Skip to content

Chapter 34

Chapter 34

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,255 words 0 views Progress saved
Download Book

karyar zakiyi min kenan, in da gaske kike ki matsa in shiga cikin dakin naki in duba kaji ni da ja'irar yarinya ko" Ya karashe maganar yana gyara babbar rigar shi "Haba Baba, wannan ba yi bane, kai yanzu a kace ka shiga dakin sai ka shiga,gaskiya kai Lusari ne wallahi" Hahahahaha Walidi ya karashe maganar yana kyalkyala dariya, ya zira hannu cikin aljihun wandon dake jikinshi wanda yayi dau'da sosai duk jirwaye, gudar dubu daya ya futo da ita ya mika masa yana cigaba da dariya kamar wani mahaukaci, ganin Walidi ya futo da Dubu daya sabuwa dal! ya bawa Sallau yasa jikin Lantana kyarma, washe baki tayi ta matso kusa da Walidi, tace"Ashe da gaske ka keyi yaron nan, ai nace dama jarina yayi kasa, kaga yau sai in shiga kasuwa in siyo kuli-kuli, Allah dai yayi maka albarka d'an nan Walidi yasa dariya yana nuna Lantana da hannunshi yace"ke dai Lantana in kika ga kudi duk sai ki shiririce, dube ki don Allah" yafada yana dariya, ya cigaba da cewa"wannan kudin sun futo daga gurin mijin Balaraba insha'Allah in kin kwantar da kai,kullum zan dinga baki dari biyu, yanzu dai ga dubu daya ke ma sai kira jari kamar yadda kika fada, Warce wa tayi daga hannusa, tana washe baki tace"da gaske kake dan nan"? "Da gaske nake mana,ke dai ki dai na takurawa Balaraba a gidan nan" "Yo ni dama ai bana takura mata,sai kaje ka nemi masu takura mata, to kaj! in kaji ina mata fada to fadan gaskiya ne, ko ba haka bane Balaraba" tafada tana kallonta Girgiza kai kawai Balaraba tayi tana kokarin komawa daki Jin hayaniya tayi yawa a tsakar gida yasa Uwa! futowa daga dakinta, yau ta makara bata tashi da wuri ba dalili jiya sun dade ita dasu Shamsiyya,da Maburuka suna lissafin kudi, har Sallau ya dawo daga mahadarsu ya taddasu suna lissafi,yayi-yayi su bashi dari biyu Uwa! ta hana shi "yayan nashi kuwa sai dariya suke masa, Shamsiyya ce me cewa" Baba zuciyar ka ta mutu, wallahi Allah ya wadaran Halinka" nan ya mike ya barsu ya shige daki yana ta zaginsu,su kuma sai dariya suke masa. Ganin kudi tayi hannun mijinta cikin mamaki, ta bi bayanshi ganin yana kokarin futa daga gidan, yasa ta kwala masa kira"Sallau" Da sauri ya juyo yana hararar ta, ta karaso gurin kanta babu dankwali daga ita sai daurin kirji tace"me nake gani a hannun ka kamar gudar dubu daya" Da sauri ya zira ta a aljuhu yace"Kwarai kuwa menene"? "Kamar yaya menene, a gidan ubanwa ka samu kudi,haka kuma kake kokarin futa batare da ka bamu kudin karin kummalo ba,tunda Allah yasa ka samu" Banza yayi mata kawai ya kama hanya zai futa a karo na biyu, da sauri ta je ta tari gabanshi, tana hura hanci tace"karya kake wallahi, ka bani ko yanzu in tara maka mutane,domin na gaji da muguntar ka, wato sai da kasamu kudin kaje kaci banza kaci wofi,to baza ta sabuba,wai bunda a ruwa" Tafada tana dukan cinyar ta Sanin halin jarabar Uwa!yasa Sallau kallo inda Walidi yake tsaye yace"Zo kara bani da wannan mutsiyaciyar Uwar taka, mayyar kudi" Dariya Walidi yake sosai ya karaso gurin yana wata irin tafiya yace"ai duk halinku daya da ita Baba, dubu daya ya ciro ya mika mata yace"kema gashinan kici albarkacin Balaraba" Da sauri Uwa ta karbi kudin daga hannun Walidi tace"karya kake inci albarkacin wata banza yarinya, wallahi" "Ke dai kika sani, zaki iya yaga kudin yanzu, ai tunda kince karya ne" Tafiyar ta tayi tana surutai gami da fadar bakaken magan-ganu