Skip to content

Chapter 7

Chapter 7

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,230 words 0 views Progress saved
Download Book

KUDI* *GIMBIYA BALARABA* πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š _in kana bukatar cigabansi ga number nan_ 08089965176 [04/05, 03:05] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *✍🏻writting by* *Binta Umar* _*MAMAN ABDUL WAHABU*_ _Bissimillahi _Rahamanir rahim_ *πŸ…Ώ11* Sallau ya taso a fusace Sallau ,yafito gami da cewa "wai menene kin tashe ni ina bacci" Sai tafashe da kuka tana nuna su Atika da hannu tace"ga sunan suna kulla min sharri a gurin Ubanku ,har da zagina" Ai ko sallau ya yi tsalle ya gaurawa Atika Mari yana zaginta ta Uwa ta Uba,kwata kwata bai lura da Malam Tanko dake tsaye a gurin ba. Tanko yace"yanzu Lantana yaushe yaran nan suka zage ki Dan sharri" to tunda Abin ya zama haka zan dauke yaran nan daga hannunki ,ya mai da idonsa kan Sallau dake tsaye yace"kaji kunya sallau ,da zaka din ga biyewa Uwarka da duk Abinda tace da kai , Allah ya shirye ka,ya mai da idonsa kan su Atika yace su koma ciki ,kafin yadawo daga masallaci. Yana fita Sallau ya riqa zaginsu shi da Lantana,sukayi masu shiru ,Lantana tace baza su koma ba cikin gidan ba tunda suka fito sun fito kenan ,sai subari Ubansu mai daure musu gindi ya dawo sannan. Bayan Sun fito daga Massalaci Tanko ya tsaya shida Amininsa yake fada masa halin da a ke ciki. Budar bakin Malam iliyasu yace"mai zai hana muha da Atika da Yunusa mana ina ganin hakan zaifi. Malam Tanko yaji dadi hakan ,ai nan suka tsayar da Magana. Bayan sun karya da kansa ya fita dasu yasa su a mota ban da Atika domin yafada halin da ake ciki. Tana kuka suka rabu da "yan Uwanta. **** Lantana kamar ta mutu jin cewar Atika zata Auri yunusa Dan gidan Malam iliyasi ,ita San samunta yaran suyi tazama babu Aure sabida tsabar qiyyaya. Ranar daurin Aure Abin sai yabawa jama'ar dake gurin Mamaki jin ana daurawa Uba da "ya Aure. Da Labari ya iski Lantana gurin daurin Auren tafito tamkar mahaukaciya tariqa dure duren Ashar Da kyar su Sallau suka jata suka mayar da ita gida. Tace"Yanzu Sallau Abinda Malam zai yimin kenan ,ya muna furce ni ,Ashe Aure zai yi ban sani ba niko mai zan yiwa Malam in wuce bakin cikin da ya kunsa min" Sai ta fashe da kuka har dasu fyatar majina. Sallau yace"ki rabu dashi Lantana,mune maganin Matar tasa wallahi ,tunda tasa ki zubar da hawaye Sai mun hanata zaman lafiya" Maman yace "kwarai kuwa sai mun daukar miki fansa a kanta" Sai tai ta shi musu Albarka ,tace"ai dama nasan zaku share min hawaye shi kuma Malam din zai shigo ya same ni wallahi" **** Lantana babu irin cin mutumchin da bata yiwa Malam Tanko ba ,ya share ta ,kawai bai kulata ba ya cigaba da hidimarsa, Gidan Malam Ilayisu nan a ka kai Atika,sosai Tanko yayi mata kayan daki babu laifi ,nan ma da labari ya iski lantana ,tai ta zuba ruwan bala'i a gidan ,tana cewa Tanko ya kwashe dukiyar "yayanta yayiwa wata banza kayan daki ,ai "yaya maza sune "yaya A takaice dai ranar Lantana bata barsu sun rintsa ba. Ashe Abu Na gaba, Sabida kayan dakin Amaryar Malam Tanko iri daya ne da Na Atika ,da Alama duk shi yayi musu. Wata makociyarsu tazo tana tsoguntawa Lantana ,Aikuwa "yan jeran nafita ,suka shiga dakin Amaryar ita dasu Sallau ,duka wargitsa shi,gami da debo kwata suka yaba jikin gadon da tsakiyar dakin ,sannan suka dinga kuza ruwa a tsakiyar gadon da dakin,sai da suka jiqa katifar jagab sannan