Chapter 33
Chapter 33
babu yabo babu fallasa yace"Khalifa ya kirani a waya dazu yace kana nema" "Kwarai kuwa" Waziri yafada yana gyara zamansa kan kujera "To Masha Allah, ina sauraron ka" Mikewa Mama tayi ta bar gurin dan ta barsu su sake suyi maganarsu amma tana mamakin abunda zai sa Waziri kiran Sarki! sabuda tasan basa jituwa ko kadan. "Wato kana jina ko"? "ina jin ka" Yafada kai tsaye! "Kasan abokina Maimarta ba Sarkin Yalwa, ko? Cikin nutsuwa yace" Eh nasanshi " "To shine ya ke neman alfarma a gurina da gurinka, a kan yana so ka auri yarinyar shi Azima, ta nuna tana sonka, to shine na nake neman alfarma a gurinka, a matsayi na na Mahaifinka, kar ka bani kunya, a gurin abokina kaje ka nemi yarinyar nan, insha Allahu baka da matsala da ita, yarinya ce nutsatstsiya" Kanshi na kasa tsawon minti biyar bece komai ba, daga bisani ya dago kanshi, a nutse yace" Zanyi tunani akai" "Zakayi tunani akai"? Waziri ya maimaita maganar da yayi cikin sigar tambaya, "Fuskarshi ya hade sosai ya dago kanshi yana kallon Waziri, yace" Allah ya taimake ka, wannan maganar da kazo min da ita tayi min tsauri dayawa dole ne inyi nazari a kanta, kabani nan da kwana biyu,duk abunda na yanke zan maka magana" Kwantar da kai Waziri yayi sabuda yana nema, yace"A'a baza muyi haka da kai ba, Magajin Sarki, ka fada min kawai yanzu, wannan abun me sauki ne, a gurinka, domin kasan ko ba yau ba, dole zaka hada mata hudu,sabuda muna saka ran zaka gaji kujerar mahaifin ka" Wadannan maganganun da Waziri yayi sun bashi mutukar mamaki, wai yau da bakinshi yake kiranshi da Magajin Sarki, lallai akwai wani abu dake zuciyar shi wanda yake boye wa, Amma sabuda ya kyaleshi ya tafi yasa yace"Shikkenan na amunce da, Allah ya shige mana gaba, Murmushi Waziri yayi yace"Allah yayi maka albarka Magajin Sarki, in sha Allahu zakaji dadin auran yarinyar, kaga sai a hada da Halisa ko" "Duk abunda kuka yanke dai-dai ne a gurina" yafada yana kokarin mikewa da niyar tafiya Hannu ya mika masa suka yi sallama, Waziri sai shi masa albarka yakeyi, sai murna yake kamar ya ari baki, nan Sarki! ya barshi, cikin farin cikin amuncewar sa ****** *Balaraba* kuwa kwana tayi tana kuka a ranar kamar ranta zai futa, taji ciwon wulakancin da Sarki! yayi mata, wai ita yake kira "yar towo-towo " yar bakin kasuwa, tayi kukan rashin iyaye, tasan duk rashin su ne ya jawo mata wannan wulakancin, gashi tana shigowa gidan Lantana ta tare ta tana zagi, wai sai ta futo mata da kudin da ta samo, in ba haka ba, zata shiga gidan ba, nan su Shamsiyya suka dinga ihu! suna dariya, tafi minti ashirin a tsaye a soro sai da Walidi ya shigo gidan, ya ga abunda yake faruwa,ya zage Lantana tas! har Uwa bai bari ba duk ya hada ya dinga dura musu ashar, ya rike hannun Balaraba suka shiga ciki, Su Sadiya da Usuman suna zaune, a tsakiyar dakin sai kuka sukeyi, babu haske,ga uban sauro sai tashi yake, a dakin, haka ta shiga takamasu ta rungume tana kuka, har sukayi bacci, kwata-kwata zaman gidan ya ishe ta, dole ne ta samawa kanta ma futa. Sam, bata yi wani baccin arziki ba, da ta rufe ido sai ta hango shi lokacin da yake tofa mata miyau din bakinshi, bata jin bacin ran abunda Lantana tayi kamar wannan, sabuda tasaba, dashi,tunani kawai take, wace irin hanya zata bi ta rama abunda yai mata, Tunda tayi sallahr asubah bata koma ba, tana zsune kan abun sallah tana lazimi, bacci yana fuxgar ta, kadan-kadan, ta jiyo muryar Lantana tana kwala mata kira, "Balaraba, ke