Chapter 23
Chapter 23
sha shida, bakwai mata sauran duk maza ne, matanshi hudu ko wacce tana da " yaya dashi, Waziri mutum ne shi mai bala'in san mulki sosai domin ji yakeyi tamkar ya kwace sarautar daga hannun dan uwanshi,kullum burinshi da kokarinshi yaya za'ayi taga sarautar ta dawo hannunshi, shida iyalinshi,shiyasa da yaga Maimartaba bai haifi da namiji ba,sai hankalinshi ya kwanta, yana jiran ranar da Maimartaba zai kwanta dama,ya gaje sarautar tunda shine namiji,cikin hukunci ubangiji Allah ya azurta Maimartaba da haihuwar Sarki!Almansor, in da ya zamo daya daya kwal cikin "yaya mata goma sha bakwai shi ya zama cikin na sha takwas, lokacin waziri kusan zaunce wa yayi,ya dinga shige sa fuce gurin ganin ya ga bayan Sarki!Almansor, Allah bai bashi iko ba,dan duk wani kulunboto da yake shiryawa sai ya koma kanshi ko kan iyalinshi,duk rabi" yayanshi maza sun zama "yan shaye-shaye in ka cire, Yusuf(Maddibo) duk ciki shine nutsatstse a cikinsu,shiyasa suka fi shiri da Sarki!Almansor kusan a tare suka yi makaranta komai iri daya suke sawa, duk inda daya yake dayan ma ba gurin, halayyarsu ce kawai bata zo daya ba,inda Sarki Almansor ya kasance mugun muskili wanda magana take masa wahala,sai ya kwana ya yini bai kula kowa ba har in dai ba kamawa tayi ba,shi kuwa Maddibo mugun saukin kai ne dashi gami da wasa da dariya, in ka ganshi sam baza kace yana da alaka da gidan sarauta ba,sabuda da kowa mu'amala yakeyi,babba da yaro, Tsakaninsu basa boyewa juna sirri duk abunda ya dami daya daga cikinsu, tsakaninsu suke warware matsalar basa taba yadda maganar ta futa waje, shiyasa kai tsaye Maddibo shi ya fara kawowa maganar Balaraba, Kiranshi da suna Sarki! da mutane keyi na gida da jama'ar gari ya samo a sali ne daga gurin mahaifinshi,shine take kiranshi da sunan tun yana yaro in yaga yana wata irin tafiya cike da kasaita, ko cin abuncin sa abin kallo ne,balle yadda yake magana, Yadda Maimartaba ya fuskanta abin a jininsa yake, shi kanshi yaron ya san ya fishi kasaita, shine dalilin da yasa yake kiranshi da sunan, mutanan gida suka kama hade da jama'ar gari Halisa kuwa " yar kanwarsu ce wacce ta kasan ce autarsu wato Fulani Mariya maca ce mai mutukar kirki da sanin ya kamata sam bata kin talaka kullum cikin jawo jama'a take gidanta, tana can tana auran sarkin garin Wani gari jaja Amare, tun Halisa tana yarinya rikonta ya dawo hannun, me babban daki, wato Uwargidan Sarki, ta hada da "yayan ta ta rike kamar gaske, tun ta so warta take mutuwar son Sarki!Almansor, tun tanayi a boye har abu ya fito fili kowa ya fahimta,har maimartaba, nan kuwa Me babban daki ta tsaya kai da fata tace lallai dole ne a kulla wannan al'amarin domin dorewar zumunci, Maimarta ba ma ya nuna yaddarsa, a kan al'amarin, Shi kuma wanda ake domishi ya nuna bayaso da kyar dai mahaifiyarshi ta lallabashi ya dadda gudun bakin mutanan gari *Wannan shine kadan daga cikin tarihin abunda ya faru a baya* *Cigaban Labari* Da asubah Maddibo yasa drevar ya futa dashi suka shiga kasuwar sha tambaya,can gefan titi yasa drevar yayi parking din motar, yana kwance cikin motar yana kallon masu shigowa cikin kasuwar duk da cewa safiya ce, Wajan karfe takwas da rabi ya hangi Napep din Ashiru Balaraba na kokarin fitowa daga ciki yau tana cikin wata irin doguwar riga baka " yar saudia rigar taji adon duwatsu sosai da sosai tayi nan nade kanta da veil kafarta sanye da wani takalmi mai tsayi mai igiyoyi,sai ta kara tsayi sosai takalmin shima baki ne sosai kafarta tayi kyau a cikin talakmin hannuta rike da wayarta da wata "yar