Skip to content

Chapter 46

Chapter 46

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,229 words 0 views Progress saved
Download Book

bace, ni ne wan mahaifin ta, na santa ciki da waje jiya nan ta yankewa d'an uwanta ya tsa da wuk'a, sabuda haka in mata yake so yazo zan bashi d'aya daga cikin "yayana masu hankali da tarbiya" Yafi minti biyar yana nazarin maganganun da Sallau ya fad'a masa, daga bisani yace"shikkenan dama abunda ya kawo ni kenan" Sallau yace"to madallah, ka gayawa Abokinka cewar yazo ya duba d'aya daga cikin "yayana zan bashi, amma ya rabo da wannan yarinyar,in ba haka ba sai ta kashe shi" Sarki! yace"za'afad'a masa, hannu ya zura cikin aljihun jins d'in dake jikinsa ya ciro kud'i kimanin dubo goma ya mik'a masa, jiki na kyarma! ya warce kamar zai had'a da hannusa, saura k'adan ya tsuguna sabuda tsabar godiya da rawar jiki, nan Sarki! ya wuce ya barshi yana sambatu daf, da zai futa daga lungun sukayi karo da Balaraba, fad'uwa ta kusa yi yayi saurin rik'o hannuta, yana kallonta ta cikim gilashin dake idonsa, kallon kallo sukeyi da ita, fuskarta a had'e ta fuzge hannunta tana hararasa, tare da zabga tsaki tayi gaba, ji yayi bazai iya jurewa ba yasa ya tarota ta hanyar fuzgota ta dawo gabanshi, ya rik'e mata kafad'u da duk hannuwan shi sannan ya mannata da bango fuskarsa daf da tata yace"wai ke dame kike tak'ama ne, mara kunya, dan ma kin samu zaki fad'i na taimake ki shine zakiyi min tsaki" a tsiwan ce tace"anyi maka d'i... bata karasa ba ya rik'e bakin da ya tsunsa biyu ya murd'e leb'ubunan fuskarshi babu walwala yace"wai me kike da suna"? Balaraba kome? d'azu kafin ki futa kin min tsak'i yanzu ma haka, daga kawai an miki tambaya, zakina wa mutane, tsaki, wai ke kina tak'ama da kyau,ko dame kike tak'ama ne"? yafad'a yana zura hannun shi ta bayanta in da ya shafo tudun mazaunan ta a hannunsa, cikin sigar duniyan ci, yace "ko da wannan kike tak'ama ne"? Zabura! Balaraba tayi tana mutso-mutso, gashi har yanzu bai sakar mata baki ba, wani munafukin murmushi ya saki, yace" yarinya ko dame kike tak'ama bai dame ni ba, babu abunki wanda zai rud'ani kamar yadda yake rud'a wasu mazan, yanzu "yar uwarki tafad'a min wai inyi taka tsan-tsan dake, bata sani ba ni ko a k'afa aka d'aura min ke sai na kwance,na gudu" yana gama fad'ar maganarshi ya sake tayi taga-taga zata fad'i sabuda rashin k'arfin jiki, shi kuma kamar walkiya ya b'ace daga gurin. Kamar ta d'ora hannu aka haka takejin wani mugun d'aci a zuciyar ta, gabanta ne ya fad'i lokacin da ta tuno muryarsa sai taji kamar tasan mai irinta, tsugunawa tayi a gurin tana cusa fuskarta tsakanin k'afafunta tafashe da kuka wurjanjan! babban bak'in cikinta yadda wannan guy d'in ya samu nasara a kanta, gashi ta kasa gane fuskarsa duk da haske futula, tunda take a duniya babu namiji da ya tab'a kusantar ta kamar haka,sai shi har yayi nasarar tab'a mata jiki, bayan shi sai Sarki! ranar da suka zo tare da Moddibo, shima kuma bai yi a banza ba sai ta d'auki fansar abunda yayi mata, ta dad'e tana kuka a tsugune a gurun, daga bisani ta mik'e ta shiga gida, duk suna zaune a tsakar gida Sallau yana mayar musu da magana abunda ya faru, amma k'iri-k'iri yak'i futo da k'udin, tanaji Uwa! tana cewa"ai yadda Shamsiyya take f'adamin mutumin da yazo yayi mata, sabuda haka ko ya sake dawo wa ka had'ashi da ita kawai, amma me za'ayi da waccan mutsiyaciyar yarinyar, nan sukai ta zagin Balaraba, gami da mata mugun baki, duk tana jinsu a d'aki, abunda ya hanata kwana a gidan da ta kama haya