Chapter 32
Chapter 32
irin kallo, a ya mutse yace"Karya nake kenen" Murmushi Maddibo yayi yace"mai da wukar malam, ni zani gurin Gimbiya in ci abunci, ko injiraka ne" A hasale yace"wallahi zamuyi fada dakai, kar ka kara sakoni cikin maganar ka da wannan yarinyar in kana son kanka da arziki, kai daka ga zaka iya kaje kayi, amma ni, kasan nafi karfin inci kazantar ta" Daga kafada Maddibo yayi alamun abunda ya fada bai dame shi ba,yace"Ni kam zanci har da side kwano, sai na dawo" Banza yayi masa har ya fuce daga dakin. Maddibo na futa wasu bayi suka shigo Maza biyu mata biyu Wani irin kallo ya watsa musu cikin tsawa yace"wane shegen ne yace ku shigo min daki,"? Kasa sukayi da kansu dukkaninsu Cikin tsawa ya cigaba da cewa"ni kuturo ne da komai sai kuce sai kunyi min, nace bana so, nace bana so, amma sabuda tsabar naci! kullum sai kunshigo min daki da sassafe! kufuce ku bani guri" yafada cikin tsawa! Zubewa sukai gabansa, kamar wasu masu neman gafara, wannan abun ya kara tunzura masa zuciya, a zafafe! yace"me kuma zanyi muku,, bakuji abunda nace ba? Mariya ita ce baiwar shi wacce take kula da gyaran bangaran shi da da kai masa abunci da daukewa in ya kammala goge-goge da share-share, ita ce tace "Ranka ya dade don Allah kayi hakuri ka bari munai maka hidima a shashen ka, domin aikin mu ne,hakan ka gafarce mu, ranka ya dade, zamu maka gyare-gyare ne" Wani kallo ya watsa mata, wanda yasa ta sunkuyar da kai kasa, babu shiri,domin idanunsa duka ya ware mata,tunda take dashi ba ta taba ganin ya bude idonshi haka ba, kullum a lumshe suke, ko kallon ka yake, baya budewa sosai kasa-kasa yake kallo. Yace"kece Sarkin iyayi ko, wacce tafi kowa iyawa, kowa yayi shiru zaki damu mutane da magiya,Ok ku fuce min a daki, tukkuna inyi abunda zanyi in futa,sai kuyi abunda zakuyi" Ya karashe maganar yana hararasu,sai kace su sukai masa laifi Daya bayan daya suka fuce daga dakin, suka tsaitsaya a falo suna gulmarsa, kasa-kasa Mariya tace"yau da alama a kwai abunda yake damun Yallabai wannan masifa haka" Wacce take kusa da ita tace"kuma hakan ba halinsa bane,shi dai kyaleshi da muskilanci gami da shariya" Mariya tace"gaskiya akwai wani abu dake damunshi" Haka dai sukayi cirko-cirko a falo suna magana kasa-kasa, gefe kuma suna jiram fitowarsa,domin su fara aikinsu Yana kokarin mikewa ne daya daga cikin wayoyinshi ta hau gyara, ko kallonta bai yi ba balle ya dauka, toilet ya nufa, cikin zuciyarsa sai mita yake, ya tsani kamarshi azo ace sai an masa komai, yana da lafiya da kuzari Allah ya hore masa sai ya tsaya an masa bauta, shi sai yake ganin wannan cutar kai ne, a rayuwar shi ya tsani yaga ana wani jin tsoransa,kamar ayi masa sujjada, kamar dai yadda suke masa, shiyasa kullum cikin yi musu tsawa!yake, baya son wannan rawar jikin da suke masa, Sarki!bayason raini ko kadan, shiyasa abunda Balaraba tayi masa ya kasa bacewa a zuciyarsa,dalili kuwa shine tunda yake a rayuwarsa babu mahalukin da ya taba yi mishi abunda tayi Toilet dinshi abun kallo ne, sosai in ka shiga baza kayi sha'awar futowa ba,domin har wani sanyi-sanyi yake,duk abunda mutum yake bukata a kwai a ciki Jaccuzi kuwa har biyu ne a ciki, sabuda girman toilet din, a nutse ya shiga ya hada sabulai na mussaman yayi wanka, ya futo ya nannade jikinshi da towol ya dauki karami yana goge kanshi, Kai tsaye dressing mirrow dinshi ya nufa, ya tsaya jikinshi a fara shafa mayukanshi masu kyau da tsada, ya taje sumarshi sai kyalli take,itama ya sanya mata mayuka, Kwantaccan gashin dake fuskarshi yake gyarawa