karamar pose ta tsaya suna magana da Ashiru Maddibo kuwa suma ne kawai bai yi ba lokacin da ya hangi fitowar ta sai ajiyar zuciya yake saukewa, yana wa Allah tasbihi cikin zuciyarsa yace" tabbas Allah ya aje baiwarsa gaskiya yarinyar ta hadu sosai, dole maza su rika rikice wa a kanta, in da take burgeshi , kamun kai da rashin kwadayi gami da dogaro da kai shiyasa duk abunda a ka fada masa a kan ta yake kauda kai,sabuda yana ganin babu mahalukin da ya isa ya hanashi auranta, Ya na can yana tunani Ashiru yaja Napep dinshi ya na kokarin hawa titi,can ya hangoshi, da sauri ya bawa drevar Umarnin bin bayanshi duk in da ya nufa. *Muje zuwa* [30/06, 04:10] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ» ββββββ _*GIMBIYA BALARABA*_ ββββββ πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ» _*Na*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` Zamani Writes Associationπ€π» ```Bisimillahir rahamanir rahim``` *π Ώ34* Sosai Ashiru yake gudu a kan kwalta,kasancewar babu cinkoso sosai na ababan hawa, sauri yake shima ya isa gurin aikinsu, kawai sai yaga katuwar mota ta tari gabanshi, sai ya rage gudu, ya fara tafiya a hankali gabanshi yana faduwa! Cikin sauri drevar dake jan Maddibo ya yi parking din motar gefan titi ya fito,yana dagawa Ashiru hannu. Ashiru ya tsayar da Napep dinshi ya fito daga ciki duk hankalinshi a tashe,ganin mutum sanye da wasu manyan kaya ja da baki kanshi nade da wani katon abu,yana gani ya fahimci daga gidan sarauta ne, Hannu ya bashi suka gaisa yace"Yallabai ne yake son yin magana da kai" Jiki na rawa Ashiru ya bi bayan dravar suka karasa inda yayi parking din motar, Maddibo ya mika masa hannu fuskarsa a sake yace"barka da asubah" Cikin dari-dari Ashiru ya mika masa hannu sukayi musabaha da juna,kana yace"barka dai yallabai,fatan katashi lafiya" "Lafiya kalau Abokina" Maddibo yafada fuskarshi dauke da murmushi ya cigaba da cewa"in baza ka damu ba inaso in nemi alfarma a gurinka" Jiki na kyarma Ashiru yace"babu damuwa Yallabai" "Masha Allah, Menene alakar ka da Balaraba"? Cikin rawar baki yace" babu wata alaka a tsakaninmu kawai ina kaita bakin kasuwa kullum" "Ok shiga muje ka nuna min gidan su" Maddibo yafada babu wata damuwa a tare dashi. Ashiru duk ya rude yace"Yallabai Allah dai yasa ba wani abun tayi muku ba,sabuda na fahimci bata kaunar Sarki!Almansor, in wani abu tayi muku, ku gafarce ta dan Allah, Balaraba marainiya ce bata da uwa babu uba,kusan itace take daukar nauyin gidansu" Ajiyar zuciya Maddibo ya sauke, wani irin tausayin Balaraba yana ratsa zuciyarsa. Yace"Babu laifin da tayi mana, alkairi ne zai kai ni gidansu,ka kwantar da hankalin ka" Da kyar Ashiru ya je ya gyara parking a gefan titi kana ya sanya key ya kulle Napep din nasa, ya shiga motar suka kama hanya har unguwarsu Balaraba. Sosai Maddibo yayi mamakin irin unguwar da Balaraban shi take rayuwa, wani irin lukuna masu dauke da dagwalan katoci ku ina kwata tabi hanya abun babu kyawun gani, hankalinshi bai kara tashi ba ma sai da yaga lokwan su Balaraba,mai tattare da tarkacan, kayan gwan-gwan ko ina gasu nan wasu a daure a buhun-huna wasu kuma a washe a hanya, in ban da wari babu abunda yake tashi a gurin, Kasa shiga ciki yayi sosai ya tsaya daga baya, Ashiru yace"Yallabai ga gidan can, in da waccan budurwar take soya a wara to nan ne gidansu" Yara ne suka fara taruwa a gurin suna kallon Maddibo,wasu na rugawa gida da gudu suna fada cewa ga Sarki yazo, ai tuni Yara suka cika gurin,kasancewar Safiya ce wasu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108