Chapter 85
Chapter 85
ina ta sauri inzo in nuna maka adona ashe ban sani ba "yar uwata ta rigani,fatan dai ta kula da kai yarda kake buk'ata idan kana bukatar wani Abu ta b'angare na ka fad'a yanzu in tashi in aiwatar maka dashi,domin duk mu du muna karkashin ka ne" Lumshe idonsa yayi ya bud'e a hankali har yanzu yana tunano abunda ya faru shi da Balaraba na d'azu, a hankali ya bud'e baki yace"Itama bani na kirata ba, Balle kiyi min wata fassara,maganar bukatar abu ta b'angaran ki, sai ki Bari sai da daddare kizo ina neman ki" Shahid dai da Shatima mik'ewa sukai suka nufi gurin cin abunci suka bar Shi da Azima. Wani k'asaitaccan murmushi tayi tace"Godiya nake ranka ya dad'e ai dole in amsa kiranka,da kamar k'arfe nawa zanzo"? Ta k'arasa maganar tana karkad'a idanuwan ta. Abunda takeyi ya bashi dariya sosai, dakewa yayi fuskarsa babu yabo babu fallasa yace" Kizo ko da wane lokaci" Azima taji dadin wannan abu tana ganin idan Sarki! Ya d'and'ana zumarta a farko, dole ya susuce domin ba k'aramin gyara tayiwa kanta ba, Mik'ewa yayi ya nufi gurin cin abunci, itama ta mike ta bishi a baya,, k'are masa kallo take a zuciyarta tana cewa Allah yayi hallita anan gurin,,, gaskiya yanzu sonshi da kaunarshi tsakani da Allah take, Sam baza ta yadda da auran sharad'i ba, yanzu ta gane dalilin da yasa Mahaifinta da Waziri suke son auranta dashi,saboda wata manufa tasu. *********** ************ *********** Lokacin da sak'o Mama ya isa gurin su Uwa! da Sallau cewar ga direba nan na jiransu su shirya "yan uwa da abokan arzki kai da duk me ra'ayin zuwa gidan sarauta ya shirya ga mota tazo daukarsu har gida, domin. Suje su kalli shagalin bukin Sarki! Tare da matayen sa uku. Kafin kace kwabo unguwa ta hautsine kowa na shiri babu Wanda yake so a barshi a baya,wad'anda basu sani ba, sukaita mamaki jin cewar Balaraba d'iyar Ayuba ita tw auri Sarki! Almansur,, lallai kowa ne dan Adam da lokacinsa. Uwa! Kuwa kuka wiwi! Ta dunga yi mutan unguwa sun cika gidan suna kallonta wasu na bata baki wasu kuwa mamaki sukeyi kukan me takeyi wasu daga cikinsu kuwa dariya suke mata sun San bakin ciki ne yake d'akinta,Sadiya matar Kawu farin ciki ya cika mata zuciya tabbas yau Allah ya nunawa Uwa! Ita ba komai bace a rayuwa , yarinyar da take rainawa ta hau wani matsayin da babu Wanda ya isa ya kaita kansa sai Ubangiji makagin baiwa. Cikin farin ciki ta kulle d'akinta ta tsallake Uwa! Dake durkushe a tsakar gida tana gunjin kuka mutane sunyi dafifi a kanta suna bata hakuri, a zuciyarta tace" Kune wahallalu munafukai kawai, d'akin Iya ta nufa. Tare suka futo da Iya sukayi fucewarsu, suka bi a yari zuwa gidan Sarki! Duk wannan wainar da ake toyawa Shamsiyya da Maburuka basa gida. Shamsiyya dai, gurin Arrama ta tafi, ita kuwa Mabaruka wani sabon saurayin ta ne yazo ya d'auke ta a mota suka futa. 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*GIMBIYA BALARABA*_ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* ```MARUBUCIYAR``` *NANA KHADIJA* *YARO DA KUD'I* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* _*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_ _________________________ ```We are here to educate, motivate and entertain aur Reades``` _________________________ _*DEDIGATED*_ _*TO*_ _RAHAMA ALIYU_ _*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR RAHIM*_ *🅿97* Buki aka gudanar irin na al'adar masarautar ,matasan samari suka shirya kilisa, duk suka shirya dokunan su da ado me k'ayatarwa suka futa, yayin da masu busa da k'ida irin na gidan sarauta suka rufa musu baya suna