Skip to content

Chapter 5

Chapter 5

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,207 words 0 views Progress saved
Download Book

Balaraba tace taci gaba dacewa Kawu Naji kayiwa babanmu Addu'a banda Mamana" Bata Fuska Kawu yayi yace "Allah yajikanta itama daga haka yaja bakinshi yayi shiru ita tarasa wace irin qiyyaya Kawu yakewa Mama ta duk da bata raye. Yace"ae sai mutafi ko gaskiya naji Farin ciki sosai Balaraba zakije Makka Aikin Hajji mu Na zaune, Dariya tayi tace "Kawu kenan kar kadamu Nabar maka kaje kai kawai Tafada babu damuwa tattare da'ita. Wani farin ciki ne ya ziyarce shi A zucci yace "ja'ira mai kama da tsohowar Karuwa ae ko baki bani ba baki isa kije Makka ba in dai INA raye a doran duniyar nan. A zahiri kuwa yariqa washe baki tamkar me sai shi mata Albarka yake kamar babu gobe. Jin shi kawai Balaraba takeyi domin tafi kowa sanin waye Kawu. Haka suka ran kaya suka nufi gida Kawu sai hirarraki yake mata Na babu gyara babu dalili. Wani gida Nafara hangowa cikin wani surqoqin lungu Wanda kwatoci sukayi wa yawa gasunan duk sun bi hanya babu kyawun gani gefe ga tarin bola da tarkace da wata tsiya ce yara duk sun Tara kayan gwangwan da Alama yaran Layin suna fita Sana'ar gwangwan domin ga Alamu nan tarin robobin qarafuna da buhunhuna. Haka sukai ta tsallake shirgin gurin Kafin su shiga cikin gidan da babu kofar arziqi duk ta lauye ko tsayuwa batayi da kafarta sai an kare da dotse ko kujera,Kawu sai zage zage take yi kafin ya shiga gidan fadi yake shegu tsinannu "yayan Allah bani duk sun zo sun cika mana layi da kayan sata "yan iskan yara kawai" Wani kallo Balaraba taiwa Kawun Mai kama da Harara tace"Haba Kawu wannan zage zagen bashi da Amfani Shiyasa suka rai naka ina ruwanka dasu ,sai La'antarsu kake yi ta'ina zasuyi Albarka kar ka Manta fa harda su Babaye da Walidi cikinsu shikkenan tunda ka hadasu ka zage babu ta yadda zasuyi Albarka ,Neman halak dinsu sukeyi yafi suje su dauki Na wani " ta qarashe maganar Cikin bacin rai! Gyaran Murya yayi ko kunya babu domin shi yanzu lallaba Balaraban yakeyi so yake ya kwace mata duk Abinda ta samu gurin saukar. Yace"Rabu dasu diyar Albarka kinji ko shige muje ciki Ae ke kaman Dan Uwana yayi sa'ar Haihuwa ba wa"yannan "yan iskan ba" Yaran dake gurin suka kwashe da dariya suna nunashi da hannu domin dai dama yaran duk sun rai nashi sakamakon zubar da Mutunchin shi da yakeyi gurin in sunje gwangwan dinsu sun dawo yabi yana kar6e musu kudi. Balaraba taja tsaki ta shige ta barshi gurin tace"ae kaga Abinda nake gudar maka nan gashinan sun mai da kai mahaukaci" Walidi ne yafito a guje su ka ci karo da Balaraba yayi mata wata bangaza tamkar zai yadda ita kasa,yayi gaba ko saurararta bai yi ba. Da sauri ta jawo hannunsa ta zabga Masa Marika hagu da dama tace" Dan Uwarka ni sa'arka ce zaka bangaje ni ka huce ko kallo ban isheka ba ko ka ga INA shiga sabgarku ne"? Kuka Walidi yafashe dashi yayi cikin gida da gudu yana cewa"Allah ya isa ban yafe ba Shegiya "yar Karuwa" Wani Bacin rai! Ya dirar wa Balaraba tayi cikin gidan A fusace yau sai taga da Wanda walidi yake taqama Lallai yau za'ayi rigima gidan nan domin tagaji da irin cin zarafin da yaran suke mata. Da sauri Kawu yabi bayansu yana zagin Walidi ta Uwa ta Uwa ba Uwa" Na zaune kan kujera "yar tsuguno tana wanki dake sana'ar tace kenan wankau Walidi ya shigo yana burara ihu tamkar Wanda a ka yanka ,Sai tambayarsa take menene da qyar yace waccan "yar karuwar ce ra mareni hagu da dama