Chapter 101
Chapter 101
dariya a tare, ashe soyyayar da sukewa juna ba za ta faɗi ƙasa ba, ashe Allah ya hukunta zamowarsu facalolin juna. Dariyar da Mishal ta yi ce ta sa jikinta jijjiga, hakan ya sa ta yi famu, sai ta ɗan cije lips ɗinta cikin jin zafi. Sai a lokacin Rabi ta lura da abun da yake faruwa da ƙanwar tata. “Me yake damunki Ƙanwata?” Nan da nan ƙwalla ta cika idon Mishal, ta turo bakinta gaba tana shirin fashewa da kuka. “Wallahi Anti Adawiyya Abu Aswad mugu ne, kuma zuciyarsa ma baƙa ce kamar kayansa, da ma ai na faɗa masa cewar sai na faɗa miki idan muka haɗu...” Nan take Rabi ta gane inda zancen ya dosa, amma kuma sai sunan da ta kira mijin nata da shi ya bata dariya. “Abu Aswad kuma Mishal?” Mishal ta share ƙwallar da ta zubo mata. “Abu Aswad mana, ba shi ne ba kullum cikin saka baƙaƙen kaya, shi ya sa na saka masa sunan...” “Na ji kin ce kin gaya masa cewar za ki gayamin abun da ya miki, da ma ya sanni ne?” Mishal ta kuma goge ƙwalla. “Ya sanki mana. Sanda kika ɓata shi na sa ya yi ta nemanki, kuma na san cewa shi ma ya gano cewar an saceki , amma shi ne ya ƙi faɗa min” Haƙuri Rabi ta shiga bata, kafin ta ƙarashe da bata shawarwari kan yadda za ta kula da kanta, da kuma gyara jikinta. Basu rabu ba sai da suka yiwa juna alƙawarin sanin dalilin rabuwar waɗanan 'yan uwan biyu. *No.86, Garki 2, Abuja...* *07:30pm* ZAID POV. Gama wayarsa da shugabansu ke da wuya, ya ji wayar ta sa na ringing. Hakan ya sa ya duba screen ɗin wayar, don ganin me kiran. Ganin Kawu Abdullahi ne ya sa shi yin murmushi, ya na ɗaga kiran. Gaisawa suka yi cike da girmamawa, kafin dalilin kiran ya taso. “Ɗazu muke jin wani zance a gida. Wai ka kai Rabi'a makarantar ƙwallon ƙafa!” Zaid dake tsaye a ƙofar ɗakinsa ya sosa kansa cikin jin nauyi, kafin yace. “Eh haka ne” “To tun wuri, ka yi gaggawar janye wannan ƙudirin naka... Ka bar ganin ita matarka ce, mu iyayenku ne, tun farko ya kamata ace ka shawarce mu kafin ka yanke hukunci a kanta. Ko a sanda take yarinya da mahaifiyarta ta kaita makarantar ba so muke ba, dan de muna ga yarinya ce, shi ya sa muka yi shiru. Amma a yanzu ta girma, tun da har mun mata aure, dan haka ba zamu ɗauki wannan shashancin ba. Tana mace me ya haɗata da wata ƙwallo?, zaman gida da kula da tarbiyyar yara shi ne ya dace da ita, ba gudu da gajeren wando a kan idon tarin mutane ba!...” Haka Zaid ya ja bakinsa ya yi shiru, har Kawun ya kai ƙarshe a faɗan nasa bai ce masa ƙala ba, sai da ya tabbatar da Kawun ya kai ƙarshe a wajen amayar da abun da ke bakinsa kafin ya seta kamillalliyar muryarsa, ya shiga koro bayani a natse, kuma cikin da girmamawa. “Na fahimce ka Kawu, kuma duk abun da ka faɗi gaskiya ne. Amma kuma ita ma Adawiyya tana da gaskiya. Ka san a ina ta yi gaskiya?” Kawu Abdullahi dake zaune a kusa da su Baba ya juya ya kallesu, dan kuwa suma suna jin duk maganar da Zaid ɗin yake, sai kuma ya girgiza kansa cikin faɗin. “A'a, sai ka faɗa” “Lokacin da ta farfaɗo a asbiti, ta kalli idona tace min maza ba su da adalci, kansu kawai suka sani; kuma kasan dalili?” Ya tambaya ba dan ya na buƙatar amsa ba, dan kafin ya amsa