suka futa daga dakin ,gami da barinshi a bude. Ko da "yan kawo Amarya suka zo Lantana Na kuryar dakinta ta tasa redio tana ji ,tana jin shigowarsu sai ta rage redio n tayi lif tana jiran me zai faru. Abin Mamaki gami da daure kai dak in suka gani a bude ,suna San ya kafafunsu ciki suka ga Abin mamaki ,Komai a fashe ga katifa jagab dakin yana ta warin kwata, Matar Liman ,ta ce"innalilahi wa'ina ilayi rajiun"! Ai ba haka muka bar dakin nan ba,kai! Jama'a wai kishi hauka ne? Lantana Na jiyo Abinda take cewa sai tafito a fusace tana gyara daurin zaninta ,Dan kwali a hannu, Ta nuna Matar liman da hannu tace"ke Shattu bana son munafurci da kankanba ,ehe! Duk wata kutun gwila da kuka hada naji labari da sanya hannuku gurin bawa Malam ,waccan Mutsiyaciyar yarinyar tsintaciyya wacce ba'a San daga in da take ba ,wato ni za ai wa rufa rufa ,an lullube kura da fatar Akuya ,an dauko Mayya an kawo min gida salon tazo ta leshe ni da "yaya Na,to wallahi baza ta sabu ba ehe!! Tafada tana buga cinya cike da neman tashin hankali! *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* _IN KANA BUKATAR CIGABANSHI GA NUMBAR NAN_ 08089965176 [04/05, 03:05] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *✍🏻writting by* _*BINTA UMAR*_ *Maman Abdul Wahabu* _Up_ _up_ _up_ *BINTA UMAR FAN'S* _INA MUGUN YINKU SOSAI DA SOSAI INA JIN DADIN YADDA KUKE KAUNAR NOVELS DINA ,NAGODE DA GOYAN BAYANKU DARI BISA DARI_ _*HAKIKA BANI DA BAKIN DA ZAN YI AMFANI DA SHI GURIN GODE MUKU ,SAI DAI IN CE ALLAH YABARMU TARE ,ALLAH YABAR KAUNA TA DAN ALLAH*_ ❀ *"YAN QUNGIYAR ZAMANI WRTERS ASSOCIATION* _INA YINKU OVER ,MUSSAMAN ,RAEL SHAXXI ,HUSAIN 8K "YAR MUTAN ARKALLAH ,HAFSAT SISI ,HALINKU YANA BURGE NI HALINKU ABIN KOYI NE_ *ALLAH YAQARA DAUKAKA ZAMANI* *πŸ…Ώ11* Shattu tace"kinga lantana mu ba tashin hankali ne ya kawo mu ba Alkairi ne ya kawo mu duk dai wannan da yayi nagari kan shi," takarashe magana tana kama hannun Amaryar Malam Tanko Da nufin shigar dai ita cikin dak in' Mutanen dake ciki suna ta faman tsane ruwan dake kwance gurin ,suka ce "Aa shattu yanzu in kinshigo da ita nan ina guri ,ki kai ta makota tukkuna mugama gyara gurin. Duk abinda mutum yayi kansa. Shatu tace "to bara muje gidan Baba Laraba I Dan kun gama sai kuzo Ku fada, Da sauri Lantana ta tare hanya tana buga cinyarta tace"Ahayye nanaye Akin bur in ji tusa ,dole Dan ace da Mijin iya baba ni warki CE daidai da qungun kowace shegiya,ihe! Muna fukar Banza kawai! Shattu tace"wai Lantana Lafiyarki kalau kuwa kishi fa ba hauka bane"A tunani Na zaki dauki Suwaibah a matsayin "yarki tunda kin San kome ya faru da rayuwarta" "Ke!! Dakata shatu" Lantana tafada ta na turo dauri gaban go shi Tace"dadin baki zaki yi min Dan bake a kaiwa kishiyar ba. Baki San yanda zafin Abin yake bane shiyasa kike shishshigi a kan Maganar, Nafada Na kara fada ni Lantana,in dai ina raye babu macan da ita sa in zauna da ita ,ko wacece kuwa" Ta karashe maganar tana buga cinya. Shatu kawai sai taja hannu Suwaiba ,wacce take ta kuka tsora ya cika ta,dama tuntuni take jin labarin matar a bakin mutan gari. Lantana ta koma ta zauna ,gami da kunne redion ta tasaka kasat din wakokin bar mana coge tana ta zubda habaici a gidan,jira kawai take su tanka ayi wace za'ayi Su dai sukayi mata shiru suna Aikinsu, Bayan da suka gama ne daya ta tafi domin Kiran shattu ta shigo da Amarya dakinta. To can kuwa gwaggo laraba

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108