aikin su. A gaskiya shagalin buki ya k'ayatar ya kuma ni shad'antar, jama'ar unguwar su Balaraba, kafun su tafi sai da suka sa a kai musu iso gurin ta, suka gaisa sosai sunai mata fatan alkairi, Iya ta bata shawarwari sosai, Sadiya matar Kawu ta kalli Lantana wacce tayi kicin-kicin da fuskar ta, so take kawai su tafi gida, domin ita gani take kamar zasu ce zasu zauna kamar yanda tayi. Tace"Lantana ai sai ki taso mu tafi haka tunda dai an gama shagalin buki ko" Wata k'atuwar harara ta Dan k'ara mata tace"Ai sai kizo ki ja ni ki kai ni gida munafuka, ai ni naga gurin zama, kuje Ku k'arata da iskancin ku" Cikin mamaki Sadiya tace"Lantana daga magana kuma sai ki fad'a min me zafi"? "Ke kika jawo ehe! masu gidan ma basu gaji dani ba balle ke karan k'ada miya" Girgiza kai tayi cike da mamaki tace"Ai gaskiya ce,Lantana ke da ya kamata kiyi wa wani fada kece kike aikatawa" "To bana son gaskiyar, nace bana son gaskiyar, gaskiya ko munafurci dai" Ta k'arashe maganar a fusace! Iya ta kama hannun Sadiya suka wuce, tana fad'in "Ke ma dai kin tsaya Ki na daka ta Lantana kamar bakinsan halinta ba, yanzu sai tasa mu raba abun kunya ba damuwarta bane" Akwai In da Mama Fulani take suka nufa, sukayi mata sallama gami da godiyar abun alkairin da a kai musu,, har wajan mota Balaraba ta rako su tare dasu Sadiya suna ji kamar su bisu gida, Balaraba ma idanunta duk ya tara kwalla haka dai sukayi sallama suka tafi, kamar yarda aka d'auko su a mota haka aka mai dasu gidajan su, kowan ne kana kallonsa kasan yana cike da farin ciki. Bayan sallah isha ne, masu karatun al'kur'ani suka zauna farfajiyar gidan suka fara karatunsu, saukar alkur'ani me girma zasu yi. ********* ********* ********* Arrama yana ganin Shamsiyya afujajan, yasan da akwai matsala, tana zama ta fashe masa da kuka wiwi! Murmushi yayi yana mata wani irin kallo yace"Da kwai matsala kenan malama Shamsiyya" D'aga kai tayi domin kuka yaci k'arfin ta kasa maganar. "Shiga ciki ganinan zuwa" Ya fad'a mata yayin da ya ke zane-zane cikin yashin dake gabansa. Wuff Shamsiyya ta shige d'an a kurkin d'akin tana goge hawayen ta domin ita gani take tazo inda za'a share mata hawaye. Arrama dama kwana biyu babu kasuwa mutane duk sun gudu domin ganin aikinsa baya ci, a cewar su mak'aryaci ne, kullum sai yace buk'ata zata biya tak'i biya shiyasa kowa ya gudu, sai d'ai-d'ai ku ne wanda basu gane ba. Mik'ewa yayi yaje ya zura sakata, ya k'wab'e babbar rigarshi ya aje ta gefe guda, ya afka d'akin. Shamsiyya tace"Arrama yanzu meye abun yi" Zama yayi kan wani dutse yana lashe baki yace" Aikin ki ya dawo sabo yarinya kin yi kuskure shiyasa komai yak'i tafiya dai-dai" Shamsiyya ta dafa k'irjinta cikin damuwa tace"Na shiga uku ni Shamsiyya yanzu babu yadda za'ayi a gyara" Arrama yayi wani bazawarin murmushi yace"Akwai hanyoyin gyarawa in har zaki bi umarni" Shamsiyya tace"Zan bi umarni in Allah ya yarda ni dai burina shine kayi min aikin da zan auri Sarki! Ita kuma waccan tsinanniyar ya koro ta gida tare da takardar saki" Murmushi yayi, ya mike yana fad'in "Ina zuwa" Futa yayi daga d'akin Allo ya d'auka yayi zane-zane layi goma ya sanya ruwa cikin k'ok'o ya d'auraye Tass, ya zuba wasu ciyayi, ya shiga d'akin yana motsawa ruwan. Zama yayi inda ya tashi, yace"Karb'i wannan" Shamsiyya ta mik'o hannu ta karb'a jiki na kyarma! Tana jiran abunda zai ce, gyaran murya yayi ya cigaba da cewa"Ki tub'e kayan jikin ki tass! Ki shafe jikin ki da rubutun yanzu kiyi a gabana ko ina ake so rubutun ya tab'a a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108