Skip to content

Chapter 45

Chapter 45

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,241 words 0 views Progress saved
Download Book

tana yi yace"lafiya lou alhamdulilahi" "Salihu yace " wai kana neman babanmu" "Eh hakane"? yafad'a ba tare da ya kalleta ba. " Bayanan amma bari in sanya yaro ya kira maka shi yanzu" tafad'a tana kokarin tafiya, sai wani murgud'a mazaunai take,wai dole sai ta burgeshi, Tare suka jera da Salihu domin futa bakin lungu ko zata ga Walidi ta tura shi ya kira baban nasu domin tana ganin wannan bak'on nasa na alkairi ne. Kanshi a kasa yayin da ya zuba hannuwansa duk biyun cikin aljihun jins d'in dake jikinshi,yana jimanta labarin da Salihu ya bashi a kan Balaraba, lallai in ko hakane yarinyar ba matar aure bace. kanshi a kasa ya fara jiyo wani mugun k'amshin turare mai dad'in gaske, d'ago kansa yayi, karaf! suka had'a ido ta cikin gilashin dake idonshi yake kare mata kallo, a kwai hasken fitala tunda da wuta lokacin, d'auke kanta tayi cikin izza! da tak'ama take tafiya, tana sanye da wasu riga da wando pakistan ta masu kalar blue da pink da adon wasu manya-manyan stons masu shek'i ta yane kanta da wani mayafi wanda ya sakko kad'an ya rufe mata k'irjin ta amma duk da haka ana ganin tudunsu, wandon ma duk da burgujeje ne,amma bai hana bayyanuwar sharp dinta ba, masu gigita lafiyayyan namiji kai har wanda ma bai cika lafiya ba, in ya kalli duri da k'irar Balaraba sai yayi sha'awa, shima da sauri ya kauda kai, ya d'an sosa kansa kamar yadda ya saba, yace"Jimana "yan mata" Tsayawa tayi tana shan k'amshi, gefe guda kuma tana tunanin a ina tasan wannan muryar. Cikin Yanayin tafiyar shi ya karasa inda take tsaye tana masa wani kallo sama sa k'asa,tana tab'e baki, har ya k'araso ya tsaya dab da ita, tayi saurin matsawa baya, tace"Lafiya Malama"? Gyara murya yayi ya k'ara yin k'asa da ita yace"amm" ina neman maigidan nan ne wanda kika futo daga ciki" D'auke kai tayi ta d'an turo baki gaba, tace"bayanan" tana fad'a tayi gaba,tana d'aga kai sama, as,usul "Ok yanzu a ina zan same shi a kwai abunda ya kawo ni, gurin shi" yafad'a yana d'an daga muryar shi sabuda tayi masa nisa kad'an. Tsayawa tayi tace"in zaka iya tsayuwa nan ka tsaya ka jira shi,yanzu zai dawo tunda tara tayi"ta k'arasa maganar tana k'okarin tafiya a karo na biyu, da sauri yace"d'an tsaya mana, "yan mata ai ban gama tambayar ba" Wani irin kallo ta watsa masa,wanda yasa shi saurin dauke kai, "wai me zan maka ne, uhum? ka tambaye ni na baka amsa,sai me kaga ina da uziri ni,yi sauri kafad'i abunda zaka fad'a in wuce abuna" Ranshi ne ya b'aci sosai! jin yadda take masa tsawa sai kace wani sa'an ta, lallai yarinyar nan baza ta canza ba, kanshi ya sosa kad'an yace"naji kince tara na dare tayi, ke ina zaki a matsayinki na "ya mace me kamun kai, babban abun mamaki ma kin ci uwar kwaliyya gami da turare mai dad'i me zai hana ki tsaya ki tayani hira kafin Baban yazo" Wanini irin kallo take masa,wanda kana kallonsa kasan ta shirya wulak'anci, a ya tsine tace"baka da hurumi a kan abunda kake tambaya ta,haka kawai daka ganin sarkin fawa sai miya tayi zak'i, aikin banza kawai ni natsani munafurci wallahi, ka tambaya an baka amsa ka tsaya neman magana" Wani irin d'aci-d'aci ya fara ji a bakinshi,tsigar jikinshi ta fara tashi, tunda yake a rayuwar shi babu "ya macan da ta tab'a ci masa mutumci irin wannan sai wannan yarinyar, Daure zuciyar sa yayi kawai yana bin ta da kallo, tabbas ya gazgata abunda Salihu ya fad'a masa yanzu a kanta Tun daga Nesa Shamsiyya