Chapter 60
Chapter 60
hira, nan suka ga shigowar mahaifin su hankalin sa a tashe, Khalifa ne yace" Allah yasa lafiya dai na ganka kana faman gumi! Zama yayi cikin kujera yana cire rawanin dake nannad'e a kansa,yace"je ka kira min mahaifiyar ka" Tafiya yayi kiranta, ya kalli sauran yaransa da kumfar baki yace" in dai nine na haife ku daga yau na rabaku da Moddibo har abada babu ni babu shi hakanan kuma babu ku babu shi" Cikin rashin fahimta Ishak yace"ban fahimci me kake nufi ba Baba" Zuwan mahaifiyar tasu ne ya dakatar da maganar da yake tazo ta zauna kusa da mijin nata,tana kallon fuskarsa tasan lallai yau an tab'oshi" "Lafiya ranka ya dad'e"? Ta fad'a cikin sigar tambaya. Waziri yace" zaki ce min baki san abunda yake faruwa bane? kun had'a kai da d'anki kun munafurce ni, yaje ya d'auko yarinya da suka gama lalacewa da ita a waje ya kawo wa wannan mak'iyin nawa ya d'aura masa aure da ita" "Duk maganar da kakeyi ban fahimce ka ba,domin kuwa ni ban San abunda yake faruwa ba" Girgiza kai yayi kawai ya umarci d'aya daga cikin yaran dake zaune a gurin yaje ya kira Moddibo. Hankalin kowa ya tashi a gurin saboda sun san halin mahaifin nasu bai iya b'acin rai ba. Mintuna goma tsakani Moddibo suka shigo tare da Ishak d'an uwansa Ko zama Waziri Zayyanu bai bari yayi ba,yace"Umarni na ne ni ne nasa a kira ka, saboda dalilai masu k'arfi,yanzu-yanzu nake so ka furta cewar ka saki wannan yarinyar da kasa aka d'aura maka aure da ita,idan kuma kak'i ni yanzu zan saki taka Uwar,saboda haka zab'i ya rage naka." *Muje zuwa* *Comment Vote and Share* [05/08, 20:08] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ ________________________ _*We are here to educate,motivate and entertain aur readers*_ ________________________ _*DIDEGATED*_ _*TO*_ ```RAHAMA ALIYU``` _BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM_ *🅿68* Dukaninsu sun furgita da jin furucin da mahaifin nasu yayi, ita kanta mahaifiyar tasu ta girgiza da furucin da mijin nata yayi,kuma tafi kowa sanin halinsa zai iya aikata duk abunda ya fad'a. Modibbo ya shiga, tsaka me wuya bai tab'a tsammanin hukuncin da mahaifin nasa zai yanke ba kenan,iya tunanin sa yana ganin zaiyi fushi dashi daga baya ya sakko shi kuma sai ya nemi afuwar sa, tabbas Uwa-Uwa ce, babu ta yadda za'ayi ta sanadiyar sa ya rushe auran da aka d'aurashi sama da shekara talatin da wani abu,dole duk son da yake wa Balaraba ya rabu da ita ko da hakan zai yi sanadiyar rasa rayuwarsa, a kan mahaifiyar sa babu abunda ba zai iya ba. Khalifa ne mara kunya sosai ya cikinsu yace"Mu baza ka jawo mana b'acin rai!ba a cikin gida saboda haka kabi umarnin da a ka baka, idan ba haka ba zamu b'ata maka rai kuma zamu hana matar taka daka aura jin dad'in duniya,a kan mahaifiyar mu,babu abunda baza muyi ba" Jin furcin da Khalifa yayi yasa Waziri umartar sa da yaje ya d'auko takarda sa biro, aikuwa da sauri ya tafi, ita kuwa Hajiya Kattime tana zaune tana kallon ikon Allah bakinta ya mutu, takasa fahimtar komai, a wannan badak'alar da take faruwa. Khalifa ya dawo hannusa rik'e da farar takarda da biro ya zo ya mik'awa Moddibo, guda d'aya, d'ayar kuma yaje ya kai wa mahaifin nasu ganin Waziri ya d'ora biro jikin takkada yasa Moddibo saurin dakatar dashi, da hannu jikinshi na kyarma! yayin da gumi yake zuba a jikinsa, ya d'ora biyu jikin farar takarda yayi rubutu kayi biyu,kamar haka. _Ni Yusuf Moddibo na saki matata Balaraba Ayuba Tanko saki d'aya kacal, kan wani dalili guda d'aya, ina