Skip to content

Chapter 6

Chapter 6

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,208 words 0 views Progress saved
Download Book

Balaraba gadan gadan! Dama sun saba dambe Dan su Shamsiyya basu da Hankali in dai Abu ya hadaka dasu Abu kadan sai a fara dambatuwa. Balaraba tayi saurin kaucewa daga jikin rijiya ta tari Shamsiyya tun kafin ta karaso suka kacame da kokawa Abin Mamaki!! Mabaruka tafara daukar Abubuwa tana dukan Balarabar dashi ganin ta kayar da Shamsiyya tana duka . Sai dura mata Ashar Mabaruka take ta Uwa ta Uba. Iya ta shiga tsakani tana rabawa gami da ruqe Balaraba Amma Ina!! Balaraba taqi rukuwa domin dama in tai zuciya fadanta baya rabuwa. Shiko Kawu sallau barin gurin yayi yana tsitstsinewa su Shamsiyya a zuciyarsa domin babu Halin yayi a fili sabida tsoran Masifar Uwa. Uwa dataga Ana cutar "yarta sai kawai ta daga ruwan daudar da take wanki dashi cikin roba ta kwararawa Balaraba a jiki tundaga tsakiyar kanta har zuwa qafarta tana ta zabga Mata zagi gami da mugun fata!! Da kyar Iya ta janye Balaraba daga kan shamsiyya tana bata hakuri gami da yi mata Fada, Shamsiyya da tasamu ta mike sai taciga ba da zagin Balaraba tana jin fan ta da kwanonisu Na cin Abinci Wanda suke gefe Dan qazanta har yanzu ba'a wanke ba qudaje sai bi suke gami da ruwan wanki da Uwa ! take kwara musu Har tasamu nasar jifanta a kanta gurin ya tasa ,cewa"take Wallahi sai naga bayanki Dan Uwarki karuwa Uwar tamu zaki dinga zagi shegiya wacce ba'a san Asalinta ba" Bakinci tamkar ya kashe Balaraba sai tafashe da kuka, a gurin su Sadiya da Shamsu kannanta suna taya dawowarsu kenan daga makarantar Allo,yara duk sun cika gidan, Iya ta janye Balaraba ta kai ta dakinta tana rarrashi tace"ko da yaushe ina fada miki ki daina Daka ta tasu Mabaruka su ba hankali garesu ba gashi yau a cikin farin ciki kike kinyi saukar Alku'ani mai girma Amma zaki bata wayonki Dan Allah ki daina kulasu. Cikin kuka tace"iya kinajin zagin da suke min fa wai mai Na tsarewa Uwa ita da yaranta suka tsane ni ,nifa basa bani ci basa bani sha komai bi nakewa kaina ni nake fita in nema in ciyar da kaina da kannena to gaskiya nagaji zan siyar da gado Na kawai in bar musu gidan gwara inje in kama haya sai yafi min" "Aa Balaraba kina nufin zaman kanki zakiyi bazai yihuba dama yaya Lafiyar kura kullum cikin yi miki sharri suke duk Wanda yaji cewar kin gama daki shikkenan sai zancensu ya tabbata ,ki kara hakuri kinji ko kwana nawane zaki yi Aurenki . "Aa Iya ki kyaleni kawai "tafada tana share hawaye. Iya tace"Aiko bazan kyaleki ba Balaraba yin hakan yana nuna cewar cin Amanar Dan Uwana Ayuba ,Sam baicancanci haka ba bayan haka kuma zumunchi bai CE haka ba Share hawaye tayi ta kalli su Sadiya da shamsu Wanda suke zaune sun zuba mata ido suma suna share hawaye,tace "kunci Abinci"? Girgiza kai sukai Alamun A'a. Mikewa tayi ta karbi mukullin dakinta gurin iya tace"Ku taso Ku je Ku siyo indomee sai in dafa muku kafin in daura girki" *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š 08089965176 [04/05, 03:04] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *✍🏻writting by* *Binta Umar* _*MAMAN ABDUL WAHABU*_ ~*MRS AHAMAD GWADABE*~ *πŸ…Ώ10* Dakinsu Na gado ,ta bude musu ,suka shiga ,tana jin su Mabaruka da Shamsiyya ,sai zaginta sukeyi har yanzu ,sai tayi musu banza, Tafito da kudi gudar Dari biyar Sabuwa dal! Tabawa Sadiya ,dake tafi Isyaku ,wayo ,tace maza taje ta siyo musu indome guda hudu ,sai ta dafa musu kafin ta Dora musu Abincin dare. Cikin Farin ciki Sadiya ta kar6a ,ta tafi kantin Abbah ,dake bakin layinsu siyowa Sai Murna takeyi dake yarinyar ,tana son. Indomee sosai ,shiyasa kullum said tayiwa Aunty tasu Addu'a in tayi Sallah,sabida duk Abinda suke Nema tana musu . *wannan kenan* *ASALIN LABARIN* ___________________ Malam Tanko Makeri Shine Ai nihin sunasa ,Wanda jama'a suke kuranshi dashi ,Amma A salin sunansa dayyabu " to tun yana yaro Mahaifinshi ya sanya masa Tanko kasancewar sunan Mahaifinshi ne dashi Shiyasa sunan ya buya idan ba Tanko Makeri kace ba babu Wanda zai gane. Mutum ne shi Wanda Allah yayi masa baiwa da Fasa ta qere qere duk Abinda ya kalla sau daya to in sha Allahu nan take zai qera makashi ,tamkar daga kamfani Shi kadai Mahaifinshi ya haifa ya koma ga Allah. Shi kuma tun tasowarsa mutum ne mai Auri saki ,Matarshi ta Farko Lantana itace Uwarsu Kawu Sallau da Kawu Maman ,Matarshi ta biyu "yayanta duk mata ne su biyar ,haka ta zubesu gaban Lantana ,tayi tafiyarta ,Lokacin da Auran ya Mutu. Lantana wata irin mace ce mai zuciyar kafurai bata da imani ko miskala zarratin,ita ke daura yaranta a kan mumun dabi'a Idan Tanko ya fita sana'arsa sai ta daurawa "yayan kishiyarta ,mata talla ,tace duk inda zasuje suje su siyar mata tallah har da daddare daura musu take ,idan suka qi kuwa tasa Sallau ya Zane su. Tun Tanko bai Sani ba har yazo ya sani ,yayi tai mata fada,budar bakinta sai cewa tayi itafa baza ta zauna da gurda gurda "yan mata gida daya ba batare da ta more su ba idan baya so ta daura musu tallata to yayi musu Aure, Dake Tanko Jan wuya ne a gidanshi ,ya tsawar mata ,yace "gidansa takyale masa yara suyi karatu ,tukkuna idan Miji ya fito ai za'ai musu Auran. Lantana taqi ji ,Tanko yana sa kafa yana fita zata fafaki yaran da faratin tallah ,suna kuka suke tafiya, Karshe Suka yanke shawarar guduwa gurin Uwarsu, Aiko ranar da Asubah suka fito dukkaninsu suna labewa suna jiran babansu ya fita sallah su gudu Tanko ya fito kamar yadda ya saba ,ya tsaya shagon su Sallau ,domin tashinsu ,suje massalaci ,daga bakin kofa ya tsaya gami da bubbuga kyauran ,ya wucewarsa Su sallau ko sunajinsa ,da suka fahimci ya kauce daga gurin sai suka cigaba da baccinsu ,dakin sai tsami ne yake tashi ,sabida ,dama bawata tsaftace dasu ba ,sai su fi sati basiyi wanka ba. Su Atika kuwa bayan sun tabbatar da wucewar babansu ,sai suka fito sadaf sadaf zasu gudu. Abin Mamaki ! Sukayi gware da Tanko ya dawo domin daukar chazbah , Sai ya kara haske fitilar dake hannunsa yana kallonsu daya bayan daya,ga Atika riqe da katuwar jaka. Yace"INA zakuje ne"? Sai suka fashe da kuka dikanninsu , Kukan da yayi sanadiyar Farkawar Lantana daga Barci duk da tana cikin Uwar dakinta, Tafito da sauri jin kukan da soro ,tana Addu'a Allah yasa ba daya daga cikin "yayanta bane ya mutu ,kanta ko Dan kwali babu. Me za ta gani su Atika ne tsaye riqe da jaka suna zabga kuka ,ga babansu a tsay" Tace"Malam Lafiya dai in ce ko "? Wa"yan nan shashashan yaran sun tashe ni daga bacci" Ko sauraronta bai yi ba ,ya cigaba da tambayar su Atika ina zasuje da Asubar nan. Atika tace "babah mungaji da Azabar da ake gana mana ,zamu tafi gurin babarmu, Lantana tayi salati kamar gaske tace"Au!sharri zaku kullamin gurin Ubanku "ooo ! Ni Lantana Na hadu da "yayan zamani, Sai ta hau kwala Sallau kira. "Sallau" Sallaau!! Sallau"!! *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108