Chapter 30
Chapter 30
nan, abu mawuyaci ne su yarda ka aure ta" "Ko kowa yaki yarda da al'amarin Maimar taba zai lamunce min,sabuda kasan halinshi da saukin kai, mutukar a kayi buncike a kanta, a gano babu wani aibu, a tattare da ita, ba zai hana kulluwar al'amarin ba" "Ok Allah ya bada sa'a" Abunda yace kenan, ya koma ya kwanta cikin kujera Shiru falo yayi kowa yana sake-sake cikin zuciyarsa,daga bisani Maddibo ya mike ya nufi wani bedroom dake falon domin ya yi wanka yayi shirin bacci Shi kuwa Sarki! da alama a falon zai kwana domin dai bashi da alamar tashi ya shiga bed din yana kwance yana dacin rai, tunani kawai yakeyi kan Balaraba, wane irin mataki zai dauka a kanta, domin duk abunda yayi mata bai wuce ba sai yaga karshen rashin kunyar ta, sai dai wannan ya zama dalilin batawarsu da Maddibo *Comment* *Vote anda Share* [07/07, 22:32] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®REAL BINTU BATULA👄* *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*Zamani Writes Association*_🤝🏻 _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{ RAHAMA ALIYU}``` *🅿41* ```Bisimillahir-rahamanir-rahim``` Har karfe biyu na dare yana zaune a falo yana kallace-kallace,Maddibo ko tuntuni yayi bacci babu abunda ya dame shi, wani film yake kalla tashar Sky Moveis, sai da yaga karshen film din sannan ya mike a nutse ya kashe kayan kallon ya nufi bedroom din nasa, kai tsaye toilet ya shiga yayi wanka gami da dauro al'wala, ya futo a nutse ya shirya, jikinshi, ya fesa turare sannan ya shimfida dadduma ya tada sallahr nafila kamar yadda ya saba,duk daran duniya, yana nan zaune kan abun sallah har aka fara kiran sallahr asubahi, ya mike tsaye hannushi rike da carbi ya sanya wani takalmi mai uban kyau,jikinshi duk wani gashi-gashi kana kallon takalmin kasan irin na masu mulki ne, futa yayi daga dakin nasa ya nufi kofa, har yq bude zai futa,sai ya tuna da Maddibo ya koma da baya, ya bude bedroom din da yaga ya shiga jiya, Maddibo na kwance bacci yake sosai, Kiran sunanshi yayi"Maddibo" Bude ido yayi dake bashi da nauyin bacci "Ka tashi kayi sallah ni na tafi massalaci, sai kafito" Bai tsaya ya saurari abunda Maddibo zai ce ba kawai ya fuce daga dakin Yana futa suka ci karo da Maimarta ba ya futo tare suka jera har zuwa massalacin, Bayan an idar da sallah suka gaisa, jama'a kowa yana so su gaisa da Maimarta ba, da yake in an idar da Sallah ya kan zauna a massalanci su gaisa da Jama'a ko kuma in da akwai daurin aure ko radin suna duk nan za'a gabatar kafin ya koma gida ya futo fada Sarki ya na zaune kusa dashi Waziri yazo suka gaisa da dan uwanshi, da alama akwai maganar da yake so yayi, ganin haka yasa mutane suka fara futa da dai-dai da dai-dai, gurin ya rage daga Maimarta ba,sai Waziri da Sarki! Sai Maddibo dake gefe guda yana lazimi Kanshi a kasa yace"Allah shi taimake, dama akwai maganar da nake so muyi da kai, tuntuni wallahi sai yau, nace,ko zamuyi maganar kawai a huta Allah shi taimake ka" Maimarta ba,yana zaune hannushi rike da wani carbi mai kyau sai kalli yake,lazimi yake, kallon kanin nasa yake, yana nazarinsa sabuda yafi kowa sanin waye Waziri, duk da girmansa sam bai san abunda ya dace ba gashi bai iya yanke hukunci ba,shiyasa ko wani abu a kakawo gaban fada,ba ya wakiltashi a kai, gwara ya wakilta Sarki!sabuda yana yin abu cikin hikima da adalci, Gyaran murya yayi yana nuna masa carbi,alamar ya daka ta tukkuna, ya cika carbin Tsit!gurin yayi har sai da ya kammala, sannan ya dago