Skip to content

Chapter 44

Chapter 44

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,227 words 0 views Progress saved
Download Book

yayi yace"gaskiya Mama yarinyar nan tana da fada! a gurinku, ke da Maimarta ba, shima lokaci guda ya amunce da maganar, ni kam banawa Moddibo sha'awar auran yarinyar" Da murmushi a fuskar ta tace"D'a duk na kowa ne, kai dai kayi masa fatan alkairi kawai" "To me nace yanzu, tunda yaji ya gani yana son ta a haka, Allah ya sanya alkairi" "Ameen, abunda zakace kenan" Hira sukayi irin ta tsakanin d'a da uwa sannan yayi mata sallama ya futa, ***** Karf'e takwas da rabi na dare, ya shirya tsaf cikin k'ananun kaya, riga da wandon jins, masu kyau ya sanya farin galashi a idonshi, sai a gogo daya d'aura a hannushi na silvar ya tsunsa uku sanya da wasu manya-manya azurfa masu kyau da tambari irin na sarauta, wani bak'in takalmi ya sanya a kafarshi mai kyau da tsada, yayi wani mugun kyau sosai, duk wanda ya ganshi bazai gane Sarki! bane sabuda yadda k'uruciyar shi ta futo sosai d'an gemunshi ya kwanta yayi luf a fuskar shi sai shek'i yakeyi, babu wanda zai ganshi yace, shine sai wanda yayi masa farin sani, Turaranshi ya fesa wanda yake amfani dashi me suna (pure love) nan take d'akin ya d'ume gurin da k'amshi a nutse ya futa. Buba Direba na jingine jikin mota, Sarki! ya futo sai yayi sauri ya b'ude masa motar tun kafin ya karaso, Cikin yanayin muryar shi yace"Malam buba, ba da wannan motar zamu futa ba" "Allah ya taimake ka, da wacce zamu futa"? Wata bak'ar toyota ya nuna masa da hannunsa yace" muje a waccan" Da sauri Buba Direba ya nufi inda motar take, yana buge ta, duk da tsaf take babu wata kurar arzki a jikinta nan ya bud'e masa ya shiga ya zauna cikin nutsuwa Buba yaja motar suka futa daga gidan. *Comment* *Vote and Share* [18/07, 20:08] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^° _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®{REAL BINTU BATULA}👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{RAHAMA ALIYU}``` _ZAMANI WRITES_ _ASSOCIATION_🤝🏻 ```Bisimillahir-rahamanir-rashim``` *🅿53* Sai bayan sun futa daga gidan ne, Buba ya d'an waiwayo A hankali yana kallon Sarki! dake kishin gid'e a bayan motar,yace"Allah ya taimake ka,ina muka nufa ne"? A nutse yace"muje wannan unguwar da mukaje tare da Moddibo kwana uku da suka wuce, Maimartaba ya umarce ni da bunkicen wani abu" "To masha Allah ranka ya dad'e Allah ya bada sa'a" Buba ya fad'a yana cigaba da tuk'in mota, a nutse. Yau da wutar nepa a unguwar sabuda haka ko ina da akwai haske tar, can gefe guda Buba yayi parking din motar, yace"Yallab'ai gamu munzo" A nutse ya dago kanshi yana bin gurin da kallo, wasu gugun! matasa ya hango sunfi su a shirin a bakin wani kanti, wasu na shan rake wasu na cin gyad'a mai b'awo, yayin da wasu suke cikin a wara, a wata k'atuwar takkada, sai hira ake suna dariya, cike da rashin kamun kai, ya dad'e yana nazirinsu, kafin ya bud'e mota ya futo a nutse, ya gyara zaman gilashin dake fuskarsa, Buba yayi saurin futowa shima, a nutse ya kalleshi yace"ka koma ka zauna cikin mota,Buba bana buk'atar rakiya" Hannu ya d'aga alamun jinjija yace"a futo lafiya, ranka ya dad'e" ya koma cikin mota kamar yadda a ka umarce shi, A hankali ya rik'a tsallake kwatoci masu d'auke da dagwalo na k'azanta, har ya k'arasa gurin wad'an nan matasan. "Assalamu alaikum" sallama ya fara yi musu, cikin muryarshi mai dad'in sauraro. Hannu ya mik'a wa na kusa dashi yace"barka da dare abokina" "Barka