Skip to content

Chapter 21

Chapter 21

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,232 words 0 views Progress saved
Download Book

dai-dai na dan nashi yayi masa hudu ba kamar yadda Annabi ya fada sannan ya kira shi da sunansa sau uku, sai ya mike tsaye gami da rungumeshi ya ce zamuje fada dashi domin tasan da zuwansa" Hankalin Fulani ya tashi amma sai ta dakewa zuciyarta tayi addu'a tasan babu abinda zai samu dan ta face da sanin ubangiji, nan Maimartaba ya fita da jinjirin a hannunshi fuskarshi dauke da walwala Fada na cigaba da tafiya kawai suka ga sarki ya shigo rungume da yaro nan hankalin kowa ya tashi aka fara rige-rigen karbar yaron Waziri Zayyanu ne yayi nasarar karbarshi daga hannun sarki lokacin da ya zauna yace"ranka shi dade a ina muka samu yaro mai kama da kai sak, sai kace an tsaga kara" A nutse Maimartaba ya ce"yau Allah yayi min baiwarshi Allah ya sauki Fulani lafiya shine dalilin kirana" Saura kadan Waziri ya yar da yaron jikinshi ya dinga karkarwa kafin kace kwabo gumi ya jika masa riga sai yafara mutsu mutsu da baki kwata-kwata ya rasa abinda zai ce, fada ta dauki murna kowa yana fadin albarkacin bakinsa wasu na boye damuwarsu ban da Waziri domin mikewa yayi ya bar fadar yana sabe babbar riga tamkar zai tashi sama haka shige gidansa dake cikin gidan sarautar, Kafin kace kwabo Labari ya watsu cikin gidan, Uwar gidan Maimartaba ta turo Jakadiyar ta domin ta tabbatar sannan tasa a ka kira mata malaminta domin yayi mata binkice, malamin yace"wannan yaron da a ka haifa ba zamu iya kashe shi ba sabuda yin haka zai janyo mana shiga hadari dani dake, amma abinda zamuyi masa guda daya ne zamu iya cire masa son mulki a cikin zuciyarsa sai dai yaga ana yi" Tace"dama ai abinda nake so kenan kamar yadda ban hafi namiji ba haka bana so wata ta zo ta haifi namiji wanda zai gaji sarauta sabuda haka kawai a cire masa son mulki inda hali ma a sanya masa tsanar gidan nan ko a kada shi ina nufin ai masa kurciya kawai ya bar garin gaba daya" "Zamuyi kokari iya iyawarmu ke dai duk abinda muka umarce ki kiyi kar ki fasa,yanzu dole zamuyi yanke-yanke kuma zamuyi kwanan bori in gari ya waye sai ayi sadake sadake zakiga abin mamaki" Haka suka dinga dauki ba dadi kan zuwan Sarki Almansor duniya dan ganin sun sabauta shi tun yana yaro amma da yake yana cikin kariyar Allah hade da addu'ar iyaye babu abinda ya sameshi dan gane da mugun abun da suke masa kullum cigaba yakeyi har kawowa yau da ake masa maganar aure. *Wannan kenan* Wayarshi ce tayi kara ya dauka yana dubawa. Maddibo2 sunan da ya gani kenan, a hankali ya daga yayi gyaran murya gami da cewa, ka shigo ne"? Daga daya bangaran Maddibo yace"Eh gani a fada muna gaisawa da mai maimartaba yanzu zan shigo" "Ok in bangaran Ummi" "Shikkenan zan shigo yanzu dama ina so mu gaisa da ita wallahi" "Sai ka shigo" yafada yana kakarin kashe wayar Ummi tace"kai da waye" "Maddibo ne" Murmushi tayi tace"ai shi babu ruwanshi wallahi na lura baya biyewa sauran "yan uwanshi, ya kan zo lokaci zuwa lokaci muna gaisawa" "Shiyasa muke shiri dashi sosai Ummi kin san bana shiri da mutum munafiki" "Nan Maddibo ya shigo ya zube gaban Ummi yana kwasar gaisuwa.Cikin sakin fuska Ummi ta amsa masa tana tambayarsa mutanan gida,yace" Ummi ni yau kwanana biyu da dawo wallahi gidan ma sai jiya na shiga" "Ayya to masha Allah, in ka kara shiga a mika min gaisuwa gurin iyayen naka" "Zasuji in sha Allah Ummi" Nan suka mike tare Ummi tana ta shi musu albarka