Chapter 41
Chapter 41
ta, tsayawa yayi yace" yawwa dama d'azu gajiya nayi na futa sabuda abokai na suna jirana a waje gashi baki dawo ba, sabuda haka yanzu me ake ciki, ki kawo kud'in da nace ki bayar domin za a sai wa Iro magani yanzu" "Kawu ina takkadun gida da shago na wanda Maimartaba da yaron shi ya bani gurin saukata"? Gabanshi ne ya fad'i sosai sabuda tun lokacin da ya karb'i takaddun daga hannunta yaje ya sanya su a caca lokaci guda a ka cinye shi cikin inda-inda yace" wannan maganar ki aje ta gefe guda domin bazan baki a hannun ki ba, sunan na adana miki" "Kawu kaje na bar maka su, kayi hakuri ni a yanzu bani da wani k'udi da zan baka, wallahi" tafad'a tana k'okarin shiga band'aki sabuda tasan tunda ta ganshi ya shigo afujajan tasan daga gurin caca yake, watakila an cinye shi ne ya tawo yana neman kud'i ruwa a jallo,tasan ko ta bashi k'udin gurin caca zai koma baba wani magani da zai sai wa Iro, tana jinshi yana zaginta ta shigewar ta band'aki, bayan ya gama zage-zagen nasa d'akin Lantana ya nufa sai kace zararre, cikin ikon Allah duk ya taddasu suna bacci, nan ya tsallake su ya shige k'uryar d'akin ya fara laluben inda, Uwa! take ajiyar kud'i Allah ya bashi sa'a ya ga wani k'aton banki, batare da b'ata lokaci ba ya fasa shi ya kud'i ne a ciki kimanin dubu bakwai, ya lissafa dubu biyar ya bar sauran dubu biyu, a watse a gurin ya tsallake yayi ficewar sa daga gidan. *Muje zuwa* ```Shin Balaraba in ta bar gidan ina zata koma?``` ```Idan Uwa! ta wayi gari taga bankin ta a fashe wace irin masifa ce zata biyo baya```? ```Ta yaya Sarki! zai fara bunkican Asalin Balaraba```? ``` Menene a zuciyar Sarki!dangane da Balaraba```? ```Maddibo ne mijin Balaraba ko Sarki!?``` *Duk wannan amsoshin suna gaba, ku cigaba da bina domin ganin wace irin waina za'a toya* *Comment* *Vote and Share* [16/07, 21:17] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^° _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®{REAL BINTU BATULA}👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{RAHAMA ALIYU}``` _ZAMANI WRITES_ _ASSOCIATION_🤝🏻 ```Bisimillahir-rahamanir-rashim``` *🅿51* Bayan ta idar da sallahr tayi addu'oin ta kamar yadda ta saba, Usuman ne ya farka daga bacci ya fara kuka, " Yaya yunwa nakeji, abunda yaron ya fad'a, Sadiya ta hau tashi daga bacci,sam ta manta bata basu abunci ba suka kwanta bacci, Sadiya ta mik'e zaune tana mutsike ido, Balaraba tace"tashi kuci abunci,kinga Usuman ya tashi yana kuka,maza jeki dakin Iya ki dauko kular abuncin ku,da sauri Sadiya ta mike, ta nufi d'akin Iya, Iya na kwance kan dadduma bayan ta idar da sallah wani bacci ne me dad'i yake fuzgarta, zazzab'in ya sauka domin har wani gumi take, Sadiya tayi sallama, d'akin Iya ta mik'e zaune tace"Lafiya Sadiya"? Iya kular abuncin mu zan dauka" Iya ta koma ta kwanta,tana cewa "in kin futa ki ja min k'ofar, nan Sadiya ta d'auki kular ta futa daga d'aki, Bud'e kular Balaraba tayi tana duba abuncin, babu abunda yayi duk da yake dafa duka ce, har yanzu da zafinsa, nan ta zuba musu suka fara ci pure watar ta dauko musu guda biyu, Usuman yace" Yayarmu ke bazaki ci abuncin ba"? "Zanci mana Usuman kai da kuci ku koshi" tafad'a cike da tausayin yaran, bayan sun gama ta rakasu suka wanke hannuwan su, suka dawo ta gyara musu kwanciya suka kwanta, nan ita kuma ta cigaba da had'a "yan kayanta da suka rage tana sakawa cikin a kwatu, domin taci