Chapter 100
Chapter 100
sai ta ji kasala ta kamata, ta ji jikinta duk ba daɗi. Kafin ta fito daga banɗakin ma sai take jin juwa na ɗinbata. Da ƙyar ta iya ƙarasawa ta zauna a bakin gadonta, hannunta na dama dafe da cikinta. A dai-dai lokacin Zaid ya shigo ɗakin yana kiranta, ba ta samu damar amsawa ba, face binsa da kallo kawai da take, ganin yanayinta ya ɗarsa masa wani zargi a ransa. “Baki da lafiya ne?” Kanta ta girgiza masa tana miƙewa. “Lafiyata ƙalau” Be yarda ba, amma ba ya so ya takura mata, sai kawai ya gyaɗa kansa ya na kama hannunta. “Na fahimta... Kin shirya?” Kanta ta gyaɗa tana ɗan cije baki, saboda cikinta da take jinsa babu daɗi. “Raj!... Me muke a nan?” Muryar Rabi ta tambaya, a sanda ta ga Zaid ya kawosu wata football academy, makarantar da ta yi ta lokacin tana yarinya, dan a sanda Ummanta ke da rai nan take kawota training ɗin ball.‘As Roma Football Academy’ haka sunan makarantar. Zaid be amsa mata ba, sai fita da ya yi daga motar, sannan ya zagayo ta ɓangarenta, ya buɗe mata motar, mamaki ya ƙi barin kan Rabi, haka ta fito baki buɗe, sai bin wurin take da kallo, wurin da rabonta da shi kusan shekaru shida kenan. “Zuwa yanzu ta girma... Dan haka ba daga rukunin da ta tsaya za ta ci gaba ba, za mu turata cikin rukunin sa'o'inta” Cewar shugaban makarantar, yayinda Zaid da Rabi ke zaune a tsallaken teburin office ɗinsa. Zaid ya gyaɗa kansa, duk da ba yau ya fara faɗa masa hakan ba, tun ranar da ya fara zuwa makarantar shugaban ya sanar masa da wannan batun. Kuma ya yarda da hakan, shi ya sa ma ya kaita aka mata gwaji a asibiti, kafin ta fara buga ƙwallon da ta kasance burin rayuwarta. Juyowa ya yi ya kalleta. A dai-dai lokacin da ita ma ta kalleshi, idonta ya ciko da ƙwalla, bakinta har rawa yake, ta ma rasa abun da za ta ce da shi, sai kawai ta kafe shi da ido tana kallo. Da haka suka bar office ɗin, aka bata kayan da zata riƙa sakawa idan ta zo makarantar, wata jar jersy ce, da wandonta, shugaban ya sanar musu da cewar zuwa gobe za su dawo, domin za su mata gwaji, idan ta ci gwajin da za su mata, za ta iya fara karɓar horo tun daga ranar. Suna tafe a mota ledar kayan na kan cinyar Rabi, hannunta ta kai ta fito da jersyn ta ɗagata sama tana kallo. ‘ADAWIYYA’ shi ne abun da aka rubuta a bayan rigar. Ƙwallar da take ta shanyewa tun ɗazu ce ta gangaro kan kuncinta. Sai ta ga kamar tana rayuwa ne cikin mafarki, domin da ƙwallo a mafarki take ganinta, bayan hargitsin da ya ahigo rayuwarta sai ta manta da ƙwallon. Ta haƙa wani wawaken rami a zuciyarta, ta cilla burikanta na rayuwa, ta binnesu, don a lokacin gani take rayuwar tata ta zo ƙarshe, labarinta ma ya ƙare, komai ma ya ƙare. Shigowar Zaid rayuwata ya sauya komai, ya sauya yanda take kallon kanta, ya sauya yanda take ganin rayuwa, ya cika mata burikanta na rayuwa, duk abubuwan da take ganin ba masu iyuwa ba ne sun iyu, ta rasa me zata ce da shi, tace ta gode?, a'a, godiya ta yi kaɗan ta isar da shi, addu'a ita ce kawai abun da ya kamata ta masa, sannan ta ba shi ko wace kulawa, ƙauna da soyyaya. Ganin ya nufi hanyar Kaura ya sa ta share hawayenta, don bayan wani lokaci me tsayi, yau Allah ya yi za ta