Chapter 59
Chapter 59
Yace"Magajin Sarki ya labarin bunkicen da nasa kayi min kan wannan yarinyar dake zaune kusa da kai" Cikin yanayin maganar sa ya ce"Allah ya baka nasara, a gafarce ni, nayi laifi saboda banzo na fad'a maka komai ba yau tsawon kwana biyu kenan, dama yau nakeso inzo in fad'a maka sai ga shi ka aiko,tuba nake ranka ya dad'e" Galadima yace"me Martaba ya karb'i uzirin ka" Moddibo ne ya kalleshi yana masa magiya da ido,dama kafin su futo sai da ya dunga lallab'ashi Sarki! yayi gyaran murya a nutse yace"Allah ya taimake ka nayi bunkice sosai nagano wannan yarinyar bata da wani aibu yarinya ce me ladabi da biyayya da bin nagaba da ita,nayi bunkice sosai duk wani sharace-sharace da ake mata basu da tushe,anayi ne domin ganin tana futa kullum gurin sana'arta,wannan shine abunda na sani a game da ita, Ya karasa maganar cikin nutsuwa. Shiru na minti biyu me Martaba yayi gyaran murya hankali kwance yace" Nayi farin cikin jin wannan abu, wannan yarinyar tun kafin in ganta hankali na ya kwanta da ita,in sha Allahu tana tare damu ita da "yan uwanta, ni ne zan shige mata gaba,kan lamarinta, a yanzu yanzu zan d'aura mata aure da Yusuf Moddibo, saboda na yaba da nagartarsa gami da jajircewar sa kan lamarin ta, wannan shine hukuncin da na yanke" "Alhamdulilahi-Alhamdulilahi, Abunda Moddibo yake ta fad'a kenan cikin zuciyarsa, Balaraba ma taji dad'in yadda abubuwa suka zo da sauk'i haka, duk wanda yake zaune a fadar yayi murna da wannan abu,in ka cire mutum biyu wato Sallau da Waziri Zayyanu, Nan me Martaba ya umarci maga takarda da ya futa ya sanar a cikin gida,sannan ya tawo da goro da Alawa domin, cika al'k'awarin da ya d'auka. Shiru fada tayi bayan futar maga takarda,kowa da abunda yake sak'awa cikin zuciyarsa,kawai sai sukaji muryar Waziri Zayyanu cikin fushi!yace" wannan hukunci da me Martaba ya yanke bai yi ba, domin ni ne nake da hakki a kan yaronan don haka ban amunce ya auri wannan yarinyar ba,in ko ya aureta zai had'u sa fushina! *Tofaaaaaa!* *Fans kuna ina ne wa ya dace Balaraba ta aura, shin me zai biyo baya in me Martaba ya d'aura auran Moddibo da Balaraba, shin wane irin rikici ne zai faru kan hakan, yaya su Lantana zasuji jin cewar Balaraba tayi aure gidan sarauta, shine wanene mijin Balaraba???* *SARKI! NE KO MODDIBO?* [05/08, 00:16] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ ________________________ _*We are here to educate,motivate and entertain aur readers*_ ________________________ _*DIDEGATED*_ _*TO*_ ```RAHAMA ALIYU``` _BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM_ *🅿67* Shiru fada tayi ana kallon kallo abunda Waziri ya fad'a ya girgiza jama'ar dake gurin. me Martaba bai tab'a yanke hukunci ba, a samu wani wanda zai ce be yi dai-dai ba, kowa yana jiran yaji abunda me Martaba zai ce, shiru yayi kawai yana jin damuwa da b'acin rai a zuciyarsa yau Waziri ya nuna masa cewar d'anshi Moddibo bashi da iko a kansa aure tunda ya riga ya yi niyyar d'aura shi a yanzu sai ya d'aura shi, saboda haka duk abunda Waziri yaga zaiyi yayi, yanzu yana sauraron dawowar maga takarda ne. Mik'ewa Waziri yayi ya futa, ba tare da ya yiwa kowa sallama ba, me Martaba yaji ciwon abunda d'an uwansa yayi masa,amma sai yayi shiru kawai. Mintuna goma da futar Waziri sai ga maga takarda nan ya dawo, yana tare da wani bawa a bayan shi, yana d'auke da d'aurin goro da kwalin alawa, Galadima ne ya matso ya kwance d'aurin goron da alawa, kansa