alwashin barin gidan gobe daga yau ta bar kwana a gidan, Sai wajan karfe d'aya saura na dare sannan ta kwanta, cikin ikon Allah a subar fari ta tashi daga bacci ta futo ta d'aura alwala ta koma d'aki da sauri ganin ana iska sosai hadari ya had'u har an fara yayyafi, tanaji massalacin bayan gidansu sun tayar ta bisu sallah, bayan an idar da sallahr rayi addu'onta, ta cigaba da zama kan dadduma tana jan carbi kamar yadda ta saba, wajan karfe shida, ta fara jin motsin mutanan gidan, sun fara futowa, bacci ne yake fuzgar ta kad'an-kad'an sai taji hayaniyar Uwa! tana buga kyauran d'akinta ta tare wa Sallau hanyar wucewa tana kunzuma masa ashar! "Wallahi tallahi babu wanda zai yi min wannan d'anyan aikin sai kai,domin dama kasha auna fasa min asusu na,ina kama ka,shine jiya ka faki idona, sai da kabari nayi bacci kafasa ka kwashe min kud'i ,wallahi Sallau ko ni ko kai a gidannan domin bazan sha wahalar neman kud'i na ba,ka dinga bin dare kana sacewa, eheee! ba zata sab'uba bunduga a ruwa! Ta karasa maganar tana tattaro wuyan rigarsa ta cukume shi, " Shikkenan daga kin ga an fasa miki banki an kwasar miki kud'i sai kice nine sabuda kin raina ni duk b'arayin "yayanki bakya tuhumar kowa sai ni, to komai masifar ki dole ne ki sake ni,inje inyi alwala inyi sallah tunda ke baza kiyi ba, baza ki hanani yi ba" "Kai dallah! rufe min baki" tafada tana kai hannuta dai-dai bakinsa kamar zata gwab'e ta cigaba da cewa"kai har kana da bakin da zaka fad'i wata magana a kan sallah, akwai babban makiyin Allah irinka, ai Sallau in kaga na cika ka agurun nan to tabbata ka futo min da kud'ina" Tafad'a tana k'ara tattaro wuyan rigar sa, k'arfi yasa ya angije ta, tafad'i k'asa ragwajab! ya futo daga d'akin da sauri, ya nufi k'ofar futa daga gidan, da gudu ta biyo bayanshi tana huci! cikin tashin hankali da masifa tace" ni ka tunkud'e ko, har kasa na fad'i a gaban yara na, to yau zanga yanda za'ayi ka futa daga gidan nan mutukar ba kud'ina ka bani ba" Mutan gidan duk sun futo suna kallon ikon Allah, Uwa! ta shak'e wuyan Sallau sai huci take, dama d'azu shammatar ta yayi ya ingije ta d'azu domin Uwa tana da mugun k'arfi sai kace doki haka take, K'ifta ido yake kamar b'era a ruwan zafi, bakin sai karkarwa yake,ya rasa abun cewa, duk alamu na rashin gaskiya ya bayyana a tattare da shi. "Ke dan ubanki sakar min wuyan d'ana kar ki kashe min shi ki cuce ni" Lanatana tafad'a lokacin da ta karaso inda suke, cikin tashin hankali take k'okarin b'anbare hannun Uwa!daga wuyan Sallau, doke hannun Uwa tayi, cikin rashin kunya tace"kinga Lantana, matsa dan Allah sam baki iya komai ba sai munafurci da kwad'ayi, in kinga na sake shi to sai ya futo min da k'udina ehee!" Gefe guda Lantana ta matsa tana rik'e hannun ta domin taji zafin buge mata hannu da tayi tace"shikkenan,to kashe shi ki huta mara kunyar yarinya kawai, a gidan ubanwa naje nayi k'wadayi da har kike kirana da haka" "Sai kiyi kuma kanki a keji" Uwa! tafad'a tana k'ara matse Sallau jikin garo Walidi ne ya shigo gidan, tashin sa kenan daga bacci ya fara jiyo hayaniya sabuda haka a fusace ya shiga gidan, cikin mamaki yake bin iyayen nasa da kallo, "Ke!dallah, wai menene haka, kuke sai kace wasu yara,k'ananu, ke Uwa! sakar masa wuya" yafad'a cike da bada umarini kamar shine Ubansu, "Walidi in kaga na saki wannan mutumin to sai ya futo min da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108