haɗu da ƙanwarta. Sai da suka fara zuwa suka ga Rhoda, kafin ta fice ita ɗaya, bayan ta da faɗa musu cewar za ta je ta ga ƙanwarta, Zaid be hanata ba, don shi ma ya na so su tattauna da Rhoda kan case ɗinsu, saboda suna kyatata zaton zuwa gobe za'a shiga kotu. Kanta tsaye Rabi ta shiga makarantar, masu gadi sai tambayarta suke, kan dalilin dena zuwanta makarantar, ita kuma tana amsa musu da rashin lafiya ta yi, kuma su ma sai suka yarda, saboda ganin tabon dake kwance a gefen fuskarta. Duk da sun ga sauyi sosai a tare da ita. Kafin ta kai ss3 har ta fara hawaye, saboda ba ƙaramin farin ciki take ciki ba, ta ƙagu ta haɗu da Mishal, don ta bata labarin abubuwan da suka faru bayan rabuwarsu. Cikin wata irin sa'a, tana isa ƙofar ajin ana kaɗa ƙararrawar break, hakan ya sa ta tsaya cike da zumuɗi tana san ganin fitowar Mishal. Sai da ko wani ɗalibi ya fice daga ajin, kafin Mishal ta miƙe tana muzurai, sai ciza baki take don tafiyar ma da ƙyar take, haka ta shiga taku cikin ƙarfin hali, har ta kai waje. Ba tare da ta lura da wanda ke tsaye a bakin ƙofar ajinsu ba ta fara tafiya ta na nufar playground. Rabi'a ta lura da yanayin tafiyarta, amma kuma ɗaukin ganinta ya sa ta ture komai tace. “Mishal!” Cak Mishal ta tsaya da tafiyar da take, sakamakon sauƙar sautin muryar yayarta da ta ji, yayarta mafi soyiwa a ranta, yayarta da take ji da ita, yayarta da take cikin halin damuwa na rashin ganinta. “... Kin ji abun da ya faru da ni!” Cewar Rabi, a sa'ilin da ta ɗiga aya a ƙarashen labarin da take bawa Mishal, suna zaune ne kan kujerun da suka saba zama a da, Mishal wadda idonta ya cika da ƙwalla ta kalli yayarta. Duk da Yazid bai samu damar ci mata zarafi ba, amma ta san yaya zafin abun yake, ta san irin baƙin ciki da ƙuncin da ake shiga, ta san zafi da tabon da abun kan barwa 'ya macen da ta fuskance shi. Ita ba ta da wani wayo sosai, amma ta san irin ƙasƙancin da mata 'yan uwanta kan fuskanta, idan har basu kai budurcinsu ɗakin mazajensu ba. Duk da ita Adawiyyan ta tsallake wannan ramin. “Yaya ina so na faɗa miki wani abu” Rabi ta share hawayenta tana kallon Mishal. “Kina kama da Aliyu, kuma na san ke ma kin san hakan, kina da danganta da shi?” Rabi ta yi murmushi tana ɗauke kai. “Wata ƙila idan na faɗa miki ba za ki yarda ba. Amma mijinki cousin brother ɗina ne, sannan kuma shi ne ƙanin mijina. Ɗan biyunsa ne, amma abun da ya shiga tsakaninsu ya rabasu ne... ban sani ba” Wani irin shiru ya gifta a wurin, ba ka jin komai sai sautin wucewar iska. A cikin wannan shirun, Mishal ta kunce ta kuma saƙa ya fi sau a ƙirga. Kenan wannan wanda take gani a tsallaken makarantarsu shi ne Zaid ɗin da Adawiyya ta aura?. “Da... Da ma Raja shi ne Zaid ɗin?” Mamaki ya kama Rabi. ”Kin san shi ne?” Mishal ta gyaɗa kanta da sauri ta na share ƙwalla. “Na sanshi...” Rabi ta yi ajiyar zuciya tana ɗaga kanta sama. “Ya kamata mu san abun da ke faruwa a tsakaninsu” Rabi ta faɗi tana sauƙe kanta ƙasa. Mishal ma kai ta gyaɗa mata cike da gamsuwa. “Yau idan muka koma gida zan tambayi Aliyu” Rabi ta yi murmushi. “Ni kuma zan tambayi Zaid” Sai kuma suka yi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112