Chapter 68
Chapter 68
kamar ta dena aiki,sai haki!tsabar d'imuwa da tashin hankali sunyi masa katutu a k'ahon zuciya. Duk suna zazzaune a tsakar gida suna jiran shigowar Sallau hankalinsu duk a tashe, kowa da abunda yake fad'a, akan Balaraba wai ita ta kai kararsa gurin Sarki! A rirrik'e a ka shigo dashi Lantana ta tashi tana sallalami gami da salati dad'i take shikkenan,wannan "ya tasa anyi masa wannan bulala ta gidan sarki!Allah ya tsine miki Balaraba" Ihu!Su Shamsiyya suke sukayi kan ubansu suka kakkamashi suka shiga d'aki dashi suna duba jikinsa sukaga babu wani k'warzane ko d'aya babu alamun duka a jikinsa. Uwa!tace"Wai meye kake haka sai kace Wanda zai tada aljanu,tun safe munanan muna fargaba,gaka ka dawo kuma me makon kayi mana bayani kuma kazo kana wani nishi!sai kace kuturo" Lantana tace"Ke rufe min baki shashasha kawai,bakya ganin halin da yake ciki,Allah yasa dai ba guba suka bashi yasha ko ya Ciba" Walidi dake tsaye bakin k'ofa yasa dariya yana nuna Lantana da hannu yace"Babu wata guba da yaci,guba d'aya itace bak'ar zuciyarsa ya kusa had'iyewa saboda tsabar bakin ciki, Hahahahahaha" Walidi ya shek'e da dariya babu abunda ya dame shi. _*TSANTSAR BUTULCI*_ *_NA_* _BINTA UMAR ABBALE_ *BINTUBATULA*π _littafin me cike da sark'akiya gami da cin amana, kar Ku bari a baku labarin_ https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ» γγγγγγγγγγγγγγγ _*GIMBIYA BALARABA*_ πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ» _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *BINTUBATULAπ* _MARUBUCIAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* _*Zamani writers Association*_ ________________________ *We are her to educate motivate and entertain aur Reades* _________________________ *DIDEGATED* *to* RAHAMA ALIYU BISIMILLAHIR_RAHAMANIR RAHIM *π Ώ78* Wata k'atuwar harara Lantana ta makawa Walidi bakinta na kumfa tace" Walidi kayi asara wallahi ban san inda kaje ka samo wannan b'akar zuciyar taka ba, yanzu ubanka na halin rai da rayuwa shine kake masa dariya" ta karashe maganar tata tana rik'e hab'a cikin mamaki! Wata mahaukaciyar dariyar Walidi ya kara saki yace" Kaji Lantana da wani magana kuma, hahahahaha, ai bak'ar zuciyarki na gado, amma naji kina zancan ina na gado bakar zuciya, to ai kece kika gada mana ita, hahaha" Ya k'arashe maganar da mahauaciyar dariyarsa, barin gurin yayi yana fad'in ni kam nayi nawa guri domin yau ina cikin farin ciki da annushwa sanadin Balaraba yau na "yantu na zama cikkaken mutum ehe duk d'an bak'in ciki sai dai ya mutu! fucewarsa yayi ya barsu da baki a sake Sallau kuwa tuni ya sharb'e a gurin bakinsa ya karkace miyau na dulala, da kyar ya d'aga hannusa guda yana kiran Lantana ta matsa kusa dashi tana salati, baki a mugud'e yace" Lantana muna cikin wani yanayi wannan yarinya da mukai wa rikon sakainar kashi, Allah ya rufa mata asiri tana gidan sarki za'a d'aura mata aure da d'an wazirin gar..... kafin y k'arasa maganarsa Lantana ta fahimci abunda yake nufi, wani uban ashar! ta kurma tamkar ba tsohuwa ba fad'i take, "Me nake shirin ji ni Lantana, Balaraba d'iyar Tanko itace zatayi aure gidan sarauta ni nawa jikokin na nan a zaune lallai da sake! tafad'a wata irin kumfa na futa daga bakinta tsabar tashin hankalin da take ciki sam yanzu rashin lafiyar Sallau din bata gabanba, tunanin ta ya koma gurin ganin yaya zatayi ta futo da Balaraba daga wannan gida ko ta halin k'aka ne. Shamsiyya ce ta futo daga uwar dakinsu daga ita sai daurin kirji nonuwanta sun cika sun tun batsa sai kace wata matar gida goshinta sai kyalli yake. Lantana ta dube ta sama da kasa tace"Dube ki cikkakiyar mace wacce ta amsa sunanta na mace kina zaune a gida kina tsotsor tsamiyya waccan mutsiyciyar yarinyar ta shallake ki, ai ko ta halin k'aka sai kin zauna gidan