Chapter 55
Chapter 55
Ajiyar zuciya ta sauke,ya cigaba da cewa"maganar gurin sai da abuncin ki ki bar wa su Hauwa'u su cigaba da samu a ciki, in sha Allahu xaki fara business in munyi aure" Cikin murna da farin ciki take masa godiya,a bisa karamcin sa a gareta, tanaji a yanzu bata da babban masoyi kamar sa, zata dunga k'okarin danne damuwar ta duk Dan ta kwantr masa da hankali, Salmanu ne, ya k'araso gurin hannunsa d'auke da wani faranti me fad'i ya aje a tsakiyar su, Moddibo yace"jeka abunka kaji" godiya Salmanu yayi ya bar gurin, Sauri-sauri yake ya gama abunda yake yaje ya fesawa abokinshi Dauda labari,shi Dauda yana b'angaran uwar gidan Sarki wato, Kulu,mai d'akin kudu, kenan Mama Kulu kenan, A nutse suke karyawa ita dashi, kana ganinsu kasan masoyan asali ne,Wanda suka yarda da Kansu, Usuman na gefe yana karyawa shima. Cikin nutsuwa yake sakkowa daga sama step by step hannunsa na rik'e dana Sadiya, yana sanye da wasu kaya na alfarma, masu tafe da wata alkyabba, kafarshi sanye da wani takalim me gidan ya tsa, babu nad'i a Kansa, duk da cewar shigar dake jikinsa ta nad'in ce amma bai yi ba, cewarshi ya gaji da kayan nauyi, sumarshi ya gyara,sosai da gemunshi, sai sheki yake,d'an k'aramin bakinsa mai d'auke da siraran lips Wanda suka d'an yi duhu kad'an, yayi Kyau kwantaccan gashi ya kewaye shi, as'usul idanunshi a lumshe kamar ko da yaushe,sai k'amshi yake zubawa, yana sakkowa masu hidima a gurin suna zubewa suna kwasar gaisuwa, ko wanne munafurci fall a abakinsa saboda ganinsa da k'aramar yarinya "yar shekara goma, cikin yanayin tafiyarsa ya nufi, daining teble d'insa Wanda yake cike da abubuwan ci, dai-dai inda suke zaune yazo ya gifta Balaraba taji gabanta yana fad'uwa duk da cewar ba ta kalli fuskarsa ba,gefansa ta kalla, Yanayin kwarjinsa da yadda yake tafiya cikin k'asaita ya furgitata ko ba'afad'a an San d'an mulki ne shi saboda abun a jinsa yake, jin kamshin turaran sa yasa Moddibo saurin waiwayo wa sai yaga yana k'okarin zama kan kujerar daining d'in, ga Sadiya ta zauna itama, ku-ku shi na tsaye gefe,yana jira ya dai-dai ta zamansa yafara had'a masa,abin kari. Mik'ewa yayi ya bar Balaraba a gurin ya nufi inda Sarki! yake zaune, sukai yi magana sama-sama,batajin abunda suke cewa, saboda a kwai tazara a tsaksninsu can ta hango,Sadiya ta zage sai kwasar girki take, babu wani kamun kai sosai yarinyar ta bata haushi, Moddibo ne ya k'araso inda take,tayi saurin kauda kanta saboda wani lokacin shima haushinsa takeji in taga yana wa Sarki!rawar jiki. "Gimbiya zanje in gaisa da mutan gida,zuwa yamma zan shigo sai muk'arasa maganar mu, don Allah ki cire fargar ba komai a ranki" A sake tace"shikkenan sai ka dawo a gaishe min dasu" "Zasuji insha Allahu" Yafad'a yana k'okarin barin gurin. Bayan futar Moddibo daga falo,sai yayi shiru saboda duk masu hidima a gurin sun gama sun futa,sai sautin AC ne kawai yake tashi, Usuman can gefe yake yana ta "yan wasaninsa, sai taji zaman gurin ya gundure ta, taja tsaki ya kai sau biyat r in ta d'aga kai ta hango Sadiya,na cin abunci ta sake sosai dashi tana masa hira har da dariya. Sam! tak'i yarda su had'a ido dashi, a sace take k'are masa kallo yana cin abunci cikin nutsuwa, gashi fuskarsa a sake,yana sauraron hirar da Sadiya take masa,cikin zuciyar ta take ayyana irin dukan da zata yiwa Sadiya. Taku! tafaraji k'was!k'was!k'was! irin na mace, takun takalmin ya d'auki hankalin ta har shi uban gayyar, da yake can inda yake zaune saitin k'ofar shigowa ne, shiyasa ya ga wacce ta shigo Gimbiya Halisa ce, Balaraba na zaune can wata kusuwar wa shiyasa bata ganta ba, Halisa tana