sosai ya gyara Sajanshi ya tsaida gemunshi iya inda yake so, sai fuskar tafito tayi wani mugun kyau da haske,kalar fatarshi ta fito sosai,annuri ne kawai yake futa a fuskarshi, Wayarshi ce take kara alamun kira,bai saurare ta ba,sai da ya futo da kayan da zai sanya,sannan ya zauna gefan gadon ya dauki wayar yana dubawa a nutse. Khalifa sunan da ya gani yana yawo kan fuskar wayar, Khalifa dai yaron Waziri ne, kani ga Maddibo, kenan yaron bashi da kunya ko kadan shiyasa basa shiri da Sarki! ko kadan yanzu ma yayi mamakin ganin kiranshi, sai da yagama yangarshi sannan ya dauko, "Assalamu alaikum" Daga daya bangaran Khalifa yace"Yallabai barka da asubah" "Barka kadai, Khalifa ya kake"? " Lafiya yallabai, dama Baba Waziri ne yace kazo yana neman ka" Shiru yayi na tsawon minti uku,kana yace"Ok ya fita fada ko yana gida"? "Yana gida" "Ganinan zuwa" Yafada yana kokarin kashe wayar, Mamaki yake kiran me Waziri yake masa Allah yasa alkairi ne, Tsaf ya shirya cikin wani uban yadin filtex me ruwan sararin samaniya, an mishi dinki irin na sarauta sosai yayi masa kyau, kafarshi saye da takalmi irin nasu shima kalar kayan jikinshi, wayoyin shi ya diba ya futa daga dakin, suna tsaye sukaji futowarsa, da sauri sukayi kasa da kansu, ko kallonsu bai yi ba ya fuce daga falo, Wasu bayi maza su biyu suna tsaye bakin kofa,suka zube suna kwasar gaisuwa, yana tafiya yake amsawa, suka mike da sauri suka rufa masa baya Duk wasu bayin dake kaiwa da kawowa a filin gurin tsayawa sukai suna gaidashi, har sai da ya wuce sannan kowa ya koma bakin aikinsa, *Ikon Allah Sarauta da mulki sai mai shi*😇 *Comment* *Vote and Share* [10/07, 05:14] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®REAL BINTU BATULA👄* *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*Zamani Writes Association*_🤝🏻 _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{RAHAMA ALIYU}``` *🅿44* ```Bisimillahir-rahamanir-rahim``` Waziri na zaune a falo tare da uwar gidanshi, Hajiya Rahamatu, wato mahaifiyar su Modibbo, wacce suke kira da Mama, macace mai mutukar kirki da maida dan wani nata, tana da kara da kawaici,da kauda kai a kan abunda babu ruwanta, shiyasa kullum cikin tsawatar da "yayanta take, a kan su lura da duniya mussaman in taga suna jiji da kai da nuna su " yayan sarauta ne, kullum takance musu,babu wanda Allah ya ware tsakanin tsakin bayinsa,me mulki ko mara mulki talaka ko me kudi,sai wanda yafi bauta masa. Wani lokacin idan Waziri yana wani abun na son zuciya takan iya bakin kokarinta gurin ganin ta hanashi, haka zasuyi ta rigima dashi, Amaryar shi ce,halinsu yazo daya,duk wasu abubuwan da yake yi ita take ingizashi,yake da girmanshi da komai,bashi da gaskiya kullum cikin shirya manakisa yake. A nutse Sarki! yayi sallama cikin falo,Mama ta amsa masa cikin sakin fuska, tana gyara masa gurin zama, fuskar sa ya saki sosai ya je ya zauna kasan kafafun ta kanshi a kasa yace"barka da asubah Mama" Kanshi ta shafa tace"barka kadai, Almansor,yau sharabon da in sanya ka a idona" Sosa kansa yayi irin na sabo yace"Yace Mama Ayi hakuri, a gafarce ni" Dariya tayi kawai tace"ai nasan hali baka son mutane dama" "Mama a dane wannan" yafada yana sosa kansa Wani irin kallo Waziri yayi masa yace"kema ai da neman magana kike wannan yaron da baya son jama'a ko kin manta da halinshi, wai kuma a haka akeso a bashi mulki" Shiru Mama tayi jin abunda mijin nata yace, tasan yanzu zai kauce hanya Girgiza kai kawai Sarki! yayi ya dago kanshi fuskarshi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108