Skip to content

Chapter 22

Chapter 22

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,269 words 0 views Progress saved
Download Book

tana da karzuwa ko karuwa ko kuma me zaman kanta,yarinya nutsatstsiya kamila, maitarbiya, sana'ar siyar da abinci da takeyi domin rufin asirin kanta ne sabuda na lura iyayenta basu wasu masu karfi bane, amma bari kaji duk izzar ka da takamar ka wannan yarinyar tafi ka, sabuda haka in kanaso mu shirya da kai kar ka kara ai bata min ita,sabuda zuciya ba zata iya jurewa ba" Dariya Sarki!ya kama yi masa ba yana nunashi da hannu yace"amma ka bani kunya wallahi,yanzu a kan "yar towo-towo kake wannan tada jijiyar wuyar"? Shareshi Maddibo yayi. Har yanzu da murmushi a fuskarsa yayi gyaran murya gami da kara gyara kwanciya cikin ginshera yace" zanso in ga wannan yarinyar, da dai ban yi niyyar zuwa ba amma ganin yadda ka hakikance a kanta yasa dole zanje na ganta,yanzu yaushe ka shirya tafiyar" Sakin fuska yayi ya juyo yana kallon Sa yace"ai a inda ke sakar kwata-kwata yarinyar taki amince min zuwa gidansu, yanzu ma da kyar na karbi numbar wayarta wallahi, amma dole insa a buncika min gidansu" Shiru Sarki!yayi yana nazarin maganarsa ji yake tamkar ya tsinka masa mari,sabuda yadda ya bashi haushi,gashi bashi da halin magana yanzu zai hayayyako masa da masifa ya lura abokin nasa ya yi nisa sosai kan son yarinyar,sai kawai ya masa shiru yana ji yana magana bai tan ka ba. "Kayi min shiru ina ta magana ni kadai" "Me kakeso in ce maka yanzu" yafada hankalinshi a kan wayarshi, ya cigaba da cewa "kace yarinyar taki baka dama kaga kenan bata son ka sabuda haka sai ka hakura kawai,domim wahalar da kanka zakayi gurin macan da bata son ka" Shiru Maddibo yayi yana jin tsoran fada masa maganar dake bakinsa,da kyar dai ya samu yace"abinda zamuyi kawai muje can gurin inda take sana'ar tata, kafin musamu gidan nasu" "Wannan ne kuma baza ayi dani ba,kome zakayi sai dai kayi,in ka damu ka sa a duba maka gidan iyayenta,ni kuma nayi maka alkwari zan maka jagora insha'Allah" ya karashe maganar batare da ya kalle shi ba "Ai kuwa dole gobe na me adress dinta ko ta halin kaka ne" Tabe baki yayi yace" yace mubar maganar haka, muyi wata wallahi raina baci yakeyi dan dai babu yadda zanyi da kai ne" Dole tasa Maddibo barin maganar badan zuciyarsa naso ba suka shiga wata hirar daban. Can wayar Sarki! ta yi kara,a nutse ya duba fuskar wayar,Halisa ce dauke kansa yayi daga kan wayar har ta katse, wani kiran yakara shigowa a karo na biyu,nan ma ta katse bai dauka ba, Maddibo yace"matsala ta da kai kenan sai ai ta kiranka a waya dan tsabar wulakaci kaki dagawa" A ya mutse yace"kasan ko wacece ne"? "Sai kafada" "Wannan shashashar yarinyar ce Halisa" Dariya Maddibo yasa yace"wai kai har yanzu baka sallama mata bane"? "Tsaki! yaja cikin damuwa yace" Zaman da ka ganni inayi gurin Ummi zancan take maimaita min wai dole sai na aureta,babu yadda na iya dole in yi musu biyyaya amma kai kanka kasan yarinyar bata burgeni sabuda dabi'unta duk babu masu kyau" "Addu'a zakayi kasan dole ne muyi wa iyayenmu biyayya kan dukkanin abun da zasu zo mana dashi mutukar bai sabawa shari'a ba , amma ina ganin zaka iya da ita duk taurin kanta,tunda na lura ta sonka da yaw........Kafin Maddibo ya rufe bakinshi daya daga cikin, bayin dake tsaye bakin kofar shiga falon yayi sallama,ya zube nan bakin kofa kai a kasa yace" ranka shidade Gimbiya Halisa ce tazo da jamar'arta" Shiru yayi kawai yana latse-latse a waya Maddibo yace"je ka shigo dasu" Da sauri ya mike gami da cewa"angama ranka