Chapter 13
Chapter 13
suka fito suna rokarsu suyi hakuri ,Amma Ina!! Sam sun ki hakura sai dukanshi suke Suna Tambayar inda ya kai Wayar Mutane, Amma Yaki Magana Sabida tsabar Taurin Kai!! Makota cike da gidan suna Kallon ikon Allah ,dayawa daga cikinsu cewa suke Alhakin Hafsatu ne ya fara kama Uwa! Uwa! Ko Na can tana zagi Sallau Cikin Rashin kunya tace"So lubiyo Namijin hotiho ,kana tsaye a shigo har gida ana dukan Dan ka ka kasa tabuka komai, kai dai kayi Asara Wallahi *Balaraba* ce ta shi go gidan Jikinta Sanye da kayan Makarantar Isilamiyya Riga da wando da Hijabi ,Kafadar ta sakale da jakar buhu ,Wacce ta sanya Alkur'ani hade da Sauran Littatafan Addini. Da kyar! Ta samu ta Ku tsa cikin Mutane ta isa gurinsu,Hsnkalinta Nakan su Umaruru ,Ganin suna dukan Iro babu Imani gashi kowa yayi shiru, Lantana Ta kalleta ta Watsar Tace"Kunga barauniya nan ita zaku doka Ba iro ba domin ita ke min satar "Yan kudade na idan naje Tallah Na dawo ko tausayi Na,bata ji Sabida tsabar Rashin Imani" Ta karashe Maganar tana mikewa Tsaye Dukan ninsu suka joyo suna Kallon *Balaraba* jin Abinda Lantana take fada a kan ta, Hakan yaba Iro da mar tserewa da gudu yayi Waje hanci a fashe yana jini ,ga jikinshi yayi budu budu Rigar da yake sanye da ita ma ta yage! Tsabar Wahala Umaruru Yace" *Balaraba* kin dawo daga Makarantar"? "Eh Umaruru Balaraba ta fada cikin Nutsuwa Umaruru ya Kalli Lantana ,yace" Wallahi kuji tsoran Allah da ranar Lahira tsohuwa ,Ku dinga fadin Alkairi a kan Dan Wani *Balaraba* yarinyar kirki ce,Domin ba 'a taba kamata da kayan Sata b..... Uwa ta katse shi ta hanyar Cewa"Dole kafadi haka mana Munafiki Allah ta Allah ,sabida kana kama ta ka latse a lungu da sako ,Ai mun San duk Abinda yake Faruwa ,Babu Abinda bamu Sani ba" Ehee!! Kuka Mai cin Rai Hafsatu ta fashe dashi ,ta shige dakin ta da gudu,ita ko *Balaraba* Tana tsaye Babu Cikin dakiya idon ta tar! Duk da a lokacin tana da kananun Shekaru ta Gama gane Bata Da babbar Makiyya kamar Uwa! _BINTA UMAR ABBALE_ *MARUBUCIYAR* *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* 08089965176 [04/05, 03:15] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? 🧝🏻♀🧝🏻♀🧝🏻♀🧝🏻♀🧝🏻♀🧝🏻♀ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 🧝🏻♀🧝🏻♀🧝🏻♀🧝🏻♀🧝🏻♀🧝🏻♀ *by* _BINTA UMAR_ *MAMAN ABDUL WAHABU* _ZAMANI WRITES ASSOCIATION_ *🅿22* Uwa! ta cigaba da cewa "dama duk wannan yawon da take yi da sunan zuwa makaranta ,mun san iskanci take tafiya tunda dama "yar nagada ce ,sabida haka kufadi kudin wayar ku a biya ku domin ana da abin da za'a biya, Ta karashe maganar cikin kuri! da cika baki,sabida tasan bata da wasu kudi idan ba jarin a wararta ba, Umaruru mamaki ya cika shi jin abinda uwa take fada,sai ya girgiza kai kawai yana mamakin sharrin wasu matan ,shiyasa a kace ko shedan yana gudun sharrin mace, Balaraba kuwa tana tsaye babu damuwa a tare da ita domin in da sabo yaci ace tasaba da irin kiyyar da suke nuna ma ita da iyayenta, shiyasa abin baya damunta da yake yarinya ce mai taurin zuciya ,sai dai abin yai ta damun mahaifiyar ta,itama babu abinda take iya yi idan ba kuka ba. Umaruru ya kalli uwa! dake tsaye tana hura hanci! yace"kudin wayar nan dubu bakwai da dari biyar ne ,sabida haka tilas a biya ,hakan kuma ba ya na nufin cewar in muga iro baza mu damka shi ga hukuma ba,tundadai kowa ya shaida da hakan. Sallau yayi saurin tarar sa yana kwantar da kai yace"umaruru kuyi hakuri a kashe magana