sarauta kema" Lantana ta karashe maganar kmar zautacciya Shamsiyya tace"Wai hayaniyar me nake ji ne tun dazu ina bacci" Nan Lantana ta kwashe duk abunda yake faruwa ta fada mata" Wani irin k'yashi da bakin ciki da hassada ne suka dura a zuciyar Shamsiyya ,rashin abunyi ne yasa ta fashewa da kuka wurjanjan! ta kalli inda mahaifiyarta take zaune kamar mutum mutumi,sai kace wata gunki tace"Uwa! kina raye a duniya haka tafaru damu k'askantacciya ta fimu komai kullum.kina cewa zaki sabautata mata rayuwa, gashinan kina zaune taje ta auri dan gidan sarauta mu muna zaune" "Wayyo na shiga uku na lalace"! Sosai Shamsiyya take kurma ihi! Wata wawar ajiyar zuciya Uwa! ta sauke zuciyarta cike da bakin ciki gami da hassada, a halin da ake ciki yanzu batasan yadda zata fara ba,amma ya zama dole ta bazama k'auyuka gurin malamai da bokaye, domin samawa kanta mafuta lallai maganar hauwa ta tabbata inda suke cewa dan hakin da ka raina shike tsone maka ido, a halin yanzu duk hankalin ya karkarta gurin ganin yaya za'ayi su sabauta Bawa Balaraba rayuwa ko ta mutu ko tai rai ko ta haukace cikin uku za ayi daya https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ» γγγγγγγγγγγγγγγ _*GIMBIYA BALARABA*_ πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ» _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *BINTUBATULAπ* _MARUBUCIAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* _*Zamani writers Association*_ ________________________ *We are her to educate motivate and entertain aur Reades* _________________________ *DIDEGATED* *to* RAHAMA ALIYU BISIMILLAHIR_RAHAMANIR RAHIM ``` Tunanin ka kamanin ka d'an uwa ka tsare kanka, Allah yai maka albarka, sai ka gyara makomar ka``` _*Wannan magana taka haka take fasihin mawak'i Musbahu m Ahamad*_ *Allah kasa mu dace* *π Ώ79* Da sauri Uwa!ta mik'e har zanin dake d'aure a jikinta yana k'okarin fad'uwa k'asa, tayi saurin rikeshi ta tsallake Sallau da kwance magashiyan a dandaryar k'asa,sai nishi yake,d'akinta ta afka kamar mahaukaciya,taje ta zura rigarta ta yafo mayafi ta futo, tana kallon Shamsiyya tace"Maza jeki sako riga mu baza ma,domin zama bai gan mu ba" Da sauri Shamsiyya ta shiga dakin domin sako riga. Lantana ta kalli Uwa!dake tsaye tana zazzage kud'i a cikin banki irin na gwangwani,tana lissafawa, tace"Uwa!yanzu, waye zai kula da Sallau gashi a kwance, kin san nima futa zanyi,yau na tashi bani da ko kwabo" Hararta Uwa!tayi tace"Ai yau dole ki hak'ura da zuwa ko ina ki tsaya ki kula da d'anki daga nan har zuwa lokacin da zan dawo, domin kema zaman jiyya ya kama ki" Lantana ta karyar da kai gwanin tausayi tace"To tunda kince haka shikkenan zan zauna, nasan dai zaki sammin abunci da zansa a baki na" Uwa!tace"Idan Shamsiyya ta dawo daga talla ta ciri dari biyu tayi cefa ne,ina da sauran garin kwaki,sai ta tuk'a muku teba,daga nan har dare,in kun ga bamu dawo ba to ku rufe Gida kawai domin in na futa yanzu sai inda mai ya tsaya" Lantana tace"To to shikkenan ai,Allah dai ya bada sa'a, a samo nasara" Uwa!tace"Ameen, ai in kana da kudinka komai me sauk'i ne, dama Dan me nake neman kud'in duk dan "yayana,saboda haka yau ranar sune" Tafad'a tana lissafa kudinta sun kai kusan dubu goma sha bakwai.haka ta zufa basu cikin wata karamar jaka, ta rataya ta a kafad'a Shamsiyya ta futo daga daki. Suna futa tsakar gida suka ci karo da Sadiya matar Kawu Mamman tana tsaye bakin k'ofar ta duk abunda yake faruwa a kunnenta. Kallonsu tayi tana me tausaya musu,ganin suna nema su jefa kansu cikin halaka,tace"Uwa!kiji tsoron Allah, ki tuna akwai ranar tsayuwa, me Balaraba tayi miki kike nema ki jefa rayuwarta cikin musiba,ki sani da shi sharri d'an aike ne, zuwa yake ya dawo saboda haka Ina mai tunasar dake cewar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108