Skip to content

Chapter 56

Chapter 56

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,287 words 0 views Progress saved
Download Book

sama Sai sannan ya mai da hankalinsa kan Halisa dake tsaye, tana cika tana batsewa duk wani abu da ya faru tsakanisa da Balaraba ta gani mussaman had'a hannu da suka yi" B'ata fuska yayi kad'an yace'' kin zama dogariya ne,wai duk gurin zaman nan bai miki ba sai dai ki tsaya a kai na" Cikin fushi tace"ai banga fuska ba, tunda ka kawo wacce kakeso har gida,ita kuma wannan mai sifar karuwan fa" Hararata yayi yace"ki iya bakin ki wallahi ranki zai mugun b'aci a kan wannan yarinyar matar Moddibo ce in sha,Allahu" Wata dariya ta shek'e da ita,ta nemi guri ta zauna, cikin jin dad'i tace" gaskiya Ya Yusuf ya iya zab'e tsaf wannan zata yi masa wayo dubi idonta,don Allah,wai me ma ya kawota shashen ka ne, kuma meyasa har ka zauna da ita da k'anwarta guri guda" ta k'arasa maganar da damuwa! "Sai ki bari sai ya zo sai ki tambaye shi,amma yanzu ni bani da lokacin baki wannan amsosin naki" Mik'ewa yayi daga gurin ya barta zaune,babu shiri ta mik'e tana bin bayansa har ya zauna kan wata kujera me cin mutum d'aya, ta zauna a wacce take fuskantar sa, wata k'aramar drowar ya jawo k'asan kujerar ya futo da wani k'aramin littafi irin na addini yafara dubawa, tunda taga yayi wannan zaman tasan ba zai saurareta ba, duk abunda zatayi kuwa,dole ta jira ya kammala tukkuna, mintuna goma ta gaji da zaman gurin sai ta mik'e ta fa kaici idonsa, ta hau sama tana laluben inda Balaraba take, cikin sa'a ta ga wani d'aki a cikin d'akunan dake barandar a bud'e,kai tsaye d'akin ta nufa cikin k'asaita ta tura k'ofar da k'afarta,ta shiga babu sallama, Balaraba na zaune gefan gado ta cire hijab d'in, tana sanye da doguwar riga,cotton mai taushi,tana da yankakken hannu, sai tayi amfani da k'ara min hijab me hula, irin na Larabawa, tayi mugun kyau,kamar wata balarabiyar k'asar Oman, Halisa sai da Gabanta ya ganin ciki da k'asaitar Balaraba,fata luwai sai kace me rayuwa a kasar waje,ko ita albarka,ita da take rayuwa a cikin jin d'adi. Dukkaninsu k'ofa suka kalla jin a bugo da k'arfi an shigo, dogarewa tayi bakin k'ofa tana watsa musu kallo, ta kalli Balaraba a k'asan kan ce,tace"zo ki rufe min k'ofar nan,ke me kama da "yayan bayi"!! D'as!d'as!d'as! K'irjin Balaraba ya fara buga jin furucin Halisa, cikin sigar izgili da nuna ke awa! kuma baki isa ba,tace" a matsayin ki na wa! da har xaki bada umarni abi,ki bari sai kin kai matsayin zama cikkakun mutane sai ki bada umarni,amma dai yanzu baki isa ba" "Ke ni kike fad'awa magana,har kike k'okarin zagina,munafukar Allah, ta'alah macuciya, an ga gidan sarauta an lallab'o, to bari kiji,shi kanshi Moddibo baza ki same shi ba,balle kuma Sarki! Wannan nawa ne ni d'aya" Halisa ta k'arashe maganar tana dungurewa Balaraba kai, abunda Halisa bata sani ba shine ba'a nuna Balaraba da d'an yatsa,komai girman ka kuwa sai ta nuna maka ruwa ba,sa'an kwando bane, Wani ba hagon mari ta tsinkawa Halisa a fusace! Sam!ba tayi tunanin abunda zai je ya dawo ba. Ihu Halisa ta kurma! tayi kan Balaraba da duka sai zaginta take,abinka da sabo da fad'a tuni Balaraba ta tare ta,su kafara kokawa abun mamaki, nan Balaraba ta yar,da Halisa a k'asa, saboda ita bata iya fad'a ba,ga jikin Hutu,babu k'wari, sosai Halisa taji ciwon fad'uwar ta k'asa, ko da mik'e bata daddara ba,ta k'ara yin kan Balaraba a karo na biyu, tayi nasarar fuzge mata hijab d'in wuyanta ta cire hular kan nata,ta tattaro gashin kan Balaraba ta rik'e sai ja take,tana gaya mata maganganu