tare da wasu bayi guda biyu suna take mata baya, wanda suka tsaya bakin k'ofar shigowa, can inda ta hange shi zaune ta nufa fuskarta babu walwala,ganinshi zaune da wata,daga can nesa tana yiwa Sadiya kallon wata k'atuwar budurwa, shiyasa ta sha kunu,sosai tana tunanin me ya kawo mace har falonsa duk da tasan halinsa ba ya Neman mata. Giftawar ta Balaraba ta hanga,ta bita da kallo daga sama har k'asa, tana ganin yanayin shigarta ta gane," yar sarauta ce. Sarki! kuwa d'auke kansa yayi daga kanta har ta k'araso gurin ta tsaya gami da d'ora hannuta kan kujerar da Sadiya take zaune tana mata wani kallo irin na raini tace"Habibi wannan yarinyar a ina ka samo ta,naga sam ba jinsin mu bace" Banza yayi mata,kawai ya cigaba da cinsa abuncin sa a tsana ke, K'ara maimata maganar tayi,ya d'ago kansa cikin jin haushin ta yace"ban sani ba, ki kauce daga kan mutane tunda ke baki da ladabi da sanin ya kamata" Ganin ya hasala! yasa ta fara yak'e tace" tunda na shigo na ganka zaune da mace a guri guda naji hankalina ya tashi shiyasa na rasa nutsuwa ta, sai da na k'araso kuma naga ashe ma yarinya ce,amma dai duk da haka hankalina bai kwanta da ita ba,yarinya sai kace,me dubi yadda take k'walo ido kamar mayya" Karaf! a kunnen Balaraba,dama taji abunda Halisa tace a farko Dan gane da Sadiya. Ranta a b'ace ta futo daga inda take,ta tsaya a gurin tana kallon su, a cunkushe ta bud'e baki tayi magana, tace"ke! Sadiya baro gurin nan, kinji ko" Duk hankalinsu ya koma kanta har shi,uban tafiyar, ganin fuskar yayar ta a murtuke ya fad'ar mata da gaba,sai ta fara yunk'urin mik'ewa tsaye domin ta cika umarnin ta, yayi saurin dafe hannun yarinyar ya hanata tafiya, ido ya zubawa Balarabar dake tsaye can gefe tana cika tana batsewa, ganin Sadiya tak'i tasowa yasa ta k'ara buga mata tsawa,a karo na biyu. A nutse ya d'an daga muryarsa yace"tak'i zuwa d'in in kin isa kizo ki jata,da k'arfi mugani" *Comments Vote and Share* https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^^^^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^^^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* _*MARUBUCIYAR*_ ```Nana Khadija``` ```Yaro Da kud'i``` ```Gimbiya Balaraba``` _*ZAMANI WRITERS*_ _*ASSOCIATION🤝🏻*_ _*DEDIGATED*_ *_TO_* ```RAHAMA ALIYU``` ```BISIMILLAHIR- RAHAMANIR-RAHIM``` *🅿63* Cike da karsashi,da jarumta ta durfafi inda suke fuskarta a had'e tamkar wacce bata tab'a dariya ba, tana zuwa tafara yunk'urin fuzge hannun Sadiya daga cikin nasa, a nutse ya d'ago kanshi tare da zuba mata idanunsa,ya bud'e tar! Gabanta ya buga! sai kace mai lak'ani a idonsa, duk gwiwarta ta sage! kanta ta sunkuyar k'asa domin bazata iya jurar k'alon k'wayar idonsa ba, amma duk da haka bata fasa k'okarin fuzge hannun Sadiyar ba saboda k'arfin Hali, rik'e hannun yayi tsaf! da tazo zata k'wace sai su had'a hannu, sai ya had'a da hannun nata ya matse,ganin abun nasa harda iskanci, yasa ta fuzge hannunta tana zabga masa harara, batare da tabari ya gane gazawar ta ba,ta kalli Sadiya,cikin fad'a tace"zan kama ki,wallahi tunda kike barin maza suna rik'e miki hannu" barin gurin tayi a fusace,ta kama hannun Usuman suka haura sama. Kallo ya bita dashi, fuskarsa d'auke da murmushi, girgiza kai yayi kawai yana mamakin k'uruciyar ta, yanzu ya gane itama yarinya ce, sakin hannun Sadiya yayi dake zaune tana mayar da k'walar da ta taro a idonta,saboda tasan halin masifar yayarta Yace"kwantar da hankalin ki kinji ko Halimatu, duk abunda tayi miki in mun had'u zan rama miki, tashi kije" mik'ewa tayi jikinta a sanyaye, ta haura
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108