tana musu fatan dorewar zumuncinsu Ban garan Sa suka nufa suna tafiya suna hira yayin da hadiman da suke harabar gurin suka dinga kawo gaisuwa Maddibo ne kawai yake amsawa shiko uban gayyar tafiya kawai yake kansa a kasa tamkar wanda ba ya son kallon rana, Wasu hadaddun kujeru suka zauna wanda suke kewaye da kayattacan falon wanda ya sha shimfido irin na gidan sarauta ga wasu manya-manyan tuntu can kan wani tudu shima ya sha shimfidu masu kyau, kafin ka hau sai ka taka matattakala nan yake zama in zai huta in baya son fita waje Maddibo yace"na lura sam baka iya tarbar baki ba wallahi baka ji yadda makogaro na ya bushe ba, a ko ruwa ka bani in sha" Wani irin kallo yayi masa yana ya mutse fuska yace"in har nine zan kawo maka ruwa zaka kwana a nan" Dariya yayi ya mike yace"masifaffe kawai kar Allah ya sa ka bani,ai ina da kafafu" Tsaki yaja yana lumshe ido yace"kasan kana da kafafu meye na magana" Sabuda ka rai namin hankali ni zan kawo maka ruwa ko kar Allah ya sa ka sha" Maddibo yace"dan Allah kar kadame ni da masifa ka tsaya ka saurari abinda nazo dashi, Yafada yana zama kusa dashi yana kokarin bude ruwan goran sake hannunsa *Muje zuwa* [28/06, 06:33] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† _*GIMBIYA BALARABA*_ βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» _*Na*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` Zamani Writes Association🀝🏻 ```Bisimillahir rahamanir rahim``` *πŸ…Ώ33* _____Cikin Yanayin maganar shi yace"Allah yasa magana ce me muhumanci, kazo kana wani damuna matsalata tafi taka" Ajiye robar ruwan yayi bayan ya gama sha yace" magana ce mai muhumanci mana, tun kafin inyi tafiya naso mu zauna muyi maganar Allah bai nufa ba sai yanzu" Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya cigaba da cewa"akwai yarinyar da na hadu da ita wallahi a garin yawace-yawace na na resturant, kasan ni dai da son abinci mai dadi,kawai kwanaki Buba ya dauke ni muka shiga kasuwa gurin wani abokinshi, a lokacin yunwa duk ta ishe ni, dole tasa muka futo daga kasuwar domin mu samu abunda zamuci, kawai Buba yace a kwai gurun cin abinci mai kyau bakin kasuwar mu tsaya muci ba sai mun futa wajan gari ba.Tunda muka shiga gurin idona yayi tozali da yarinyar naji duk duniya babu macan da ta dace da ni kamarta, yanzu abinda nakeso da kai kawai ka shige min gaba gurin neman auranta domin nikam nayi mata" Maddibo ya karashe maganar tashi yana sauke ajiyar zuciya, fuskarshi cike da farin ciki da annushuwa. Wani irin tsaki Sarki! yaja yana wa Maddibo wani irin kallo yace"Lallai ka rai namin hankali wallahi , duk ka gama ya wace ya wacen ka kazo ka kare a gurin mai tuwo-tuwo sabuda tsabar ka rai na ni kazo kace in shige maka gaba, kar Allah yasa ka aure ta din" Maddibo ya karyar da kai kamar wani maraya yace"Kasan kuwa yadda nake son yarinyar nan, wato na kawo maka kuka na kai da nake tunanin zaka sharemin hawaye ka mara min baya a kan al'amarin zaka sace min gwiwa, bai kamata kayi min haka ba, Alhaji" "Kaga malam nifa ka fitar dani daga cikin wannan al'amarin haka kawai kai karasa wacce zaka ce kana so sai " yar tallah a bakin kasuwa, kai ka san "yayan tallan nan ba tarbiya ce da su ba, ka sani ma ko tana biye-biyen maza kawai kaje ka kwasowa kanka datti da karzuwa, ka bata mana zuri'a kar ka kara sani a cikin wannan shirmen naka" Cikin fusata!Madibbo ya dakatar da shi, yace"kayi karya kace wannan yarinyar

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108