fatan Allah ya had'amu da ita a aljanar Firdausi_ Yana gama rubutuwa ya ninke takadar, zuciyarsa tana wani bugawa fatt!!fatt!fatt! Waziri Zaiyyanu ya mik'a masa hannu yana nufin ya bashi takardar, a hankali ya karasa inda yake zaune ya mik'a masa, bud'e takardar yayi ya karanta ya mayar ya ninke ta ya aje ta gefe,wani takarda ya kara cirowa ya mik'awa Moddibo cikin bada Umarni yace"Saki uku zaka rubuta mata,saboda nasan halin wancan mutsiyacin zai iya turasasa ka ka mayar da ita,don haka ban yarda da saki d'aya ba" Cikin tsantsar b'acin rai Hajiya Kattime tace"Wannan abunda kake tsantsar jahilci ne da son kai, Allah da kansa shi ya hallici saki,kuma ya umarci da ayi shi,amma kuma baya son ayi din,saboda haka tunda ka tursashi ya rubuta saki d'aya saboda son zuciyar ka to ka kyaleshi haka, ba lallai sai an saki mace saki uku ba take sakuwa,saki d'aya ma ya hallata" Cikin tsawa Waziri yace"Zakayi abunda na saka ko sai ka gama jin hudubar da mahaifiyar taka take maka" Ganin Moddibo ya tsaya yayi shiru da takarda a hannu yasa Waziri ya d'ora biron dake hannusa a jikin takarda ya fara rubutu. Moddibo ya rik'e hannunsa jikinsa zafi rad'au! muryasa a shak'e yace"Baba Waziri ka gafarce ni, idan nayi maka,laifi, ni Yusuf Moddibo na saki Matata Balaraba saki uku" "Innalilahi wa inna ilaihi rajiun" Shine abunda Kattime take fad'a zuciyarta kamar tayi bunduga tarasa wane irin bakar zuciya ne da mijin nata. Mik'a masa takardar yayi a karo na uku yace"rubuta min da hannun ka" Ganin babu abunda yayi saura yasa Moddibo ya rubuta ya mik'a masa, ya bud'e ya karanta tsaf, cikin bada Umarni yace"Ka tafi da kanka kaje ka kaiwa wanda ya d'aura maka auran" Moddibo ya karb'i takardar ya kama hanya, yana tafiya yana had'a hanya jiri yana kwasar sa,Allah yasa bangaran babu ma'aikata sosai, sai da ya futa harabar gidan sarautar sannan ya dai-dai ta nutsuwar shi,amma duk da haka duk Wanda ya kalleshi a lokacin yasan yana cikin tsananin damuwa, haka ya isa fada, lokacin ana shirye-shirye kiran sallaar magariba me Martaba ya futo kenan domin shiga gida suka ci karo da Moddibo, yana kallonsa ya gane da akwai matsala, kafin yace komai Moddibo ya mik'a masa takardar hannunsa, da sauri maga takarda ya karb'a ya bud'e ya fara karantawa kamar haka. _Ni Yusuf Waziri Zayyanu na saki matata Balaraba Ayuba Tanko saki uku,saboda wani dalili,ina rokon Allah ya had'amu da ita a aljanar Firdausi_ *Innalilahi wa innailaihi raji'un* Kalmar da me Martaba yake ta maimai tawa kenan, kafin su ankara Moddibo ya zube a gurin yana wani irin murk'ususu, jini na fita ta baki ta hanci, ya rik'e cikinsa tamau! bakinsa na motsi,kalamar shahada kawai yake Sarki! ne ya futo daga b'angaransa ya na d'aure da alwala,sai ya hango abunda yake faruwa saboda haka cikin sauri da sassarfa ya k'arasa gurin,lokaci mutane har sun taro, hankali a tashe ya tsuguna ya d'ora gwiwarsa a k'asa ya d'auki kan Moddibo ya d'ora a cinyarsa, cikin damuwa ya sanya gefen rigar shi yana goge masa jinin dake futa daga bakinsa, Moddibo ya rik'e hannunsa tamau!! wani hawaye yana zuba ta gefen fuskarsa, muryarsa bata futa sosai yace"Allah yayi bazan yi tsayin kwana ba, a duniya balle in rayu da yarinyar da zuciyata take mutukar so, d'an uwana ne kai ko na mutu kai na amunce da ka maye gurbi na gurin Balaraba, ka bata hakuri,ga tanan na bar maka amana son Balaraba wani b'angare ne na zuciyata na tabbata ko na rayu a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108