anan don Allah za muyi masa fada ,in sha Allah bazai kara ba. Uwa Kuwa da taji maganar dubu bakwai gabanta ya yanke ya fadi sabida tasan dudu-du jarin a wararta bai kai na dubu uku ba,kuma dashi take joyawa suna cin abinci sai tafara sake-saken yadda zatayi, "Tun yaushe kake fadar haka,cewar zaka ja kunnesa naji labari cewar ai kai yake kawowa kudin kuke rabawa shiyasa kake daure masa gindi Sallau ya gigice sai rantse rantsa yake yace"ni ko kwabo baya bani ban sani ba ko uwarsa yake kawowa gatanan a gabanku ni babu ruwana" Dama umaruru ya fadi maganar ne domin ya tsoratar da shi. Cikin uwa! ya duri ruwa sabida tasan idan suka gane tana karbar wani abu daga hannun iro itama ba kyaleta zasuyi ba, Tayi sauri ta katse sallau dake basu hakuri,cikin rashin kunya tace"dallah malam matsa kabawa mutane guri solobiyo kawai,kai umaruru nawa kace ma kudin wayar,? tafadi maganar sai kace wacce zata iya biya "Dubu bakwai dari biyar ne" Ta kalli Lantana wacce tunda zu ta kasa furta ko a sabida taji ana maganar biyan kudin waya, ita kam bata da ko kwabo ba zata bayar ba. "Lantana ki fito da kudin nan danaga kina lissafawa a biyasu kudinsu ,tunda dai kema iro yana mora miki kullum da daddare sai kin ce ya siyo miki balangu ko kifi" Lantana tayi tsuru-tsuru tana motsa baki ,da kyar! tace "mai nake dashi "yannan ! da zan bayar so kike na rusa jarina" Cikin rashin mutumchi Uwa tace "Lantana dole fa kifito da kudin jikinki ko kinqi ko kinso wallahi domin bazan bari su kashemin da ba,ehee"!! Da kyar! Lantana ta kwance zaninta tana daga zaune ,sai surutai take tafito da "yan ashirin ashirin da "yan goma goma ,kwata kwata a kudin babu hamsin ko daya Uwa tazo ta kwashi kudin da sauri ,tafara lissafawa, *Balaraba ko na tsaye cikinta kamar ya kulle dan dariya sai boye dariyar take dan kar ta fito amma INA! sai da ta subuce mata ta zauna kasan gurin tana yi tana kallon Lantana dake faman share gumi! Sai tsine-tsine take,wai sam bata yadda ba kalawa Iro sata a kayi ,Aiko Lantana ta dauki wata sanda da suke tone kwatarsu idan ta toshe ta kaiwa Balaraba duka da ita tana faman zaginta ta uwa ta uba. Balaraba ta mike da sauri ta shige dakinsu tana jiyo Lantana kamar mahaukaciya tana ta dura mata ashar tamkar ba tsohuwa ba. To da kyar! dai Uwa ta samu ta hada dubu uku da dari biyu,domin kudin gun Lantana ko dari biyar basu kai ba,ta mikawa Umaruru gami da cewa"gashinan Abinda ya samu kenan,Shamsiyya bata dawo daga tallaba,kuje kubawa mai wayar hakuri idan an kwana biyu za'a cika masa kudinsa,domin Allah ya hore abin da za'a biya Umaruru ya karbi kudin yana lissafawa tsaf! Yace "kifadi ranar da zaki ciko kudin kawai bama son jeka ka dawo" Tabe baki tayi tace"ku dawo rana ita yau zan Baku kudinku" "To Allah ya kaimu kar muzo kice wani abu fa" "Mtssss nifa nace kudawo Ku karba ,akin banza akin wofi,Uwa! tafada a zafafe ,bakin cikinta yadda ta rusa jarinta yanzu kafin ya tashi ma aiki ne Umaruru yaja ta wagarshi suka fice daga gidan,suna fita Uwa tace dawa Allah ya hada ta duk wanda ya kwana ya tashi a gidan sai taci masa mutumchi kar dai Sallau yaji labari, Simi-Simi ya kama hanya zai shige daki ,tayi saurin janyo masa riga gar wuyanta ya yage ,tace"kama hanya ka fita ka nemo mana abinda zamu ci ehe! wallahi baza ka shigarmin daki ka zauna min ka kashe min katifa babu abinda kake min sai dai in nema ,in ci da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108