Balaraba" Lantana tafada tana dukan kofar dakin kamar zata karya ta. Tana jin ta tayi shiru har sai da ta ha'da carbi sannan ta mike a nutse taje ta bude kofar, Lantana tayi mata wani kaskantaccan kallo, tace"au! kwana kikayi kina kuka naga idanunki sunyi jajazir!" tafada tana rike ha6a cikin mamaki! "Me zanyi miki ki ke buga min kofa" tafada kamar bata san abunda ya kawo ta ba, "Au! tambaya ta kike me zaki min"? Lantana tafada cikin mamaki! " to kudin gasara zaki bani" ta karashe maganar tana gyara daurin zaninta "Lantana yau bani da kudi, sai gobe" "Baki isa ba wallahi" Tafada cikin hayaniya da masifa Rantsuwar da tayi ya mutukar bawa Balaraba,mamaki, ita ko yau batayi niyya bayar wa za taga inda wanda ya isa yasa ta bayar *Comment* *Vote and Share* [11/07, 05:47] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 ^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®REAL BINTU BATULA👄* *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*Zamani Writes Association*_🤝🏻 _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{RAHAMA ALIYU}``` *🅿45* ```Bisimillahir-rahamanir-rahim``` Kawu Sallau ne ya futo daga daki, hannushi rike da wata karamar redio yana kokarin dai-dai ta tasha, dake safiya ce , yana so ya saurari labarai, kofar dakin Balaraba ya nufa inda Lantana take tsaye tana karewa Balaraba zagi, tace"Jiya kinfi awa daya a waje,kuma ance me mota ne mutumin da yazo gurin ki amma sabuda kin raina mana hankali shine zakice baza ki bamu kudin gasara ba to ko sai kin bayar sannan zaki futa daga gidanan kinji na gaya miki" Jin abunda Lantana tace yasa Sallau saurin karasowa gurin yana rage karar redio dake hannushi yace"Lantana wai me yake faruwa ne, tun daga daki nake jiyo hayaniyar ki" Gyara tsawuyar ta tayi tace"Yo in banda sharri irin na wannan yarinyar, da tsabar mugun abu, wai yau bata da kudin gasara wanda take bamu muna siya muna karyawa dashi, jiya fa Wani me mota ne yazo zance gurinta, ta dade a waje,kafin ta shigo gida" Walidi ne ya bude kofar bandaki ya fito,hannushi rike da bota, da alama sai yanzu zai yi sallar asubah, a jiye botar yayi nan bakin rijiya ya nufi gurin da suke, ya kalli Lantana yana wani ciccije baki yace" Yawa! kike fa Lantana, Ehh wannan da kuke gani fa tafi karfin wulakanci a gurinku, kune mutsiya ta daga ke har ita Uwa!din, kudin gasarar banza da wofi, kullum da take baku kudin ai babu wanda ya taba gode mata, sai dai kullum ku bita da zagi! To wallahi kukayi wasa zan k'ona kudin da aka bani in baku, banzaye fattararru kawai!! ya karashe maganar yana wani tangadi kamar zai buge Lantanar, da ssuri ta matsa gefe guda, Cikin mamaki tace"Ni kake zagi ko Walidi" "Kinga Lantana"! Walidi yafada yana nuna ta da yatsa Ya cigaba da cewa" nifa a kan wannan zan iya kaddamar miki, gwara ki kauce kawai, Eh! ni dai na fada miki" Shiru Lantana tayi tana zare ido, shi kuwa Sallau ko a jikinsa, duk irin rashin mutumci da Walidi yakewa mahaifiyar sa, a cewarsa ai itace ta jawo wa kanta, Washe baki yayi yana kallon Balaraba yace" "yar Albarka, sannu da kokari, kinji ko ki cigaba da hakuri damu, ni dai nasan ban miki wani laifi ba, sabuda haka zan tafi gurin me shayi, yanzu" Balaraba ta gane munufar sa, sabuda haka sai tace" Kawu kai ma yau sai dai kayi hakuri, domin bani da kudin da zan baka yau da gobe kayan Allah" Murtuke fuska yayi, ya hau zuba mata ruwan ashar, yace"wato nima
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108