Skip to content

Chapter 20

Chapter 20

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,226 words 0 views Progress saved
Download Book

ruwana" Shiru tayi tana nazarin maganarahi, tasan Yaron ta da tunani da hangen nesa yana da nutsuwa, nutsuwarshi ce ma tasa Maimarta ba ba ya zartar da wani abu da ya shafe shi ko na menene sai ya nemi shawarar dan nasa Cikin nutsuwa tace" duk na fahimci abunda kake nufi, ina so ka yi min biyyaya da dukkanin abinda na umarceka dashi, sabida kasan halin yadda nake rayuwa cikin kishiyoyina, da sauran matayen waziran Mahaifinka, mutukar kaki yadda da wannan abu to babu shakka zasuce nice na hanaka auran "yar uwarka, kasan halin mahaifin ka shi babu ruwanshi da kananun maganganu na gidan nan, sabida haka nake neman alfarma a gurinka ka daure ka aureta, na san yadda kake a tsaye duk fitinar Halisa sai tayi laushi, sabida nasan baza ka yadda da shirme ba" Ummi ta karashe maganar tana sauke a jiyar zuciya Shiru dakin yayi na tsawon minti biyu sannan yayi gyaran Murya yace" Ummi na amince da abinda kika umarce ni, zan auri Halisa domin in faranta miki rai, amma kin san ba zan yadda da kananun maganganu na cikin gidan nan ba, za'ayi rigima dani, mutukar naji wata magana ta biyo ba,domin ba zan lamunci wani ya zage min ke ba rayukan zasu baci, maganar Halisa ce, na kuma amince zan aureta shikkenan sai su bar maganar" *Yanzu muka fara* [26/06, 22:19] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† _*GIMBIYA BALARABA*_ βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» _*Na*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` Zamani Writes Association🀝🏻 ```Bisimillahir rahamanir rahim``` *πŸ…Ώ32* ______Cikin nutsuwa Ummi tace"alhmdulilahi in sha Allahu babu abinda zai biyo baya sai alkairi,sai dai ina san ka rage zakin zuciyar nan taka kuma ka din ga fitowa cikin jama'a kwata-kwata kwana kwana biyu na lura baka zaman fada ko zaka iya fadamin dalili"? Yafi minti uku baice komai ba daga bisani ya dago kanshi yana kallon mahaifiyarshi yace"Ummi kin san halina bana ganin ana yin ba dai-dai ba in yi shiru duk ranar da mai martaba bai fita fada ba in ya wakiltani na lura su galadima basa su mussaman Baba waziri,Ummi su mulki ya dama sam ni bana sha'awar shi zaman fadar ma dan dai Mai martaba yana so ne,shine dalilin da ya sa kawai bana son zama sabuda zakiga suna yin abunda bai dace ba, kuma ba'a isa ai magana ba" Shiru Fulani tayi tana nazarin maganar dan nata tasan a kwai badakala a cikin gidan duk ranar da Mai martaba ya fadi ya mutu,domin dukkaninsu abinda suke wa kenan mulki, shiyasa suka tsaneta in banda tana da karfin arziki a gidan da tuni sun koreta babu irin jifan da basa mata tunda suka lura tana da ciki shikkenan ko wanne ya tashi hankalinsa, kishiyoyinta tamkar su mutu Asiri ko ta ina,in da Allah ya taimaka itama ba a kwance take ba maca ce mai addini da addu'a shiyasa duk asirinsu baya kamata ko ya kamata bayayin wani tasiri yake karyewa, a taikaice dai sai da cikin Almansor ya kai wata goma da wata goma sanan ta haifeshi lafiya sumul gida ya kace me da murna,da hayaniya sarki Almustap ya haifi da namiji kasancewar duk "yayanshi mata ne su goma sha uku uwargidanshi kawai ta haifi " yaya maza uku, kuma suka dinga mutuwa daya bayan daya, shine malamin ta yace mata kishiyar ta ce take kashe matasu sabuda tana so ta haifi danta wanda take so ya gaji kujerar mahaifiyarshi dole sai ta tashi tsaye, nan ta daga hankalinta ta dinga