shiga, kai tsaye jikin mirror ta isa, kuma abun da ta gani shi ne ya rikirkito da duniyarta ƙasa. Wata tsawa da walƙiya suka haska a cikin kanta, wani irin tashin hankali da ba ta san akwai irinsa a duniya ba ya ziyarceta. Wannan yankan da aka mata a gefen fuska, ya na nan, har da ɗinki an yi wa wurin, dan har ya warke an cire zaren. Sannan ga gashin kanta da aka yanke mata, gashinta da a da yake sauƙowa har gadon bayanta, shi ne yanzu yake iyaka kafaɗunta, ga kuma tabon dukan da aka mata a kanta. Sannan wannan raunin fuskar tata shi ne ya ɗan sauya kammanin fuskarta, duk da ba du ba, amma yanayin fuskar tata ya sauya. Waɗanan alamomin su ne suka ƙaryata hasahsen zuciyarta, waɗanan alamomin su ne suka murmushe fatanta har garinsa, wanan alamomi su ne suka tabbatar mata da duk abin da ya faru a waccan ranar ba mafarki ba ne, gaskiya ne, da gaske ne cewar waɗanan mugayen samarin guda biyar, sun haike mata, da gaske ne cewar yanzu ita ba ta da wata martaba kamar ta sauran mata, kuma da gaske ne cewar ita yanzu ba budurwa ba ce, yanzu ita ba ta da wata kima da daraja wadda jama'a za su kalleta da ita, ba ta da wani abu da za ta nunawa mijin da za ta aura. A lokacin da ƙwaƙwalwarta ta kai ƙarshe wurin zayyano mata waɗanan kalaman, a dai-dai lokacin ne ta ɗago da hannunta ta shafa fuskarta, ta taɓa kanta. Nan take ta ji wani kukan ɓacin rai da na tashin hankali sun haɗe wuri guda sun tsaga haƙwaranta, sun raba laɓanta, sun fito cikin 'yancinsu. Wani kalar kuka take me sauti, jikinta har rawa yake. “Me ya sa ni ba ni da ƙaddara me kyau?!, me ya sa komai nawa yake rugujewa?! Me ya sa ni ba zan yi farin ciki kamar kowa ba?!, Me ya sa za'a zaɓi da a lalata min rayuwa?!, Me na yi haka?! Wani kalar zunubi gareni?!, Allah na tuba ka yafemin, Allah na roƙeka da kada ka ƙara ɗoramin wata jarrabawa bayan wannan, ya Allah

Table of Contents

Chapters

112 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112