ta hango Balaraba da Sarki! a tsaye, tamkar zata tashi sama haka ta k'araso gurin zuciyat ta tana tafarfasa, tace" ke dabbar Araf! mayyar maza, wato ke duk inda ki kaga namiji sai kin nuna masa ke karuwa ce ko, to bari kiji wannan da kike gani yafi k'arfin wallahi sai dai ki gani ki kyale, domin shi dai ba d'an iska bane irin ki" Shamsiyya ta karashe maganar tamkat zata tsone mata ido Abun mamaki sai yaga kawai Balaraba ta girgiza kai zata wuce ba tare da tacewa Shamsiyya komai ba, a zuciyarsa yace"wato wannan yarinyar rashin kunyar ta da rashin mutuncin ta akan mu yake" kallasa Shamsiyya tayi tana wani fari da ido ta jawo mayafin da Balaraba ta nannad'e kanta dashi Balaraba tayi saurin dafewa sanadin haka har sai da wayarta ta fad'i k'asa had'e da pose d'ita sabuda in ta cika, Shamsiyya zata iya cirr mata kuma babu hula zai ga gashin ta, Shamsiyya tace"kaga wannan wallahi kar ka yadda da ita,sai ta lalata ka, dan muguwar makira ce ta iya kissa da kisisina duk da haka takewa maza irin ku masu kud'i" A dake! yace"to ke wanene yace miki ni mai k'udi ne, sakar mata mayafi ta tafi" yafad'a a cunkushe, dan yaji haushin abunda tayi Balaraba ko meye dalili oho Sakar mata mayafin tayi tace"gayyar tsiya gayyar datti da najasa sai an dawo" Wuce Balaraba tayi bata kallon gabanta, sabuda tsanani b'acin rai, karo sukaci da Sallau ya shigo lungun yana baza babbar riga sai kace wani limami ya kalleta, a banza ce yace"wallahi in baki dawo da wuri ba zaki zo ki tadda mun kulle k'ofarmu domin baza mu tsaya jiran ki ba" yana gama maganar sho ya shige bagaz-bagan, Duk wad'annan maganganun da Sallau yayi kamar a gaban Sarki! yayi su dan yaji komai, haka Shamsiyya. *Muje zuwa* *Comeent vote and Share* [19/07, 22:49] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^° _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®{REAL BINTU BATULA}👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{RAHAMA ALIYU}``` _ZAMANI WRITES_ _ASSOCIATION_🤝🏻 ```Bisimillahir-rahamanir-rashim``` *🅿54* Sai surutu Shamsiyya take masa, kanshi a k'asa sam baya k'aunar ya kalli fuskar ta, haka Sallau ya same su, jiki na rawa yace"barka da zuwa" D'ago kansa yayi a nutse ya kalli Sallau hannu ya mik'a masa yace"barka kadai Baba" Washe baki Sallau yayi yace"yan samari nayi mamaki jin cewar nayi bak'o,gashi bangane fuskar ka ba" Shamsiyya tana tsaye tana dariya tace"aikuwa nima nace bangane shi ba" Shiru yayi na minti biyu ya kalli Shamsiyya a ya mutse yace"d'an bamu guri, zamuyi magana ne" Yak'e tayi tana "yar dariya takama hanya zata huce Sallau yace" ai "yata ce in taji babu komai" bana buk'atar taji" yafad'a babu walawala a fuskar shi, wani kwarjini yayi wa Sallau sabuda haka sai ya kalli Shamsiyya yace ki shiga gida" Ko kunya babu ta shiga gida, sai ta mak'ale a soron gidan ta kasa kunne tana so taji, abunda ya kawo wannan guy addu'a take Allah yasa cewa zaiyi yana sonta, A nutse Sarki! yace"wani abokina ne yaga "yar gidan nan shine muke bukince a kanta, ance mana kaine mahaifinta" Washe hak'ura Sallau yayi yace"Eh duk "yayana ne, wacce kakw nufi a cikinsu"? " Balaraba" yafad'a kai tsaye Murtuke fuska Sallau yayi yace"wannan lalatacciyar yarinyar kake nufi, yanzu nan ta futa yawon bariki, ai inaji ma ka ganta wata gansamemiyar mara kunya" "Eh naga wata yarinya yanzu ta futa ko ita ce"? " Babu shakka itace, shawarar da zan baka shine kaje ka fad'awa abokinka ya janye maganar auran ta domin ba d'iyar arzik'i

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108