Skip to content

Chapter 61

Chapter 61

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,253 words 0 views Progress saved
Download Book

duniyar nan to da soyayyarta zan mutu, Sarki! na baka amanar Balaraba" Ya k'arashe maganar yana wata irin shak'uwa! Cikin tashin hankali da damuwa me Martaba ya bada Umarni a dauko mota domin a tafi asibiti,Moddibo najin abunda ake sama-sama girgiza kai kawai yake domin shi yasan halin da yake ciki,,hannun me Martaba yake taso ya kama,ganin haka yasa Sarki!kamo hannun me Martaba ya had'a dana Moddibo, me Martaba ya rik'e hannun sosai yana kalmatussha hada, nan take Moddibo ya fara fad'a shima. "La'ilahaillallahu Muhammadur rasulullahi,sallalahu alaihi wassalam" Da wannan kalmar Moddibo ya cika, dai-dai lokacin da ake k'wala kiran sallahr magariba. [07/08, 13:48] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ ________________________ _*We are here to educate,motivate and entertain aur readers*_ ________________________ _*DIDEGATED*_ _*TO*_ ```RAHAMA ALIYU``` _BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM_ *🅿69* Wata irin ajiyar zuciya Sarki! ya saki lokacin da ya ji jikin Moddibo ya shika a jikinsa, sai yayi zaman dirshan a gurin had'e da rungume gawar yana wani irin kukan zuci idanunsa sunyi jajawur!kalmar innalilahi wa'ina ilaihi raji'un kawai yake maimaita wa cikin zuciyarsa. Kafin kace kwabo mutuwar Moddibo ta watsu a cikin gidan,mutane kowa na futowa daga b'angaran sa cikin tashin hankali, lokacin da labarin ya iski Waziri bai yadda ba,sai da ya tura Khalifa domin yaje ya gani gaske ne,aikuwa Khalifa ya dawo cikin tashin hankali,ya tabbatarwa da Mahaifin nasu hakane. Waziri ya shiga cikin tsananin rud'u da tashin hankali,a gigice ya futo kafarsa babu takalmi ya nufi fada,zuciyarsa na yi masa sak'e-sak'en cewa Sarki Almustafah shine ya kashe masa d'ansa saboda wani dalili nasa. Lokacin da ya isa,gurin ana ta k'okarin cire gawar Moddibo daga jikin Sarki! Abun ya gagara domin ya rik'e shi tam! wasu hawaye na zubo masa masu tsananin rad'ad'i, cikin zuciyarsa yake cewa shikkenan na rasa d'an kuwa nagari shikkenan narasa amini me share min waye, me yasa mutuwa zata d'auki Moddibo ta barshi,shi a duniya shima tabbas bashi da wani amfani a cikinta. me Martaba ne yake ta rarrashin sa kan ya sake shi a d'auke shi daga gurin,gashi lokacin sallah yayi,amma tamkar da dutse yake magana,kwata-kwata Sarki! baya fahimtar abunda yake cewa. Waziri ne ya k'araso gurin idanunsa a kan gawar Moddibo,kurrr!! Yake kallonsa kamar wani zautacce yace"K'arya ne, babu wani munafurci da ban sani ba,a gidan nan duk wani abu a dake shirya min ni da "yayana nasan shi, saboda haka, ni sai nabi kadin jinin d'ana Yusuf Moddibo" Cikin mamaki jama'ar dake gurin suke kallon Waziri jin irin maganar da yake fad'a,maganar tasa tayi kama da ta masu tab'in hankali. Babu wanda ya saurare shi, a cikin su, suka cigaba da bin umarin me Martaba, da k'yar suka samu suka b'anb'are Moddibo daga jikin Sarki! suka nufi fada dashi, domin killace shi tunda dai dole yayi kwanan keso. Waziri ne ya bi bayan su yana gyara alkyabar dake jikinsa, yace"Ban yadda a aje min gawar d'ana anan ba, domin inaso in kaishi kabarinsa da duk sassan jikinsa gaba d'aya, idan aka aje min gawar d'ana a wannan fada ban yafe ba,domin wannan fada bata alkairi bace,bata tattare da komai sai shirka,da tsafi gami da shanye jinin mutane" Jin irin kalaman da Waziri yake fad'a ne yasa wad'anda suke d'auke da gawar Moddibo suka dakata, me Martaba kuwa cikin karfin hali yace"Kuje Ku cika umarnin da na Baku" Aikuwa