Chapter 9
Chapter 9
sun zubarwa da Suwaibah Joni ******* Tun daga ranar Su Sallau suka matsawa Suwaibah in har suna gidan bata isa ta fito ba sai su hau jifanta ko su sanya mata kafa tafadi ,ko du zuba karkashi kofar dakinta da ta fito tafadi kasa, Su kuma Na gefe Na faman kyalkyala mata dariya Ko idan tayi girgi ,suje su kwashe su cinye tai magana su zageta Ranar Sallau ya dauki cokali mai ya tsu ya kai mata jifa a goshin ta,bayan ta fito daga ban daki,ai kuwa kan kace kwabo jini ya tsinke sai ta saki butar hannunta,ta dafe gurin tana jin wani mugun zafi Lantana dake zaune kan kujera "yar tsuguno tana tsintar shinkafa ta kyalkyale da dariya,tace kayi min daidai Sallau!! *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* ππππ _in kana bukatar cigabanshi ga number nan_ 08089965176 [04/05, 03:09] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? π§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββ *πΎGIMBIYA BALARABA*πΎ π§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββ *βπ»Writting by* _*BINTA UMAR*_ *MAMAN ABDUL WAHABU* _BISSIMILLAHI RAHAMANIR RAHIM_ *π Ώ14* Suwibah ta dago kai tana kallon Sallau ,dake tsaye , zuba mata ido yana jiran ta tanka masa ,yayi mata wankin babban bargo! Tafi minti biyar tana kallonshi ta gaza furta ko kalma daya,sabida tana tunin yin magana ,a yadda suke su kadai a gidan zasu iya yi mata duka, Sai kawai ta wuce shi ta nufi dakinta jini Na diga a goshinta, Suka kwashe da dariya suna nuna ta da hannu Lantana kamar ta tuntsira kasa Dan dariya Tace "in kin sa kiyi magana mana" Maman yace"wallahi Na dauka ma ramawa zatayi da naga tana kallonka. Sallau ya zabura! Yace ta rama? Lallai da ta tarowa kanta Masifa tana cikin gidan Uban nawa" Lantana tace "duk Ku rabu da ita a kwai Abinda zamu kulla mata idan an kwana biya" "Zo kaji" tafada tana yafito sallau da hannunta Rada tayi masa wacce ko Maman dake gurin a zaune bai jiba. Su LA fashe da dariya murya kasa kasa ,Sallau yace"gaskiya Lantana dole a Sara miki' Lantana tace ba dole ba! ai ni duk Wanda yaci tuwo miya ya sha dani Ko da Malam tanko ya dawo yaga goshin suwaibah a fashe yayi tambayar duniya yaya haka tafaru taqi fada masa,sai ya rabu da ita kawai ya samo mata magani ,ta sha ta kwanta nan da nan bacci ya dauke ta,kwananan tana yawan yin bacci tarasa meye dalili. ***** To haka rayuwa tai ta tafiya har cikin suwaibah ya fito ,lantana ta daga hankalinta,sosai Amma da ta tuno Abinda suka shiryawa cikn ita da sallau sai hankalinta ya kwanta. Cikin suwaibah Na da wata tara tana dab da haihuwa ko yau ko gobe, ta fito zata ban daki ,da kyar take taka kasa sabida tsabar nauyin da cikin yayi mata bayan haka kuma Mararta Na mata ciwo Ta juya baya tana jawo ruwa a rijiya Sallau ya fito daga dakin mahaifiyarsa ya hankade ta ,tayi taga taga zata Afka cikin rijiyar tayi saurin dafa bango ,Amma INA!! Santsin gurin ya kwashe tafadi ,gurin rigijff!! Cikinta ya bugu da murfin rijiyar dake jin gine jikin bango Duk yayi tsatsa ,dalili kenan da yasa yaqi zama a rijiyar shine Lantana ta jin gine shi gurin Suwaibah ta kwala ka!! Tana fadin wayyo Allah cikina *innaliliahi wa inna ilaiyi rajiun* Lantana tafito a suk wane tana fadin "ke lafiya ne kike yi mana ihu? Sai taga nta zube bakin rijya gurin wanke wankensu, Cikin zuciyarta tace Sallau ya cika ai ki kenan Suwaiba ta dinga daga mata hannu Alamar ta temake ta, Tabe baki lantana tayi "tace Abinda ya dame ki kenan ,nima lokacin da nake haihuwa babu wacce take te makamin ,sabida haka kije can ki karata,ta koma cikin dakinta,tana waqe waqe. Sallau ma