na b'atanci kuma sai ta d'aure ta,tunda ta sake tayi kokawa da ita, Balaraba kuwa k'okarin kwatar kanta takeyi hannuta ta kama ta murd'e! da k'arfi, Halisa ta saki ihu,babu shiri ta sakar mata, kai tana duba hannunta tana cije baki, ki take kamar wacce tayi targad'e, ganin sunk'i su dai na fad'an yasa,Sadiya sauka k'asa da gudu, domin taje ta fad'awa Magajin Sarki, yana zaune,a inda yake,kanshi k'asa yana duba littafin hannun sa, ya ga Sadiya gabansa tana zare ido,d'ago kai yayi yana rufe littafin hannusa, yace"dukan ki tayi kike haki! haka"? Girgiza kai tayi cikin tsoro tace" Yayarmu fad'a suke yi da wannan da tazo gun ka" Falon yake bi da kallo, cikin mamaki, ina Neman Halisa, M'ikewa yayi kawai ya rik'e hannun Sadiya suka nufi sama, Yana tura k'ofar yaga abun mamaki da d'aure kai, Balaraba ce, rik'e da wuyan Halisa ta mak'ure a bango,ita kuma Halisa duk tayi wujiga-wujiga,sai k'okarin k'watar kanta take,ta kasa,idanunta duk sun firfito waje, k'arasawa yayi ciki har inda suke, batare da yace,komai ba ya fara, k'okarin b'anb'are hannun Balaraba dake wuyan Halisa, sanyi da taushin Hannunsa,suka sa ta dawo hayyacin ta, kallonsa tayi da idonta wanda suka kad'a saboda b'acin rai! Hannunta ya matse cikin nasa,shima ya zuba mata idonsa,kamar yarda tayi masa, dafin! dake nasa idon ya fi nata,dole tasa, ta risinar da idonta, ta zare hannuta daga nasa ta koma gefe guda tana huci! Halisa kuwa zubewa tayi a gurin tana nufarfashi,na wahala! Dariya ce take cinsa ganin yadda Halisa tayi wurjanjan, cikin yanayin maganar sa yace"Halisa,da ilimin ki da komai kike kokawa sai kace a jahiliyya,in ita ta saba da dambe,ke sai ki biye mata,gwara ma da tayi miki duka" Yafad'a babu damuwa a tare da shi. Hawayen b'akin ciki ne ya fara zubowa Halisa,tace"abunda zaka ce kenan ko"? "To me zan ce miki me ya kawo ki gurin ta,ko na aiko ne"? Mik'ewa tayi tana gyara alkyabar jikinta,tace" zaka ce na fad'a maka wannan k'ask'antacciyar bata isa ta dake ni a banza,ba tana a matsayin baiwa ta,wallahi sai na wulak'antata" Siririn murmushi ya saki iya leb'anshi ya d'an kalli Balaraba kad'an sai kuma ya kauda kansa,ganin ta babu hula,ga botiran rigar jikinta duk sun zube, saboda fad'a duk saman k'irjinta a waje, Ki yayi yanayin jikinsa na sauyawa, Matsalar shi kenan shi mutuk'ar zai ga wani shashe na jikin "ya mace shikkenan sai sha'awarsa ta motsa, ya cije leb'anshi na k'asa kad'an yace" Wannan tafi k'arfi ki Halisa,kika tab'a ta kin tab'a zuciyar Moddibo,ki bari zan mishi magana ya ja mata kunne" Hannunta ya rik'e suka fara tafiya, domin barin d'akin,tace"wato ni ba zuciyar ka bace,kenan har zaka kasa d'aukar mataki a kanta dubi irin dukan da tayi min" Kamar zai yi dariya, yace"muje k'asa in rarrashe ki, ko" mamaki sosai yake na k'arfin halin Balaraba, kizo har gida kina fad'a da masu gida, da alama dai yarinyar tana da aljanu. https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ _*DEDIGATED*_ *_TO_* ```RAHAMA ALIYU``` ```BISIMILLAHIR- RAHAMANIR-RAHIM``` *🅿64* Da harara Balaraba ta bisu dashi,har suka futa, Sadiya ta matso kusa da "yar uwarta tana wasa da hannuta tace" don Allah yayarmu ki daina fad'a da ita baki ga ita "yar Sarki bace,kar ki jawo a kulle mu,kinji tana cewa sai ta d'aure ki" Ta k'arashe maganar tana sharar hawaye Tsawa! ta buga mata tace"rufe min baki,duk bake kika jawo ba, wallahi duk sanda na k'ara ganin kinje gurin wancan mutumin sai ranki ya b'aci,ki ko kiranki yayi kar kije" Kwanciya tayi kan gadon tana kuka,Usuman

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108