Chapter 70
Chapter 70
Mama Fulani tayi musu shiru kawai tana kallonsu da murmushi a fuskarta,taji dad'in sakin fuskar da Balaraba tayi. Yana kwance, cikin Sofa yayi lif kai baka ce a kwai mutum cikin d'akin ba,duk wannan abunda yake faruwa yana ji,tun futowar Balaraba, ya nemi nutsuwarsa ya rasa hatta baccin da ya rufe masa ido nemansa yayi ya rasa,ya lumshe ido kawai yana sauraron muryarta wacce ta kashe masa jiki, ashe haka yarinyar take da surutu,muryarta nada dad'i,abunda yake fad'a kenan cikin zuciyarsa. Mama Fulani ce kawai tasan yana gurin,domin da futo ta ganshi a kwance har tayi masa maganar tafiya shashensa yace"Sai ad'an jima zai tafi" Yanzu ma murya ta d'an daga kad'an tace"Magajin Sarki!" Da sauri Balaraba ta kalli inda Mama take kallo,gabanta na fad'uwa yanzu da yana gurin ta saki jiki take,dariya sai kace wata shashahsa, k'asa tayi da idonta lokacin da ta hangi inuwarsa kwance kan kujera, dake gurin da yake babu wadataccen haske,ya k'ashe k'wai shiyasa lokacin da ta futo bata ganshi ba, Jin muryar Mamansa yasa yayi gyaran murya,yana daga kwancen yace"Na'am Mamana" Cikin tausasawa tace"Yau da alama dai nan zaka kwana,ko"? Shiru na minti biyu,yace"Mama yau wani irin kad'aci nake ji wallahi,ki barni inyi kwanciyata nan,ina jin motsin ki" Murmushi tayi cike da tausayinsa tace"Yau yarinyar tar ce kuma ta motsa maka" Murmushi yayi wanda har sai da sukaji sautinsa,Balaraba taji wani yarrrrr! A jikinta. Yace"Dama ni kullum yaro ne,a gurin ki, tunda har yanzu banyi auran fari ba,kuma ban haihu ba" Shiru Mama tayi,kunya duk ta isheta Mama Fulani maca ce mai mutukar kunya a rayuwarta, Jakadiya Shafa'atu tayi murmushi tana k'okarin mik'ewa tsaye tace"Lallai Uban d'akina dole kasa Fulani tayi shiru,saboda ka tab'o abunda baza ta iya magana akai ba,saboda kunya, kana maganar auran fari,kai kasha kurumin ka, mata uku zaka aura me yafi wannan dad'i" Miskilin murmushi yayi iya leb'anshi yana satar kallon Balaraba shi yana ganin fuskarta sosai,itace takasa gano fuskarsa,sai dai zatinsa, Jakadiya ta runk'umfa tana fad'in A tashi lafiya Uwar d'akina" Mama tace"Allah ya bamu alkairi" Sarki!ta kalla kanta a k'asa tace"Yallab'ai a tashi lafiya" Hannu kawai ya d'aga mata,maganar tana masa wahala,dama zuwa-zuwa ce, in yaga dama wataran haka zai ta hira,mussaman da Moddibo ko Mamansa Balaraba ma mik'ewa tayi ,tai wa Mama sallama, Mama tace"Har zaki shiga Balaraba, ko dan kinga Jakadiya ta tashi" Girgiza kai tayi cikin jin nauyi tace"Ba haka bane Mama,ina so in d'an kwanta ne, naji kaina na ciwo kad'an watak'ila bacci ne" "Ayya, to ki tabbatar kin sha magani kafin ki kwanta kinji ko" Tafad'a cikin kulawa. Balaraba tace"Insha Allah Mama, Allah ya bamu alkairi" Mama tace"Ameeen Balaraba ta wuce d'akinta a nutse, Idansa a k'asa sai ka rantse da cewar bacci yake saboda yadda ya lumshe su, amma duk wani motsin Balaraba yana gani har ta shige d'aki. Ajiyar zuciya ya saki,yanayin jikinsa na sauyawa, ya rasa abunda yasa yake jin wani irin sauyi a jikinsa mutukar zai ga gilmawar ta,sai sha'awarsa ta motsa,yasan yanzu idan ba'ai wasa ba,kwana zaiyi yana mafarkai, shi kansa yasan mutum ne mai mutuk'ar Sha'awa, yana daurewa kawai,amma abun mamaki idan yana tare da Halisa baya shiga irin wannan yanayi Shi kad'ai a kabari a k'aton falon, domin Mama ma ta shiga ciki, rage haske futular yayi ya gyara kwanciyarsa,bacci ya d'aukeshi, mai cike da mafarkai, mafarkin da ya dad'e bai yi ba,yau yayi Balaraba ya gani, tare da wannan matar suna cikin farin ciki da annushuwa,suka zo gurinsa, kamar kullum, matar ta kama hannusa dana Balaraba ta had'a guri guda, ta tafi tana waiwayensu, fuskarta cike da farin ciki har suka daina ganinta. Balaraba ya kalla sai yaga tanai masa wani k'ayataccen murmushi, gashi ta rik'e