shine, babu fenti babu shara, yanzu futar da tayi ma kenan, domin tasa yara su share mata gidan, tunda anyi fenti da yamma, haka ta kwanta tasa su Sadiya da Usuman a gaba tana kuka tunda take bata tab'a kukan maraici ba sai yau *Comeent Vote and Share* [21/07, 06:17] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^° _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®{REAL BINTU BATULA}👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{RAHAMA ALIYU}``` _ZAMANI WRITES_ _ASSOCIATION_🤝🏻 ```Bisimillahir-rahamanir-rashim``` *🅿55* Da wuri ta tashi tayi shirye-shiryen ta, tsaf ta shiryasu Usuman cikin kayan makaranta, ta had'a musu shayi, suka sha, itama ta had'a tasha, tana zaune gefan katifa, wayarta tafara k'ara tana dubawa taga Moddibo ne, sai ta kusa katsewa ta d'auka, ajiyar zuciya taji yana saukewa,sai ya bata tausayi , sallama tayi cikin muryar ta mai dad'in sauraro, yace"Gimbiya kin tashi lafiya"? "Lafiya k'alau, kai fa"? " Nima k'alau na tashi, jiya nai ta kiran wayar ki tun safe a kashe, gashi baki futo kasuwa ba" Cikin nutsuwa tace"wallahi kuwa na kashe ne sabuda ina da uziri,nagode sosai" " Wane uziri ne wannan, da alama kina cikin damuwa" yafad'a da cikin tausayin ta gami da so da k'auna A jiyar zuciya ta sauke, tace" yanzu zan fito zan kira sai muhad'u domin maganar ta wuce a fad'eta a waya" "Ok toum in sha Allahu yanzu zan futo sai mu had'u, amma kicire damuwar komai a ranka kinji ko" K'walla da take k'okarin zubo mata take k'okarin mayarwa tace" nagode Yusuf sai mun had'u" kashe wayar tayi ta aje gefan katifa, ta cigaba da kurb'ar ruwan shayin ta, sha takeyi kawai amma zuciyarta babu dad'i,, tana jiyo hayaniyar mutan gidan a tsakar gida,, Uwa sai cinikin awara take babu abunda ya dameta A nutse ta futo daga d'aki nta ta jawo k'ofar gami da sanya mata kwad'o, Lantana na tsaye bakin k'ofar futa hannunta rik'e da wani k'aramin buhu da alama kasuwa zata shiga, wani kallon banza ta watsawa Balaraba, ta ci gaba da magana da Uwa! dake zaune a kujera "yar tsugono tana faman soyawa a wara, gaishe su tayi, suka k'i amsa wa, tace" Matar Kawu Ina antashi lafiya"? Sadiya dake sunkuye tana wanki bakin rijiya tace"lafiya lou Balaraba,kin futo"? "Eh matar Kawu" Balaraba tafad'a tana k'okarin barin gurin. "Allah ya bada sa'a" Matar Kawu tafad'a ta cigaba da wankin ta. "Ameen" Balaraba tafad'a ta nufi kofar d'akin Iya. Iya jiki yayi sauk'i suka gaisa a gurguje, ta aje mata kular abuncin su Sadiya tayi mata sallama ta futa. Ashiru yana cikin Napep yana jiran futowar ta, dan haka tana shiga suka gaisa, cikin mutumci yaja Napep din suka bar Unguwar. Daf da zasu shiga kasuwar wayar ta tayi kara, tana dubawa taga Modibbo ne, d'aga wa tayi tace" Ina titin jark'asa yanzu, zan tsaya dai-dai masu sai da lemo da a yaba sai kasame ni a nan" "Ok gani nan zuwa" Moddibo ya fad'a gami da kashe wayar. Futa tayi daga Napep d'in ta sallami Ashiru, Nik'ab d'inta ta futo dashi ta sakaye fuskar ta,sabuda zurga-zurgar jama'a duk da safiya ce, ko minti goma batayi ba, taga wata mota mai kyau tayi parking a gabanta, d'auke kai tayi domin tasan ba motar Moddibo bace, futowa yayi yana murmushi, yace"Gimbiya wannan shan k'amshin naki yana burge ni, gaskiya dole maza su dunga jin shakkar ki" jin muryarsa yasa ta waigo da murmushi a fuskarta tace"barka da zuwa" "Barka kadai Gimbiya,shigo mota mana" yafad'a yana bud'e mata k'ofar motar, tunda take bata tab'a shiga motarsa ba sai yau, sabuda haka a nutse ta

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108