kiran malamai gami da "yan bori suna mata aiki a gidan, a kan duk dan da Mai martaba zai haifa in dai namiji ne to kawai ya mutu tun kafin yazo duniya,sosai take aiki da aljanu a gidan duk dan kar wata tazo ta haifi da namiji Abin da bata sani ba shine sauran "yan uwan Maimartaba Almustapah basa so ya haifi da namiji sabuda gudun kar mulki ya koma hannunsa bayan babu shi. Babu irin abinda basa yi na shirka domin ganin bayan Sarki dan su samu damar hayewa kujerar mulki Fulani ita ce matar maimartaba ta uku lokacin da sarki ya aure ta sai a ka dinga surutai cewar ya auri " yar malaminshi kuma ba "yar sarauta ba ce, nan kishiyoyin ta suka sanya ta a gaba lokacin tana bata da shekaru da yawa batafi shekara sha uku ba, da yake yarinya ce mai hankali sam bata musu rashin kunya in suna zaginta sai dai ta shige gurinta tayi kuka ta gayawa Allah damuwarta, kusan shekarar ta goma sha biyar a gidan,sannan Allah ya bata ciki da yake doguwar maca ce sai cikin ya boya in banda Maimartaba babu wanda ya sani a cikin gidan,sai ko jakadiyar ta mai suna Shafa'atu da yake ita take hidima da ita, Cikin ikon Allah da lokacin haihuwa yazo ta haihu lafiya babu matsalar komai.Jakadiya Shafa'atu ce ta gyara jariri tsab ta kwantar dashi a wani kayataccan gado mai kyau irin na yara,sannan tazo ta taimakawa mejego itama ta shirya tamkar ba itace ta haihu ba, Nan ta zube a gabanta tanayi mata sannu tace" ranki ya dade ki fadi abinda kike bukatar ci yanzu sai a kawo miki,sai ki kwanta ki huta" Fulani ta sauke ajiyar zuciya kana kallonta kasan tana da damuwa tace"bana bukatar komai yanzu kawai kije fada ki kira min maimartaba" Da sauri ta mike ta fita daga dakin domin cika umarnin da a ka bata, Lokacin da ta isa fada cike take duk su Waziri Zayyanu da Galadima da Wamabai hade da dakatai duk suna gaban sarki a gurfa ne, ta karasa taje ta kwashi gaisuwa,sannan ta isar da sakon Uwar dakinta nan fada tayi shiru kowa yana mamaki yarinya karama zata aiko kiran sarki,kowa jira yake yaga zai je ko bazai je ba, abin mamaki! maimartaba ya mike a nutse ya kalli mutanan gurin yace"zan shiga in fito yanzu a cigaba da tattauna maganar da muke kai insha Allahu in nadawo za'mu samu mafita" yana gama fadar maganarshi ya wuce wasu dogarawa uku suka bi bayanshi suna baza babbar riga,tare da fadi takawar lafiya gaba salamun baya salamun Sarki mai adalci a fito lafiya, Jakadiya Shafa'atu ta bi bayasu itama tana nata kirarin. Nan baki kofa suka tsaya bayan Maimartaba ya shiga bangaran Fulani Tana zaune ita kadai tana tunanin irin rikicin da zai tashi mutukar mutanan gida suka ji cewar ta haihu kuma da namiji wadanda basu san sa zaman cikin ba ma cewa zasuyi karya ne,ita tsoranta kar taje a sabauta mata yaro Maimartaba yayi mamaki ganin ta tsaf tamkar bata haihu ba.Sannan ga yaronsa mai kama dashi mutuka tamkar an tsaga kara, a hannuta tana shayar dashi, sai ya karasa kusa da ita da sauri fuskarsa dauke da murmushi yace" Fulani mai halin manya mace ma kara da kawaici da kunya,yau na kara tabbatar wa cewa ke alkairi ce a gare ni" A nutse ta mika masa jinjirin tana murmushi tace"gaskiya naji dadin wannan yabon da kayi min, yau Allah ya sauke ni lafiya kaga bawar da Allah yayi mana" Hannu biyu yasa ya karbi jariri cikin farin ciki yace"masha Allah dukan godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki da yayi min wannan bai wa Allah shine abin godiya" Kunneshi ya kara

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108