ga Balaraba, Sallau ma fucewa yayi ya bar gidan, Lokacin Balaraba ta samu ta futo ta shiga bandaki, domin tayi wanka ganin rana tafara yi, jan ruwa take a rijiya, Maburuka ta futo hannuta rike da bokiti, da kutto wande ke dauke da sabulu da soso, daga ita sai daurin kirji,wani irin kallo ta watsawa Balaraba, taja tsaki, yaje ta dangwarar da bokitin saura kadan ya fada kafar Balaraba, tayi saurin kaucewa, kawai bata saurare ta ba, ta dauki ruwan da taja cikin wani bokiti irin na roba ta shiga bandaki, nan ta jiyo Mabaruka na cewa, banza kawai, kina dauke da najasa kina shigarwa mutane,ban daki dole ne ma in kin futo in wanke bandakin domin bazan je in kwashi cuta ba" Ranta ya ba'ci sosai jin abunda Marubuka take cewa a kanta, sauri-sauri take ta futo daga bandakin taci Uwarta, ta lura idan bata, tasar musu tsaye ba,zasu hanata shan ruwa a gidan, Mabaruka na zaune a kan rijiya tana wake-wake cikin rashin kamun kai, Balaraba ta futo daga bandakin, tayi kamar zata wuce, sai tai sauri ta dawo da baya,ta damki! wuyan Maburuka ta rike tamau, ta jawota sosai suka matsa daga jikin rijiyar, had'a ta da bango tayi ta makure ta sosai tace"wa kike zagi ne, mara kunya" Kakari! Mabaruka take sosai tana son tayi magana takasa, idanunta sunyi jajazir, Wani wawan mari Balaraba ta tsinka mata,wanda yasa jinta da ganin ta suka dauke na wucin gadi, tace"Ke baki kira kanki da najasa ba, zaki kira wani, bari kiji dan uwarki, duk irin iskancin da kikeyi a unguwar nan nasani, shegiya me bakin uwa, duk sharrin ku sai ya koma kanku,ni nafi karfin ku wallahi" Hawaye ne, kawai yake zuba a idanun Mabaruka, jikinta sai kyarma! yake yau ta tsorata da Balaraba sosai,ashe haka take da karfi,sai kace me aljanu, Cikin ikon Allah har yanzu babu wanda ya futo daga daki cikin mutan gida, Kasa da muryar ta tayi tace"bani hakuri dan Uwarki ko in cire miki makogwaro yanzu-yanzu Bakinta na rawa tace"Allah ya baki hakuri" Sakinta tayi tana hararar ta tace"karyar rashin kunya kike yi yarinya,wallahi kika duk ranar da kika kara zagina sai naci miki uwa"! Shiru Mabaruka tayi tana kallonta Har ta shige dakinta, Cikin sauri-sauri take shiryawa ta tashi su Sadiya da Shamsu ta shiryasu cikin uniporm kamar kullum, ruwan tea ta dafa musu,dake tanada kayan shayi a dakinta nan ta hada musu suka karya,suka futo a tare,a gurguje ta leka dakin Iya suka gaisa, tace"yau baki futo ba" "Wallahi na tashi da zazzabi ne, tun dazu nake jin hayaniya a gidan, lafiya in ce ko"? "Lafiya kalau" Balaraba tafada ta cigaba da cewa" amma kin sha magani ko"? "Ai cikin dare zazzabin ya rufe ni" Iya tafada tana kara rufe jikinta, "Insha Allahu zandawo da wuri sai muje chamis a duba ki" "To sai kin dawo,kinji Allah yayi miki albarka" "Ameen Iya nagode, in su Sadiya sundawo su zauna a gurin ki tunda babu isilamiyya yau" "To shikkenan sai kin dawo" Balaraba na futa taci karo da Walidi shida abokansa, da sauri ya taso ya zo ya karbi jakar hannunta, sai washe baki yakeyi, suka jera,har inda me Napep dinta yake, tsayuwa in yazo daukar ta Tunda ta futo matasan dake unguwar suke kallonta wasu su fadi alkairi,wasu su fadi sharri a kanta, babu abunda ya dame ta, ta shiga Napep, Walidi ya mika mata jakar ta, yana mata adawo lafiya Suna futa daga unguwar ta kunna wayarta, ko minti biyu ba ai ba kira ya shigo, sai da ta kusa katsewa sannan ta daga, Ajiyar zuciya ya sauke, muryar shi kasa-kasa yace"Allah ya taimaki Gimbiya ta" Shiru

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108