Skip to content

Chapter 65

Chapter 65

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,261 words 0 views Progress saved
Download Book

kazo ka aje amanar taka baka zuwa dubata haka ake rik'e amana" Sosa kai yayi irin na sabo yace"Afuwa Mama ni kaina bana cikin nutsuwa bani da lafiya" Me Martaba yace"Dole ne kayi Magajin Sarki wannan rayuwar bata da tabbas babu komai a cikinta sai rud'u da tashin hankali" Sarki!ya sauke ajiyar zuciya yace"Allah ka jik'an Moddibo" Tare suka amsa da "Ameen" Mik'ewa yayi yaje ya kwanta kan wata katuwar Sofa, ya lumshe idonsa wani irin bacci yake ji. Me Martaba yace"Yarinyar nan ai tana gurinki ko" Mama Fulani tace"Tana cikin d'aki ita da "yan uwanta,gaskiya ina tausayawa rayuwarsu wallahi" "Dole ai abun tausayi ne, shi yasa na yanke shawarar d'aura mata aure da Magajin Sarki tunda ta rasa miji me nagarta kamar Yusuf ina ganin shi Almustafa zai iya rik'eta amana" Murmushi Mama tayi cikin k'arfin hali tace"Wannan hukuncin naka yayi Allah ya tabbatar da alkairi, amma ina hasashen rigimar da zataje ta dawo kasan dai rigimar k'anwarku Madabo ko"? Me Martaba yayi gyaran murya a nutse yace"Barta wannan duk rigimar ta a bayan fage take kuma batayi a gabana sai bayan idona,na riga na yanke hukunci Almustafa zai Auri matar Yusuf Balaraba kenan zai kuma auri Halisa d'iyar k'anwata Madabo" Duk irin maganganun da suke wakana tsakanin iyayen nasa yana ji yayi lamfu, shi kad'ai yasan abunda yake sak'awa a zuciyarsa Bud'e ido yayi kad'an yana kallon iyayen nasa ya mik'e zaune, a nutse yace"Allah ya taimake ka maganar Azima fa" Shiru Martaba yayi daga bisani yace"Maganar Azima tananan itama za'ayi tunda an yiwa mahaifinta Alk'awari kar ka damu, Zamu aika masa da wasik'a cewar ranar juma'a me zuwa za'a d'aura auran sai su shigo da shirinsu insha Allahu zaka had'a mata uku rana d'aya ina maka addu'a da fatan alkairi,insha Allahu zaka samu nasara a rayuwarka" Godiya Sarki yayi yana girmama al'amarin mahaifin nasa,shi da kansa yake addu'ar Allah ya bashi ikon yin adalci tsakanin matansa, Me martaba yace"Kaje ka kiramin ita yarinyar,ina so mu zauna da ita gaka gata gani ga mahaifiyar ka, domin in fad'a mata irin hukuncin da na yanke a kanku, bazan yi mata dole ba, a rayuwarta" Mik'ewa yayi a nutse Mama tace"Tana cikin uwar d'aki takasa sakewa har yanzu" Kai tsaye d'akin ya nufa, yana taka k'asa kamar me tausayinta. [15/08, 05:41] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ ________________________ _*We are here to educate,motivate and entertain aur readers*_ ________________________ _*DIDEGATED*_ _*TO*_ ```RAHAMA ALIYU``` *🙆🏻‍♂🙆🏻‍♂BANI BANE🙆🏻‍♂🙆🏻‍♂* _(Zargina ake_) ~BY: MAMA QUEEN~ *💫DA BAZAR MU WRITER'S ASSOCIATION*💫 *NOTE* Wannan book yana kunshe da abubuwa kala-kala kama daga cin amana,sark'akiya,rikitarwa dad'i sauransu..... _Wannan yana da banbamci domin kuwa killatacce ne duk Wanda ke buk'ata se ya biyoni ta number kamar haka_ Whatsap numbar 07061553385 *Karku bari abaku labari* _*BISIMILHIR-RAHAMANIR-RAHIM*_ _*INA MIK'O GAISUWA TA GAMI DA FATAN ALKAIRI GARE KA*_ *_Adimin Haruna H Umar_* *_Beneficial writers fan's_* ```INA MAKA ADDU'A DA ALLAH YA BAKA MACE TA GARI🥰``` *🅿74* A nutse ya bud'e k'ofar ya shiga bakinsa d'auke da sallama. Wata irin fad'uwar gaba taji lokacin data tsinkayi muryarshi tana daga cikin toilet tana d'auro alwala, lokaci guda taji duk jikinta yayi sanyi wasu hawaye masu zafi suka fara zubuwa a idonta, cikin zuciyarta tace"Shikkenan yanzu zai zo ya dawo min da damuwa ta baya,wayyo Allan Moddibo, hawaye ne ya ke kwarara sosai a idonta mutuwar Moddibo ta dawo mata sabuwa dal!tunda taji muryar d'an uwansa Sarki!sai