Skip to content

Chapter 94

Chapter 94

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,209 words 0 views Progress saved
Download Book

_*TO*_ _RAHAMA ALIYU_ _*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR RAHIM*_ *🅿105* Yara suka fara taruwa a kanta sai kurma ihu! Take, da sauri wannan matar ta d'ora ta a hanyar gida tana tafe tana kuka kamar shashasha sai surutai take. ********************** Mota a ka kawo su har k'ofar gida cike da kayan arziki, yaran unguwa suka yi dafifi suna shafa motar suna tsalle har yanzu sun kasa sabawa. Yara matasa suka kwashe kayan da suka zo dashi suna shiga gadan dasu,, suka bi bayan su duk jikinsu a sanyaye,, Buba direba yaja motar sa ya tafiyar sa,, suna k'okarin shiga gidan ana k'okarin futo da Sallau a rirrike jikinsa yayi tsanani, Lantana ta rafka salati gami da fashewa da kuka tana fad'in "Ina zaku kai shi"? Walidi Yace" Asibiti za a kaishi domin jikinsa yayi tsanani, nan ta bisu a baya tana kuka, Uwa! Kuwa gida ta shige tana matsar hawaye, Sadiya da Iya na tsaye tsakar gida cike da tausayin Sallau Uwa ta shigo gidan, kallo suka bita dashi ganin tana matsar hawaye domin sun d'auka ko ganin jikin Sallau ya rikice yasa ta kuka, zauna tayi a tsakar gidan tana kukan nadama. Ko minti goma ba'ayi ba sai ga Shamsiyya ta shigo gidan tana kurma ihu, ta zube gaban mahaifiyar ta tana fad'in"Shikkenan Uwa! Aiki ya lalace "yan sanda sun kama Arrama jiya da yamma" "Don Allah ni yi min shiru da zancan wani Arrama in zaki hak'ura ki hak'ura ki zauna inda Allah ya aje ki, ni kam. na dawo daga rakiyar wannan duniyar me cike da rud'u" Uwa! Ta fada tana sharb'e hawaye Shamsiyya ta d'ago kai tana kallonta cikin mamaki tace"Ban gane abunda kike nifi ba kina nufin in rabu da maganar aure na da Sarki! Ko me"? "E abunda nake nufi kenan, Domin babu yadda za'ayi ya aure ki yana da Balaraba" Shamsiyya ta fashe da kuka tana fad'in "Uwa kar muyi haka dake kinji, kece fa kika yi mana alk'wari cewa ko da zakiyi yawo tsirara sai in da k'arfin ki ya k'are zaki tsaya min gurin ganin buk'ata ta ta biya" "Ke ni ki k'yaleni don Allah inji da masifar da nake ciki, ubanki ya sake ni saki uku, ga masifar Ku ta same ni, Nazo a banza zan koma a wofi ni yanzu waye zai aure ni" ta k'arashe maganar tana rusa ihu! Shamsiyya ta dafa kirji tana fad'in "Baban bamu ne ya sake ni yau she haka ta faru"? Nan Uwa ta kwashe duk abunda ya faru ta fada mata har da zuwan su gidan Sarki! Shamsiyya ta kwanta tana rusa ihu! Babu kamar wacce uwarta ta mutu *********************** Suna zaune gaban Mama Fulani duk su ukun sai shi da ya zama cikon na hud'un,, yana hakimce kan kujera. Mama tace "Salati goma da Annabi" Duk suka amsa da "Sallalahu alaihi wasalam"Minti goma tsakani tayi addu'a ta shafa suka shafa suma,, ta kalli Sarki a nutse tace" Babban abunda yasa na tara ku anan shine, in ja muku kunne gami da nasiha, mussaman kai" tafad'a tana nuna shi da hannu, kansa ya sunkuyar kasa, ta cigaba da cewa"Allah ya d'ora maka wani babban nauyi a kanka na mataye har uku, dukaninsu suna da hakki a kanka babu wacce tafi kowa a gurin ka sai wacce tafi kyautata maka a cikinsu, don haka ina mai gargadin ka da ka rike amanar su ka bawa ko wacce hakkin su,da ya rataya a kan ka" Yace"Insha Allah Mamana kar ki damu" "Ku kuma na dawo kanku" Tafad'a tana kallonsu duk su ukun, ta cigaba