hannunsa sosai, taja hankalinsa cikin mafarkin, wanda yayi sanadin da yakasa daurewa ya rungume ta sosai yana kiss d'inta, ji yake kamar gaske, jikinsa duk ya shiga babu abunda yake buk'ata lokacin sai Jima'i, sai da ya kai k'ololowa sannan ya farka cikin wani mugun yanayi jikinsa duk ya b'aci, still kamar yadda yake ganin girmansa cikin mafarkin haka take a fili, ta mik'e tsaye! Tana jiran hakkinta . https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*GIMBIYA BALARABA*_ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* ```MARUBUCIYAR``` *NANA KHADIJA* *YARO DA KUD'I* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* _*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_ _________________________ ```We are here to educate, motivate and entertain aur Reades``` _________________________ _*DEDIGATED*_ _*TO*_ _RAHAMA ALIYU_ _*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR RAHIM*_ *🅿81* Ya dad'e yana jin wani irin yanayi a jikinsa, wanda bai tab'a jin irinsa ba, da k'yar ya samu ya mik'e a jigace, futa yayi daga shashen gaba d'aya, ya nufi nasa, lokacin ana kiraye-kirayen sallahr asubah, a gurguje yayi wanka gami da tsarkake jikinsa, ya futo ya zura jallabiya me yankakken hannu, wani takalmi mai kyau ya zura a k'afarsa ya futa, da nufin zuwa massalaci, domin gabatar da sallahr asubah. ******* Uwa! da Shamsiyya ne zaune gaban wani mutumi zaune a kan wani buzu, da wasu manya-manyan carbuna, gami da alluna irin na k'arfe a jijjigine a bango, yana sanye da riga da wando na wani yadi bulu, wanda akai wa d'inki "yar shara. Gabansa wani fefe ne k'aton gaske cike da yashi, yana zane-zane a ciki, shi kad'ai ya san abunda yake zanawa. Yana ganinsu ya saki fuskarsa, sannu da zuwa kawai yake musu. Suka nemi guri suka zauna suna gaisawa, amsawa yake, hankalinsa na kan Shamsiyya. Yashin, da yake gabansa ya hau zanawa, tsawon minti biyar, ya d'ago kansa yana kallonsu yace" Na duba naga abunda yake tafe daku, ina fatan dukanin abunda aka umarce ku dashi zakuyi batare da kun bamu wahala ba" Uwa! ta gyara zamanta sosai, tace"Allah ya gafarta maka, duk abunda aka umarce mu muyi zamu yi mutuk'ar buk'atarmu zata biya" "To Masha Allah" Arrama ya fad'a yana kallon Shamsiyya sai sid'e leb'e yake. Gayan murya yayi, yace"Naga wata yarinya buduwar wa,gata anan" Yafad'a yana nuna wani zane da yayi jikin yashin. Uwa! ta k'walalo ido tana son ganin budurwar da ya fad'a Murmushi yayi yace"Ai baza ki ganta ba, wannan aikinmu ne" Uwa! tayi yak'e tace" Allah ya taimake ka" Arrama ya cigaba da cewa "Wannan yarinyar da nagani, naganta kewaye da wasu taurari masu haske da d'aukaka, kuma na fahimci akanta kuka zo" Shamsiyya ta gyad'a kai tana fad'in "Hakane Arrama, Balaraba sunanta. Murmushi yayi, ya sid'i leb'ansa a karo na biyu yace" Itace Balaraba, gatanan cikin gidan sarauta, kewaye da dawakai da bayi, gatanan cikin shigar alfarma, kuma zata haifi "yaya maza sosai a gidan, ciki kuwa harda Sarki!" Arrama ya k'arasa maganarsa yana duba ya shin dake gabansa. Uwa! saura kad'an ta saki futsari saboda jin abunda Arrama yace, bakinta na rawa tace" Yanzu Allah ya taimake ka babu yadda za'ayi a rusa mata rayuwa,a sabauta mata rayuwa ta haukace, a maye gurbinta da Shamsiyya, gata a gabanka" Ta k'arasa magana tana nuna masa Shamsiyya Arrama, yayi wani bazawarin murmushi, yace"Akwai yadda za'ayi mana mutuk'ar zaku bi umarni kamar yadda na fad'a muku tun farkon zuwanku nan". Shamsiyya tace"Insha Allah zamu bi umarni" Arrama yace"To yanzu abunda za'ayi, ke zaki zauna a gurina tsawon kwana bakwai zan fara yi miki wankan magani, ke kuma" Yafad'a yana kallon Uwa! yace"Ke kuma zan had'a miki wasu magunguna da zakuje kuyi amfani dashi duk rintsi kar ku wuce kwana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108