Chapter 28
Chapter 28
wani abu, ni Sunana Balaraba Ayuba Tanko kamar yadda kasani, kana ji na ko"? tafada tana hura hanci, kana ta cigaba da cewa, "kai kuma in har ban mance ba Kai ne Almansor Sarki! dan Sarkin Almustapah, hakane ko ba haka ba"? tafada cikin sigar tambaya gashi ta tsare shi da ido, tana tsaye babu fargabar komai a tattare da ita, Cikin jarumta tacigaba da cewa" Wallahi baka isa kazo har kofar gidanmu ka ci mun mutumci ba, domin ni bani na kira ka ba" Tsit!!!! gurin yayi Maddibo yana mamakin jarumta irin ta Balaraba,ko shi da yake Namiji bazai iya tsayawa gaban Almansor har ya gaya masa magana irin wannan ba, sabuda kwarjinin da Allah yayi masa. A tsanake ya dago kanshi fuskarshi a murtuke, ko da wasa bai kalli inda take tsaye ba, murya a cunkushe yace"in kagama abunda kake kashigo mutafi,in kuma baka gama ba zan wuce kawai, sai katawo" "Wai me yake Faruwa ne,? tsakaninku naga kamar a kwai abunda kuke boya min, gaskiya banji dadin irin yadda kuka gaisa da junanku ba, abun bai min dadi ba" Maddibo ya fada yana kallon Balaraba, Murmushi tayi mai cike da takaici tace"Yusuf abokinka dan rainin hankali ne, wallahi ni kuma kasan bana daukar raini, ni "yar talaka ce, amma ban nema gurin wani ba sabuda haka babu mutumin da ya isa ya zage ni ban rama ba" A fusace!Sarki ya bude murfin motar Balaraba na tsaye jiki tayi taga-taga kamar zata fadi,cikin tsoro ta matsa gefe,gabanta yana dukan uku-uku, duk da cewar babu wadataccan haske a gurin sai hasken farin wata, hakan bai hanata hango tsantsan bacin rai a fuskarsa ba, ganin fitowarsa yasa Buba Direba dake can gefe a tsaya yayi saurin karaso gurin yana baza babbar riga, ya na zuwa ya zube a gurin gami da dunkule hannunsa alamun jin jina, yace"ranka shi dade, a kwai abunda za'ai maka ne" Cikin wani irin murya yace"Babu abunda za'ayi Buba koma inda kake" Buba ya mike da sauri, kanshi a kasa yace"Allah shi taimaki Yarima Sarki Allah ya ja Zamanin ka" Da Sauri Balaraba ta dauke kanta, ganin ya maido da hankalinshi kanta, ya zuba mata ido, kawai yana kallo, Lokaci guda ta nemi nutsuwar ta tarasa jikinta yayi mugun sanyi, ganin shi tayi yana matsowa kusa da ita a hankali, fuskarshi a murtuke! jinsa daf da ita yasa ta jingina da jikin motar a karo na biyu, kamshin turaransa duk yq cika mata hanci, sai sa ya tsaya daf da ita sosai har numfashinsu yana haduwa, sannan ya kafe ta da idanunsa masu tsananin kaifi,da kassara jikin duk wata "ya mace me ji da kanta A nutse a bude bakinsa yace" Duk abunda kikayi a yanzu, bazan yi mamaki ba sabuda nasan zakiyi abunda yafi haka" Wani irin kamshi taji yana futa daga bakinshi, lokacin da yake mata magana, kanta ta sunkuyar kasa kagabanta na lugede tunda take, babu wani da Namiji da ya taba kusantar ta kamar haka, kokari kawai take ta kwaci kanta, amma babu hali,sabuda yadda ya yi bake-bake a gurin,duk tsahonta ya rufe ta. Yayi tsawan Minti biyu kafin ya kara cewa komai kana ya cigaba da cewa" Babu mamaki duba da yanayin unguwar da kika taso a ciki, babu abunda yake damunki sai tsan-tsan jahilci, da gidadan ci , da Zama cikin maza, a cikin kasuwa, shashashar yarinya kawai, zan koya miki hankali, zaki nuna min da me kike gadara, da kikewa kanki kallon ke wata aba ce" Yana gama fadin wannan maganar ya tattaro miyau, a bakinshi ya dai-dai ci fuskarta ya tofa mata, ya dora mata da wani banzan kallo yace"ina sauraron ki da duk hukuncin da zaki dauka a kaina" *Comment* *Vote and Share* [06/07, 13:37] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ» ββββββ _*GIMBIYA BALARABA*_ ββββββ πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ» _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *MARUBCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*Zamani Writes Association*_π€π» ```Bisimillahir-rahamanir-rahim``` *Real Bintu Batulaπ* *π Ώ39* Hannu kawai ya dagawa Buba Dreba da sauri ya karaso gurin, Cikin nutsuwa ya mai da idonshi kan Maddibo yace"Ni zan wuce, naga alamar baka da ranar tafiya, ka kawoni gurin yarinyar mara tarbiyya tana neman ta zageni" Cikin daga murya Balaraba tace,"to in na zageka me zaka yimin karkari kasa a daure ni to ka dade baka sa an daureni ba,kuma zakasan wanda ka tofawa miyau dinka,wallahi sai na rama kaji na rantse" Cikin hayaniya take fadar maganar,hawaye yana kokarin zubo mata, Babu zato taji wani sabon yawu a fuskarta ya kara tofa mata a karo na biyu, baice komai ba ya shige mota Buba Direba ya shiga ya kunna mota suka bace daga gurin. Maddibo kamar ya dora hannu aka domin takaici da Sarki! ya kunsa masa, ya dauko shi domin yazo ya gyara masa lamarinsa gurin Balaraba, yazo ya bata daya goma bata gyaru ba,yanzu yaya zaiyi? Cikin muguwar kunya gami da jin nauyi ya kalli Balaraba tana goge hawayen bak'in ciki,tana sane ta matse kukan batayi a gabansa ba,sabuda kar yaga gazawar ta, sai bayan ya tafi hawaye ya balle mata,kamar me tunda take a duniya babu mahalukin da ya taba yi mata tozarci irin na yau,dole ne ma sai ta rama wulakanci da mutumin nan yayi mata. "Kiyi hakuri dan girman Allah,Balaraba, hakan ba halinshi bane, dana san abunda zai faru a tsakanin ku da ban gayyato shi ba,dama da yaya ya yarda zaizo din,kiyi hakuri dole zan dauki mataki akan haka,sabuda ke kanki kiba da daraja da mukami cikin zuciyata" Fuskarta goge da hannuwanta duk biyun,fuskarta a hade tace" Ya kuke dashi,ma'ana menene alakar ka da gidan Sarki"? Tsayuwa ya gyara sosai yana fuskantar ta, yace"Ni Sunana Yusuf kamar yadda kika sani, amma Mutan gida na kirana da Maddibo asali sunan kakanmu a gare ni shiyasa suke kirana da haka, Sarki Almustaph Wan mahaifina ne, Waziru Zayyanu" Da sauri Balaraba ta dago kai tana kallonsa cikin mamaki! Ya cigaba da cewa"Sarki! Almansor dan Uwana ne na jini kuma aminina abokina tare mukai karatu dashi tare muke rufewa mu kashe, amma halin kowan daga cikinmu daban yake da na dan uwansa, yana da saukin kai sosai in ka fuskance ki, amma bashi da hakuri ko kadan in ka tabashi, Mugun muskiline,sosai shiyasa nayi mamakin abunda ya hadaku haka kuke fadawa junanku bak'aken maganganu, da alama s kwai abunda ya taba hadaku a baya" Shiru tayi na minti biyu ta kalleshi a nutse tace"kana kallonshi yayi min wulakanci har da tofa min miyau bakace komai ba, dama ka dauko shine domin yazo ya wulakantani ko, babu komai, Nagode" Tana gama fadar maganarta ta kama hanya ta barshi tsaye a gurin,tafiya take kamar zata kifa jin zuciyarta take kamar zata kone sabuda tsabar turiri da take mata, da kyar ta kai kanta gidansu, Maddibo ko binta da kallo yayi har ta bace masa, jikinsa a sanyaye ya futo da waya ya kira daya daga cikin Direbobin cikin gidan Maimartaba Sarki Almustaph ya fada masa unguwar da yake,yace yazo yanzu-yanzu ya dauke shi Yana nan a tsaye a gurin, Sallau Direba ya karaso gurin Lokacin goma da rabi na dare,da sauri ya bude motar ya fito ya budewa Maddibo ya shiga suka bar unguwar, Salihu Yana tukin mota yana mamakin me ya kawo Maddibo irin wannan unguwar, ya gaza hakuri ya yace"ranka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108