masa ya ci gaba da cewa. “Dalilin shi ne; mu maza a kullum gani muke mune a gaba, dan haka dole duk abun da muke so shi za'a ayi, hakan ba wai kuskure ba ne, saboda mu Allah ya bawa girma, amma kuma su ma suna da nasu 'yancin. Domin ko addini ya basu 'yanci, daraja da kima, sai de ni kuma a yau ba ma duba hakan, sai namiji ya auri mace, ya zaunar da ita a gida, ya hanata rawar gaban hantsi, ya sa ƙafa ya take mata burinta da kuma 'yancinta, ga shi de ba ta son abun da yake mata, amma saboda ganin ita macace sai ta haƙura ta ja bakinta ta yi shiru. Kawu a mafiya yawan lokuta muna dannewa mata hakkinsu, suna da baiwa kamar mu, suna da shauƙi kamar mu, suna da zuciya kamar mu, duk abun da zai fusata mu suma zai iya fusata su, banbanci mu da su shi ne, su sukan iya jurewa abun su shanye a cikinsu, wata dan 'ya'yanta, wata dan iyayenta, wata ma dan mijin shi kansa, haka za ta jure rintsi da wuya. Kawu, Adawiyya ta shiga taskun rayuwa kala-kala, taga iftila'i da ban da ban, yanzu ne ya kamata ace ta samu jin daɗi da hutu, a yanzu ya kamata ace burukanta sun cika. Ni kuma ina son ta yi farin ciki, kuma na yi alƙawarin sama mata duk wani abu da zai dawwamar da murmushi a fuskarta. Ƙwallo mafarkinta ne, lefi ne dan na temaka wurin ganin ya zama gaskiya?!” Shiruuu, har bayan shuɗewar wani lokaci, a cikin wannan shirun Baba dake kishingiɗe ya miƙe zaune da kyau, cikin alfaharin kasancewar Zaid jika a gareshi, Kawu Abdullahi kuma nadamar kiransa da masa wannan kashedin yake. Kasa cewa komai ya yi, ya kashe wayar. Jin wayar ta katse ya sa shi sauƙe wayar. Sannan ya fita daga ɗakin, dan da ma niyyar fita yake, kiran shugaban nasa ya same shi. Shi ya sa ya tsaya ya amsa saboda muhimmanci kiran. Kitchen ya nufa, dan ya san ba za ta wuce can ba. Damm, zuciyarsa ta harba bindiga, lokacin da ya saka ƙafarsa a cikin kitchen ɗin, abu na farko da ya fara arba da shi shi ne, Wutar gas a kunne tana ci. Irin waɗanan dalilan ya sa baya san shiga kitchen, ko da magana yake san yi da Rhoda idan har tana kitchen sai de ya haƙura. Ba shiri ya ji kansa na juyawa, duniyar ta fara masa duhu, numfashinsa ya shiga kokawar ɗaukewa. Rabi dake wanke nama a sink ta juyo da sauri jin fitar wani kalar numfashi. “Ga ruwa” Cewar Rabi tana miƙa masa ruwa a cikin wani glass cup, Zaid da ke zaune kan kujera a falo ya ɗago da kansa ya kalleta. Kafaɗarsa ya daga ya na miƙa hannunsa tare da karɓar glass ɗin. Rabi ta zauna a gefensa tana shafa kafaɗarsa a sanda yake shan ruwan. Ita ta karɓi cup ɗin ta aje, bayan da ya kammala shan ruwan. Gefen fuskarsa take kallo cike da damuwa. Har zuwa lokacin tana shafa kafaɗarsa a hankali. “Na zubo maka abinci?” Zaid da ya cilla duniyar tunani ya girgiza mata kai, ya na jingina da bayan kujera, hakan ya sa Rabi ta ɗauke hannunta daga bayansa, ta dawo da shi ƙirjinsa tana masa tausa. Ganin har zuwa lokacin be dawo dai-dai ba ya sa tace. “Me yake damunka wai?” Kallon fuskarta ya yi na wasu 'yan sakkani, sai kuma ya kama hannunta dake kan ƙirjinsa, ya kwantar da ita akan ƙirjin nasa, ta yanda har
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112