kanshi cikin nutsuwa yace"Wace irin magana ce, wannan wacce ka boye ta ka kasa fada gashi kullum muna zama a fada, da tuni an warware ta" "Allah shi gafarta maka, ai wannan maganar bata shafi fada, ba ta shafi cikin gida ne," Girgiza kai Maimarta ba yayi tsawon minti biyu bece komai ba,daga bisani ya kalli Waziri yace"ka sameni a shashen Fulani sai mu tattauna maganar, Allaj ya warware mana" "To" To Masha Allah, Allah ya kara nisan kwana ai magana ce ta alkairi nasan kuma kai ma zakaji dadin ta" Murmushi Maimarta ba yayi ya mika masa hannu suka musabaha, yace"ai tunda naga kana farin ciki nasan maganar ta shafe ka" "Kwarai kuwa" Waziri yafada shima yana murmushi, amma fa ta ciki na ciki Sarki! ne ya matso sosai kusa da mahaifin nasa, kanshi a kasa yace"barka da asubah" Hannunshi Maimarta ba ya riko fuskarshi a sake yace"kai kayi min laifi, kwana biyu baka zuwa fada,bazan karbi gaisuwar ka b Sosa kai yayi na sabo,yayi kasa da kanshi yana murmushi yace"tuba nake ranka shi dade, tunda mukaje can gwarzo na dawo bana jin dadi jikina,wallahi" "Me yasa baka kawo uzirin ka ba" Shiru yayi sai faman sosa kai yake Waziri Zayyanu yace"wannan sharme ne, mu me yasa muke futowa fada, kullum kuma ai tare mukaje can Garzon ko ba haka ba ne, wannan yana nuna mana cewar sam baza ka iya wakiltar jama'a ba. Cikin fada ya karashe maganar, A nutse Sarki ya dago kai yana kallonshi,ya wani hade fuska sam ba ya so yana shiga lamarin shi,shi kuma yaki ya gane, Ganin yadda Sarki! ya hade fuska ne yasa Waziri saurin sunkyar da kansa, sabuda wani irin kwarjini da Allah yayi masa, Wannan abun da Waziri yayi masa yasa ya fasa gaida shi,kawai ya dauke kanshi,jira kawai yake Maimarta ba ya mike shima ya samu damar tafiya, Maddibo ne ya karaso kusa da Maimarta ba ya gai dashi, ya gaida Mahaifin shi Waziri Zayyanu, Maimarta ba ya mike cikin nutsuwa, suma suka mike suka biyo bayanshi lokacin gari ya soma washe wa, Wasu fadawa ne guda Uku tsaye bakin massalacin sune suka rufa musu baya,har sai da Maimar taba,ya shiga Shashenshi,sannan kowa yayi nasa ban garan, Sai wajejen Goma da wani abu sannan Waziri ya samu Maimar taba,bangaran Fulani, nan suka zauna a ke bantaccan falo wanda yake zama domin sirri irin wannan, Gyara zama yayi sosai yace"ranka ya dade magana ce daga Sarkin garin Yalwa, kasan tare mukayi karatu dashi,sosai har yanzu alakar mu dashi tanan, to shine yake neman wata alfarma a gare ka, wato ya naso ya hada jini da kai, wai yarinyar shi Azima tana son Auran Almansor,, shine ya aiko min da sako, a kan hakan, Allah shi tai makeka kaji abunda yake tafe dani" Waziri ya kare maganar yana sauke ajiyar zuciya Kanshi a kasa yana sauraron abunda Maimar taba zai ce Minti biyu a tsakani, Maimarta ba yace"wannan ba hurumi na ba ne,domin bazan iya tilas ta Sarki! ya je ya nemi auran yarinyar nan ba, abunda zakayi kawai ka nemi shi kafada masa zan can, sannan yarinyar tazo ya gan ta in yaga tayi masa shikkenan,ni dan addu'a ne, sai a hada da Halisa kawai" *Comment* *Vote and Share* [08/07, 13:24] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®REAL BINTU BATULA👄* *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*Zamani Writes Association*_🤝🏻 _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{ RAHAMA ALIYU}``` *🅿42* ```Bisimillahir-rahamanir-rahim``` Shiru Waziri Zayyanu yayi na minti biyu kana ya dago kanshi yana kallon Maimartaba yace"Allah shi taimake ka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108