take ganin kamar zata ga Moddibo. Jikin bangon band'akin ta jin gina tana share hawaye sai k'okarin dai-dai ta kanta take, amma ina dole fuskarta ta nuna alamun anyi kuka. Murmushin k'asaita ya saki lokacin da suka had'a ido da Sadiya dake zaune kan gado,tana wasa da wasu awarwaron Balaraba da ta cire ta aje kan drowar duk wani kwalliye-kwalliye ta daina sai kace me takaba kullum da hijab a jikinta da carbi,kai hatta da d'an kunne ta cire ta aje,gani take itama rayuwarta tazo k'arshe babu Yusuf Moddibo rayuwarta ba zatayi dad'i ba. Da gudu Sadiya taje ta rungume shi tana dariya tace"Magajin Sarki!yau kwanana bakwai ban gan ka ba,wai ina ka shiga ne?ina Yusuf kullum yayarmu sai tayi kuka idan na tambayeta sai tace babu komai" Lokaci guda duk tayi masa wannan tambayoyin. Hannunta ya kama suka zauna cikin wata kujera ya d'ora Usuman a cinyarsa, yana shafa kan yaron cikin tausayi,yace"Na fuskanci Halimatu kina da surutu da yawa, Ok kina son in sanya ki a makaranta ko"? Cike da farin ciki ta d'aga kai, murmushi yayi kawai yana girgiza kai,yace"Kar ki damu insha'Allah a satin nan zaku fara zuwa school ke da d'an uwanki" Tsalle ta buga na murna cike da farin ciki tace "Mun gode Magajin Sarki,Allah yasa kazama Sarkin mu" Murmushi yake sosai yace"Ameen,in dai na zama Sarki kece Gimbiya ta" tsalle Sadiya take tana murna cike da k'uruciya Usuman sai taya ta yake, Wata tsawa taji wacce tasa tayi saurin shiga taitayin ta d'akin yayi shiru, Balaraba ce ta futo daga toilet taga shashancin da Sadiya take ranta ya b'aci sosai, ta lura shi kuma sai biye mata yake,tana jinta ko gaida shi batayi ba saboda rashin hankali. Fad'a sosai takewa yarinyar kamar zata kai mata duka Sadiya har ta soma hawaye, ganin hawayen ne yasa ransa ya b'aci ina dalili ita ba'a hakura mata ba,ita zata takurawa wata. Cikin wani irin voice me kashe jiki yace" Ya isa Malama" Kallonsa tayi ta gefen ido tayi saurin kauda kanta, kasa-k'asa tace da Sadiyar taje ta gaida shi, Simi-simi Sadiya taje ta tsuguna tana gaishe shi,ya amsa sama-sama suk hankalinsa na kan Balaraba dake k'okarin ta da sallah, Rarrashin Sadiya yake har Balaraba ta idar da sallahr ta d'an waigo kad'an bata yarda sun had'a ido ba tace"Ina wuni" Shiru yayi kawai yana rikitata da mayun idanunwansa masu sa kasala. Jin bai amsa ba, ta kara maimaita gaisuwar. Gyaran murya yayi a nutse yace"Lafiya, nake, yayi shiru na minti biyu kana ya cigaba da cewa"Me Martaba na neman ki yanzu" Cikin fad'uwar gaba ta mik'e tsaye da sauri har tana k'okarin faduwa ta dalilin dogon hijab din dake jikinta Bakinta na rawa tace"Allah yasa ba wani laifin nayi ba" Shiru yayi mata yana binta da kallo ganin jikinta na tawa. Had'e fuska yayi yace"Ji mana, kinga ki nutsu ba wani abun bane,naga kina ta wani rawar jiki, yawwa bayan nan kuma, Wad'an nan yaran da suke gaban ki ki bar ganin k'annan ki ne, to in kika cucesu sai Allah ya saka musu, na fad'a miki" Yana gama maganar sa ya mik'e ya futa a nutse, bai tsaya kallonta ba balle ya saurari abunda zata ce,ita kuwa binsa tayi da kallo har ya fuce tana mamakin yanda yake mata magana cikin isa!da gadara, lallai ruwa ya daki babban zakara, [16/08, 14:28] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ ________________________ _*We are here to educate,motivate and entertain aur readers*_ ________________________ _*DIDEGATED*_ _*TO*_ ```RAHAMA ALIYU``` *🙆🏻‍♂🙆🏻‍♂BANI BANE🙆🏻‍♂🙆🏻‍♂* _(Zargina ake_) ~BY: MAMA QUEEN~ *💫DA BAZAR MU WRITER'S ASSOCIATION*💫 *NOTE* Wannan book yana kunshe da abubuwa kala-kala kama daga cin amana,sark'akiya,rikitarwa dad'i sauransu.....

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108