ficewa yayi daga gidan babu Abinda ya dame shi. *BINTA UMAR ABBALE* _MARUBUCIYAR_ *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMIBIYA BALARABA* ππππ _in kana bukatar ci gabanshi ga number nan_ 08089965176 [04/05, 03:09] +234 808 996 5176: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? π§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββ *πΎGIMBIYA BALARABA*πΎ π§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββπ§ββ *βπ»Written by* _*BINTA UMAR*_ *MAMAN ABDUL WAHABU* _MALUKAL MULKI ZULJALALI WAL IKIRAM_ *π Ώ15* Suwaibah ta ruqe cikin ta tana fidda numfashi Sama Sama ,sai ko karin tashi take yi a gurin ta kasa ,sai kawai ta koma ta kwanta tana salati gami da Addu'oi tana fatan idan mutuwarta ce tazo to Allah yasa ta cika da Kalmar shahada. Murqususu take tana jin wani mugun ciwon Mara kwankwason ta tamkar ya balle daga jikinta,tun tana iya yin Addu'ar afili har ta gazayi ta dawo yi a zuciyarta Lantana tafito daga dakinta hannunta riqe da bota da Alama ban daki zata shiga, Sai taga Suwaibah kwance a bakin rariyar Bandaki kamar ma bata numfashi, Wani farin ciki ya kamata ,ta karaso gurin ta daki cikin Suwaibah da kafar ta tana dariya ,tace" shegiya "Yar mutsiyata "yar dadi miji ,yanzu shi malam din ai sai yazo ya karbar miki haihuwar ,shida ya dirka miki cikin,in sha Allahu dake da duk Dan da zaki Haifa sai kun muto kowa ya huta da jaraba" Tafada tana kara dukan cikin a karo Na biyu ganin suwaibah bata motsa bah. Nan ma shiru Sai ta daga botar dake hannunta ta kwara mata ruwan ciki. Suwaibah tasaki Ajiyar zuciya Wanda yayi dai dai da tsinkewar jini ,a jikinta kwarara yafara bin rariya Gaban Lantana ya fadi ,ganin yadda jini yabi bin makwarara tamkar Wanda a ka kwance famfo ,tayi sauri ta tsallake Suwaibah ta shiga bandaki tayi uzirinta ,tafito da sauri ta shige dakinta ,tabar Suwaibah ,Akwan ce Rai a hannun Allah. Atika ta shigo gidan Cikin Sallama ita ma da nata tsohun cikin,dama tare suke jerawa ,kusan kullum ta kanzo gidansu gurin suwaibah ,si ta hirarrakinsu duk a kan Haihuwa, Lantana tai tajin haushi tana zubarmusu da habaici,basa kulata *innalilahi wa'ina ilaihi rajiun*!! Shine Abinda Atika tafada ta yi kan suwaibah tana kokarin tashin ta ,Amma ina!!ina takasa sakamokon yadda jikin Suwaibah ya shika bubu kwari wuya ya langwabe, Bakinta a bushe tace"Atika mutuwa zanyi ki cewa babanku ya gafarce ni bani da rabon kumawa ga Dan gina ,Dan Allah duk Abinda Na haifa ki riqe min shi a hannunki Na baki Amanarshi Atika ta fashe da kuka tace"bazaki mutu ba in sha Allahu zaki goya danki da hannuki" Suwaibah ta rimtse ido tana cije baki! Cikin Wahala jin wani Abu da yake kokarin dannowa ta kasanta ,ta riqa sakin Nushi a galabaice!! Atika ta kwantar da ita a gurun ta mike cikin zafin Nama tayi dakin Lantana da Sauri. Tana zaune kan tabarma da mifici a hannunta ,ta ware wakokin bar mana coge cikin redion ta sai ji take cike da Nishadi tana bin wakar cikin kwarewa ,tamkar ita ce ta rerata. Atika taga labule fuskarta jike da ruwan hawaye Ciki tashin Hankali tace"Lantana ki kawo temako Dan girman Allah,ga suwaibah can zata haihu jini yana kwarara a jikinta" Lantana tayi mata kwallon banza tace"ke Fice min A daki munafukar banza da wofi ni ce nai Mata cikin zaki zo kice in temaka mata kowa ai da haka ya haihu,lokacin da nake haihuwa Uwarki! Ta taya ni ne"? Da sauri Atika ta fita daga dakin tana Mamakin Rashin Imanin Lantana Ta yi hanyar waje da sauri domin taje ta kira Gwaggo Shattu matar Liman, Ita ko Lantana tana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108