da cewa"Ku yi kokari Ku kula da mijin Ku Ku fahimci me yake so da Wanda ba ya so, yi nayi bari na bari Ku yi k'okarin zama lafiya da juna domin Ku kwantar masa da hankali gurin ganin ya rik'e amanar Ku, da jagorancin mutanan gari da ya hau kansa, ni Wannan kawai zakuyi min Ku faranta min, insha Allahu , kuma idan wani sab'ani ya shiga tsakanin ku dashi, ba fata nake ba,, zama ya gaji haka zo mu zauna zo mu sab'a haka duniyar take, to sai Ku same ni Ku sanar dani insha Allahu komai zai zo da sauk'i" "Mama Insha Allahu zaki same mu masu zaman lafiya da juna" Balaraba tafad'a kanta a kasa,, Azima da Halisa ma Abunda suka ce kenan, Mama tace"Masha Allahu Allah yayi muku albarka" Ameen suka ce gaba d'ayan su. ************************ K'arfe shida na yamma, gurin Walima ya d'auki harami ya tsaru ya k'yayatu sosai Shahid da Shatima ne suke ta kai kawo a gurin suna saukar abokan su, da suka fara zuwa. Suna sanye da wata arniyar gezna wacce ta amsa sunanta anyi musu dinki iri daya hula da takalmi duk kalar shaddar ne,, ruwan toka kenan sai shek'i take aikin ya. zauna a jikinta. Suna zaune a falonsa ko wacce kujerar ta daban da "yar uwarta babu wacce tayiwa " yar uwarta magana, suna sanye da kaya iri d'aya Shadda ce, sky blue anyi musu d'in ki Aliya taji sirfani duk gaban rigar ko wacce ta d'ora d'auri dai-dai da kwalliyar ta, gwal kuwa kamar yayi magana hannayen su da wuyan su, takalman su iri daya ne, Azima da Halisa sun sha kwaliyyar fuska, babu Mayafi a jikinsu, Balaraba kuwa babu laifi fuskarta babu komai sai farar hoda da kwalli da ta zizara a idonta, bayan haka ko man leb'e bata sa, amma haka bai hana bayyanuwar kyanta ba, ta yafa k'aramin mayafi Wanda ya sauko ya rufe mata k'irji. A hankali yake sakko wa yayin da k'amshin tura ransa ya cika gurin , dukanin su suka mai da su kansa,, Kallo guda tayi masa ta d'auke kanta gabanta na fad'uwa. Yana sanye da shadda irin jikin su Sak,, anyi masa dinki irin na zamani,, me falmaran wacce yaji sirfani me tambarin sarautar su,gaba da baya hular shi ma da yanki shaddar aka had'a ta,, kafar shi sanye da wani ruffan takalmi mai gashi-gashi sky blue hannunsa daure da agogo na zallahar azurfa, ya tsunsa ma zobuna ne manya-manya masu d'auke da tambarin sarautar su. Cikin nutsuwa ya k'araso gurin su,, Fuska babu yabo babu fallasa yace"Ku tashi muje" a nutse ta mike jin abunda yace, gaba yayi suna bin shi a baya,, sai ga Shahid da sauri ya tare shi tare da wasu fadawa su uku suna take masa baya, Shatima yace"Kuyi tafiyar ku kawai,, suka ce "An gama ranka ya Dade, magana yake masa k'asa-k'asa, tsayawa yayi yana d'an hararsa, shi kuma ya sa dariya, yace" Hakane mana sai kayi gaba ka bar amaran naka a baya kai fa d'an gata ne" banza tayi masa yana d'auke kai da alama yau "yan muskilancin nasa na kusa,, Shatima ya k'araso tare da su Balaraba dole suka tilas tashi ya shiga tsakiyar su,, suna tafiya su uma suna take musu baya. Tunda futowar su har zaman su a masu hotona da vidio suke aikin su, marok'a duk sun cika gurin da roko, sosai gurin ya cika ya tumbatsa da mutane kowa sai farin ciki yake, ciki kuwa babu " yayan Waziri Zayyanu ko guda. D'aya suna can bakin ciki kamar ya kashe su, jin cewar har governor sai da ya hallarci gurin. Walima tayi kyau sosai an raba kaya naci Dana sawa

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108