a kasa yace"Allah ya taimake ka, Waziri tuba yake yayi abisa kuskure a gafarce shi" Murmushi kawai me Martaba yayi ya kalli Sarki! dake zaune kanshi a k'asa yana jini b'acin rain abunda Waziri yayi wa mahaifin sa. Kafin me Martaba yace wani abu Sarki! Ya fahimci abunda yake nufi, kamar ya sani kawai ya zura hannu cikin rigarsa ta ciki ya futo da kud'i zasu kai duba talatin ko sama da haka, mik'ewa Moddibo yayi ya rik'e a hannusa, kasa-kasa yace"ka rik'e a hannuka ana d'aurawa sai ka bata sadakin ta" Moddibo ya k'arba fuskar sa d'auke da murmushi kana ganinsa kasan na farin ciki ne. Kafin kace kwabo fada ta cika da mutane, nan me Martaba ya Umarci babban limami a fara d'aura aure. Alhamdulilahi-Alhamdulilahi an d'aura auran Moddibo da Balaraba kan sadaki dubu arb'ain da biyu, nan maga takarda ya fara rabon alawa da goro me Martaba ya Umarci Moddibo ya d'auke Balaraba su futa, haka kuwa a kayi, suka futa,suka bar Sarki! suna ta gaishe-gaishe da mutane Jiki a sanyaye Balaraba ta dunga tafiya har suka isa shashen Sarki! gabanta sai fad'uwa yake tana jin kamar a kwai wani abu da zai faru. Can fada kuwa komai yana tafiya dai-dai kana kallon Sallau kasan yana cikin wani mugun hali na d'imuwa yayi yunk'urin mik'ewa ya kasa saboda yadda yake jin jikinsa na rawa ji yake kamar kafarsa ba a jikin jikinsa take ba, nan me Martaba ya sallami kowa, mutanan da suka rage a ciki sune makusantan sa, sai Sallau da me gari Halilu da Walidi, kyautar ban girma me Martaba yayi wa Walidi, wanda tasa shi kusan sumewa a gurin ya dunga godiya, me Martaba yaja kunnen Sallau sosai, da sosai, sannan ya gargad'i me gari Halilu kan kar ya kuma aikata abu maka mancin haka, me gari Halilu ya bada hakuri kuma ya nemi afuwa, shi ko Sallau bud'ar bakinsa,sai yace"ranka ya dad'e maganar sauran yaran wato Sadiya da Usuman ina so abani su mu koma gida" Sarki!! Ya d'ago da kansa cikin fushi! yace"Sadiya da Usuman zasu zauna gurin "yar uwarsu,kai ka tafi ka kad'ai" Wani bafade ya kalli Sallau da jajayen idonsa yace"gyara kintsi dai!!! kayi na d'aya kayi na biyu kar ka sake kayi na uku,anan zan tub'e ka in zane maka jiki,ko zaka nunawa me Martaba abunda ya dace ne." Girgiza kai Sallau yayi jikinsa na kyarma! cikin tsawa wannan bafade yace"ka nemi afuwar gurin me Martaba" Jiki na rawa Sallau yace"Allah shi gafarta maka ina neman afuwa" Saura kad'an Walidi ya saki dariya saboda yadda ya ga jikin mahaifin nasa yana rawa, murmushi me Martaba yayi yace"Allah yayi mana afuwa baki d'aya, wato malam Sallau maganar wad'annan yaran naka Sadiya da Usuman kayi hakuri kabar su gurin "yar uwarsu kaji ko, duk lokacin da kukayi sha'awar ganinsu za'a kawo muku su har gida,idan kuna sha'awar zuwa gurin su k'ofa a bud'e take muna maraba da ku baki d'aya" me gari Halilu yace"godiya yake ranka ya dad'e" Ganin babu yadda zai yi ne yasa ya fara yak'en dole yana godiya ga me Martaba, amma in zaka tona zuciyarsa a lokacin tafi garwashi zafi da turiri. Nan me Martaba ya bada Umarni a kaisu gida tare da kayayyakin abinci buhu-buhu mota guda a ka had'a musu na kayan masa rufi,Walidi kuwa in ya tuno da kyautarsa da akayi masa sai yaji kamar babu wanda ya fishi sa'a a rayuwa,gobe i yanzu yana cikin kasuwar sha tambaya yafara gudanar da kasuwancin sa. Cikin tsananin b'acin rai! Waziri Zayyanu ya shiga b'angaran sa,sai a kayi sa'a duk "yayan shi maza na zaune a falo suna
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108