sai suka shige ciki sosai suka aje Moddibo gefe, suka futo gami da tsayawa bakin Kofa,suna jiran Umarni na gaba, me Martaba ya kallesu a nutse yace"Ku tsaya nan gurin ban yadda kowa ya shiga inda yake ba,yanzu zan futo zan shiga sallah" Nan suka amsa suna godiya Me Martaba ya wuce Waziri a gurin yana zare ido. Waziri kuwa duk ya rasa abunda yake damunsa duk wannan maganganun da yayi, yayi ne kan ya b'ata wa me Martaba rai sai yaga ko a fuskarshi be nuna ba, ya fahimci yana cikin tashin hankali,kuma yasan bata komai bace face ta rasuwar gudan jininsa,. Shi yanzu sam bai damu da rasuwar Moddibo ba,burinsa kawai yaga ya rusa sarautar Sarki Almustafah,ya kafa tasa B'angaran sa ya koma fud'un-fud'un yana tafiya yana zancan zucci. Bayan idar da sallar ne limami ya sanar da rasuwar Moddibo ta lasifi k'a inda jama'ar gari suka ji suka shiga cikin tsananin d'imuwa da jin mutuwar bawan Allah Moddibo, mutumin da bai dauki kansa a komai ba, yana rayuwa dai-dai da kowa Moddibo in ka ganshi baza ka taba cewa yana da alak'a da sarauta ba. Hajiya Kattime tayi kuka tayi Ala wadai da turr! da halin mijinta,babu tamtama shine yasa zuciyar Moddibo ta buga ya mutu lokaci guda, duk da cewar ita musulmace muka ta yadda duk kanin me rai mamaci ne,mutuwar Moddibo tana alak'a da mahaifinsa Waziri,shine sila. Humm Rayuwa kenan, me Martaba ne da Sarki! suka wanke Moddibo tsaf suka suturtashi, suka kuma kwana dashi, har garin Allah ya waye. Mutane damk'am a harabar gidan sarautar suna jira a futo da gawar Moddibo domin su sallah ce shi, kowa da irin abunda alkairin da yake fada a kansa. Har waye war gari Waziri bai futo ba, kuma duk irin karatun da ake cikin gidan yana ji, domin malamai ne suka taro suna ta sauke wa Moddibo al'ikur ani. Me martaba ne ya bada Umarni a je a kira Waziri dole ya zo kan gawar danshi kafin a d'auke shi, sannan ya umarci Sarki! kan yaje ya futo da Balaraba, itama tazo kan gawar mijinta kafin a d'auke shi. Gabansa ne ya fad'i domin kwata-kwata ya manta da Balaraba, nan take ya shiga wani yanayi da ya tuno da nauyin ta da Moddibo ya dora masa kafin rasuwar sa. A nutse ya mike ya futa daga fadar, wani bawansa yana take masa baya, kai tsaye shashensa ya nufa. Balaraba kuwa tun lokacin da Moddibo ya kaisu daki ya ajesu, ta shiga cikin wani yanayi me wahalar fad'a motsi kad'an tayi zataji gabanta na faduwa,lokacin da Moddibo ya zo futa kiran sa tayi ta sanya kuka, tace"Yusuf a rayuwata bani da babban masoyi sama dakai da me Martaba, tabbas yanzu na kara tabbatar da soyyayar da kake min ta gaskiya, Yusuf na baka amanar kaina, saboda kazama jigo na rayuwa ta, ina rokan Allah ya amintar da ruhimu tare" Hawaye ya share mata,yana wani murmushi Wanda ya kara masa kyau,ya kama duk hannuwanta ya rik'e a nasa cikin taushin murya yace" Gimbiya baki da matsala dani insha Allahu karshen kukan ki ya k'are a duniya,fatana dake kawai ki rik'e amana ta,kuma ki tayani addu'a zanje in nemi yafiyar mahaifina, saboda na lura da halin da ya shiga lokacin daurin auran mu" Wani hawayen ya kuma zubo mata,ba tare data goge ba tace"Yusuf inajin wani abu a zuciyarta a game da wannan al'amari, don Allah ka nemi afuwa gurin Baba Waziri, kan dukkanin abunda yazo maka dashi" Damk'e hannunta yayi sosai cikin nasa, da murmushi a fuskarsa yace" Insha Allahu komai zai zo da sauki, yanzu abunda zakiyi shine, kici abunci ki bawa su Sadiya suci su kwanta, ke kuma sai kiyi alwala kiyi sallah raka'a biyu ta nafila domin ki nema mana zab'i na Allah, yanzu zanje in dawo muyi hira me

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108