shidade, Allah ya taimeka ,yanzu zan cika umarninka" ya fuce da sauri! Maddibo ya kalleshi a fakaice ya na kunshe dariya yace"kaga mutuniyar taka ko muna zan canta sai gata tazo,gashi bakace komai ba" Uffan! bai ce ba masa ba har Gimbiya Halisa suka shigo ita da masu take mata baya. *MUJE ZUWA* [29/06, 05:20] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† _*GIMBIYA BALARABA*_ βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» _*Na*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` Zamani Writes Association🀝🏻 ```Bisimillahir rahamanir rahim``` *πŸ…Ώ34* Cikin kasaita ta shigo falon kai tsaye in da yake zaune ta nufa,tana wata irin tafiya cike da izza da takama. Nan jama'arta suka zube bakin kofa suna kwasar gaisuwa,daga bisani suka fuce daya bayan daya, Wani irin zama tayi kan kujerar tamkar zata shige jikinshi tace"Yayana ya kake? kwana biyu duk kasa hankalina ya tashi in na kira wayarka sai kaki amsa min, kasan ko yadda na damu da kai kuwa" Fuskarshi a hade yace"ki matsa daga kusa dani mutukar kina so in saurare ki da abunda kikq zo dashi,kin san bana son wannan dabi'ar taki yana daya daga cikin abunda yasa sam ba kya burgeni" Jikinta a sanyaye tace"wai me yasa kake fadamin duk maganar da tazo bakinka,yanzu me ye laifin wanda yace yana sonka,kasan fa ban rasa masoya ba" Wani irin kallo yayi mata mai kama da harara cikin kasaita yace"ni ina ruwana da wasu masoyan ki kin san kina da masoyan zaki makale dole kice sai ni zaki aura,kije ki zabi daya daga cikin masoyan naki ki aura zai fi miki alkairi" Shiru tayi na minti biyu tana tunani tasan halinshi mugun dan wulakanci ne da girman kai,ya zama dole ta lallabashi tunda dai ita ke nema dole ta kwantar da kai har Allah yasa burinta ya cika. Kwantar da murya tayi tace"kayi hakuri insha Allah zan gyara,ni dai burina kawai ka dinga kulani kana daga waya ta idan na kira" Shareta yayi ya cigaba da duba wayarsa. Maddibo ta kalla tace"Ya Maddibo ka sanya baki mana wallahi ina jin tsoran wulakancin abokinka kullum da irin kalar da zai min gashi zuciya ta takasa hakura dashi." Cikin dariya Maddibo yace"kar ki damu insha'Allah komai zai wuce,amma dole kiyi hakuri da halinshi domin ba ke kadai yake wa,so tun yanzu ya kamata ki gane wane irin namiji zaki aura" Ajiyar ta sauke tace"bakaji yadda nakeji a cikin zuciya ta ba amma babu komai" Cikin dariya gami da barkwanci Maddibo ya kalli abokin nasa yace"mutumina kana ji fa ya kamata ka aje wayar nan ku fuskanci juna da mutuniyar kafin zuwan lokacin" Hankalinshi na kan wayar yace"ba kaji abunda tace min ba yanzu,wai tana da masoya,kajifa wani zance dan Allah, tasan tana da masoya me yasa ta nace min, "yar rainin hankali kawai" "Ni dai nace kayi hakuri" Halisa tafada muryar ta kasa kasa A ya mutse yace"in ban hakura dake ba yaya zanyi,ai dole ki kuyi iya magana,domin ni bana son shirme" "to zan koya in sha Allah" Nan dai ta lallabashi ya hakura suka cigaba da hira sama-sama, Maddibo yace"to ni zan wuce sai munyi magana a waya kafin gobe,insha Allah zan sa a duba min" "Allah ya kaimu" abinda yace kenan,Halisa tace"Ka gaida gida Maddibo a gaida su Mama" Sosai Halisa ta dinga jansa da hira, wani ya amsa wani ya share ta,to inda sabo ta saba da haka,cikin zuciyarta tace a juri zuwa rafi wataran tulu zai fashe,yanzu ni burina kawai in ga na mallaka duk wulakancin ka zan jure **** Maddibo da ne ga wazirin Sarki,inda Waziri ya kasance kani ga Maimarta ba Sarki Almustapah,Uwarsu daya ubansu daya, Waziri yana da "yaya goma

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108