kadai" Salihu ya fad'a lokacin da yake mik'a masa hannun sukai gaisa, wani irin taushi yaji lokacin da hannusa ya had'u dana Sarki! da sauri ya d'ago kanshi yana kallon fuskar Sarki! gefe guda kuma wani mugun k'amshi ne ya cika musu hanci, shiyasa duk sukayi d'if! suka bar hayaniyar da suke suna kallo Sarki! dake tsaye,hannusa cikin na Salihu, Gyaran murya yayi yace"Abokina in babu damuwa ina son in maka wasu tambayoyi" Duk da Sarki! yayi basaja,domin kar a ganeshi, amma muryarshi taso ta tona masa asiri sabuda duk wanda yake cikin garin har in yana sauraron kafofin sadarwa,to muryarshi ba b'oyayyi b'ace mussaman da azimi,da lokacin aikin hajji, akwai wani Maudi'i yake gabatarwa na addini wanda kafafan sadarwa suke sawa kullum, wannan Maudi'i kuwa shi kad'ai yake gabatar dashi sai dai kawai, a tura shi Media, shiyasa Salihu ya furgita jin kamar Muryar Sarki! magajin Sarki, yace"babu komai in sha Allahu zan baka amsar abunda zaka tambaye ni mutukar na sani" Fuskarshi a sake yace"muje can gurin maganar sirri ce" Jiki a sanyaye Salihu ya mik'e ya bi bayan Sarki! sauran abokanshi suka bisu da kallo cikin mamaki, Kai! wannan guy, d'in me ya kawoshi gurin Salihu, Allah yasa dai ba wani abun ya jawowa kansa ba" Maganar daya daga cikin matasan dake gurin kenan, "To wa yasa ni mudai babu ruwan mu" na kusa dashi yafad'a ya cigaba da shan raken sa. Can wani gefe suka tsaya,wanda yake da k'arancin haske, A nutse Sarki! ya kalli Salihu yace"Abokina kasan wata yarinya Balaraba a nan unguwar"? Shiru yayi na tsawan minti biyu yana tunani can yace"Eh na san wata a can lungun take" yafad'a yana nuna lungun gidansu Balaraba, ya cigaba da cewa, "amma gaskiya ba a fiye kiran ta da sunan ba sai a gidan su mu dai matasa muna kiranta da Gimbiya sabuda girman kanta, gashi ita ba " yar kowan kowa ba, a na tunanin ma Uwar da ta haifi baban ta Mayya ce" Shiru Sarki! yayi yana nazarin maganar yaron, daga bisani yace" kasan gidan nasu ne,inaso ka rakani gurin baban ta" "Nasan gidan mana" Salihu yafad'a ya cigaba da cewa"k'anin ta Walidi abokina ne, Allah yasa kai ma ba wani abun tayi maka ba, dan jiya ma wanta Iro ta cirewa d'an yatsa guda, yanzu haka yana can kwance yana jinya" Cikin mamaki Sarki! yace" garin yaya mace kamar wannan zata cirewa saurayi kamar ka d'an yatsa guda, dame ta cire masa"? "Humm Wannan yarinyar ai inda kasan " yar daba haka take, da wuk'a take yawo, mu dai inda mukaji wai tana so shi yayan nata yayi lalata da ita dama kuma shine zai aure ta, shine da yak'i amuncewa ta futo da wuk'a ta yanke shi, muje in raka ka kaji a bakin mutan gidan nasu" Cikin mamaki Sarki! yake bin bayan Sallau, yana al'ajibin abunda Salihu ya fad'a masa yanzu al'amarin yarinyar har ya kai haka Yayi mamaki sosai da inda yaga yarinyar take rayuwa a rin wannan lugun mai tattare da k'azanta da bola amma take wa mutane kallon banza, Shamsiyya na zaune a kujera "yar tsuguno tana lissafa cinikin a wara, ta bisu da kallo, da Sauri Sarki! ya dauke kanshi zuciyar shi na wani irin tashi, sabuda kauri gami da zarnin futsari da warin bola da ya cika masa hanci, hankici ya futo da shi yana d'an goge fuskarsa cikin basarwa, Salihu ya k'arasa kusa da ita yace" Shamsiyya babanku yana nan"? "Bayanan menene"? tafad'a kai tsaye "Dama wannan guy din ne yake neman shi" Da sauri ta mik'e ta karasa kusa da Sarki! cikin kwarkwasa tace"sannu ina wuni"? Dauke kai yayi da sauri, sabuda wani irin k'auri da yaji

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108