inaji ma ido na yafashe yafada tana rintse ido daya cikin sharri Cikin Sababi! Da tashin Hankali! Uwa ta Mike tana gyara daurin zaninta tace "Lallai Yau zaci kambu a gidan nan Wallahi tallahi bazan lamunci wata "yar iska ta riqa dakar Min "yaya ba bara ta shigo inji meye dalil......kafin ta karasa tajiyo Muryar Kawu yana ta Surfawa Walidi zagi! Abin Mamaki! *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š [04/05, 02:52] +234 808 996 5176: πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *✍🏻writting by* *Binta Umar* _*MAMAN ABUDL WAHABU*_ *MRS AHAMAD GWADABE* _*WANNAN BOOK DIN NA SIYARWA NE 200 IN KANA BUKATAR CIGABANSHI GA NUMBAR NAN*_ *πŸ…Ώ8* "Yau kuma da Abinda kashigo da shi kenan Malam me walidi yayi maka kake ta surfa masa zagi haka? Kar dai a ce tarewa mutsiyaciyar yarinyar nan kake Balaraba" Tafada tana nuna Balaraba dake jikin rijiya tana kallonta. Kawu ya gyara tsayuwa gami da riqe Abubuwan dake hannunsa da kyau ,ya kalli "Uwa yace"Laifi ne Dan Na tare mata Yarinyar kirki haka ka wai kin bata yaranki kin sangar tasu basa ganin kowa da mutumchi a gidan nan yanzu a ce kamar Balaraba ita Walidi zai zage yayi ta zagi kina kallonshi kice in yi shiru" Mugun Mamaki ne ya kama Uwa jin Abinda Kawu yake fada Lallai a kwai lauje cikin nadi kawun da yake zama a zagi Balaraba da ita da iyayenta da qannenta yau shine yake tare mata fada. Ta gyara tsayuwa gami da gyara daurin dankwalinta ta kalli kawun tace Au! Ashe kai ma tafara baka cin hanci cewa zakayi kafara cin kudin zina da sata Tafada tana wani girgiza jiki cike da Neman fitina, Kifta mata ido Kawu yayi ganin har ta hasala Duk Balaraba Na kallonshi. Aiko dake "Uwa tasan Halin Mijinta nan da nan ta dago Abinda yake nufi kifta mata idon da yayi [04/05, 02:54] +234 808 996 5176: πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *🐾GIMBIYA BALARABA*🐾 πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€πŸ§β€β™€ *✍🏻writting By* *Binta Umar* _*MAMAN ABDUL WAHABU*_ *πŸ…Ώ9* "Ke kuwa Uwa wane irin Abu mai muni yarinyar nan tayi miki ? Kike jifan ta da Mummunan Al'kaba'i haka me yayi zafi kema fa kin haifa" Iya take fada bayan fitowarta daga dakin ta tana tsaye ruqe da ha6a tana kallon Uwa cikin Mamaki Kafin Uwa tace komai sai gasu Mabaruka sun shigo a guje ko wanne hannushi ruqe da Farin botiki Wanda suke zuba Awarar da suke Siyarwa da kwai suna kaiwa kasuwanni Sai wasan banza suke suna dariya kamar wasu shashashai ko wacce taci janbaki gami da wani katon A cuci a kawunansu. Sai suka tsaya ganin Iyayen nasu a tsaye dagani Fada a keyi. Uwa tace "Yawwa "yayan Albarka dama tunda naji shiru nace Lallai yau Awara zata qare Allah dai yayi muku Albarka Ya Baku miji nagari duk Dan bakinciki sai ya mutu ehe!! Tafada tana kallon gefan da Iya ke tsaye tana kallonsu, Shamsiyya tace"wai meye ne ? Naga duk kunyi wani cirko cirko tafada tanawa Balaraba Wani Dan iskan kallo. Uwa tace"Wannan mai ido a tsakar kan ce take zagina bay an ta mari Walidi shine babanku yake cewa wai laifin walidi ne kan nayi mata magana Shine yar Ubanta tafito zata tare mata . Tafada gami da zama kan kujerar da tatashi ta ciga da wankinta tana sakin habaici ga Iya. Mabaruka ta kalli Kawu sallau Mahaifinsu ,Cikin Raini da rashin kunya tace "Haba Kawu yanzu har ka fi son bare da Jininka yanzu a gabanka wannan jakar! Take zagin Maihafiyarmu baka ce komai iyi!? Kawai sai ta aje botikin Awarar a Fusace tayi kan

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108