Skip to content

Chapter 35

Chapter 35

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,254 words 0 views Progress saved
Download Book

tayi bata ce komai ba, "Tuba nake gani tun misalin bakawai ina nan ina zaman jiran ki nazo in baki hakuri bisa laifin dan uwana yayi miki jiya" Ajiyar zuciya tayi, tace "Yusuf halinka daban da kai da dan uwanka" Murmushi yayi kamar yana kusa da ita, yace"Halinmu daya da dan uwana,shima dan dai baku fahimci juna bane, ta wani gefan ma yafi ni kyawun hali" "Hummm, yanzu dai ina kan hanya, ganin zuwa sai muyi maganar" bata saurari abunda zai ce ba ta kashe wayar, Tunani take wace hanyar zata bi domin ta dauki fansar abunda Sarki! yayi mata _Muje zuwa My Fans๐Ÿ˜˜_ *Comment* *Vote and Share* [11/07, 20:48] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation ๐Ÿ‘ธ๐Ÿป๐Ÿ‘ธ๐Ÿป๐Ÿ‘ธ๐Ÿป๐Ÿ‘ธ๐Ÿป ^^^^^^^^ _*GIMBIYA BALARABA*_ ^^^^^^^^^ ๐Ÿ‘ธ๐Ÿป๐Ÿ‘ธ๐Ÿป๐Ÿ‘ธ๐Ÿป๐Ÿ‘ธ๐Ÿป _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *ยฎREAL BINTU BATULA๐Ÿ‘„* *MARUBUCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*Zamani Writes Association*_๐Ÿค๐Ÿป _*DEDIGATED*_ _*TO*_ ```{RAHAMA ALIYU}``` *๐Ÿ…ฟ46* ```Bisimillahir-rahamanir-rahim``` Tun kafin ta futo daga Napep din ta zuge jakarta ta futo da niqabi ta rufe fuskarta sabuda ganin kasuwar ta soma cika da jama'a wataran har kusan faduwa take sabuda idanun jama'a Sai da takara jaddadawa Ashiru akan kar ya wuce shida da rabi na yamma, bai zo ya dauke ta ba,domin bata so ta dinga kai wa Magariba a waje. Duk da niqab din dake sanye a fuskarta hakan bai hana wasu gane ta ba, sabuda yanayin tafiyar ta, wasu suke gane ta, shiyasa bayan wucewar ta suka kama yi da ita, Wani Alhaji Musa yace"wallahi na rasa yadda zanyi in tunkari yarinyar can, sabuda mugun kwarjinin da take min,gashi Allah ya jarrabe ni da sonta kamar me" "Ai ba kai kadai ba" wanda yake kusa dashi ya fada, ya cigaba da cewa"ni kaina kwarjini take min,wallahi ina mutukar son tsarin jikinta, da yanayin tafiyar ta, yarinyar fa tayi sosai, matsalar kawai "yar talakawa ce" "Duk wannan ba matsala bace a gurina mutukar zan samu fuska a gurinta" Alhaji Musa ya fada, yana jan numfashi, yace"kwanaki da muke zancan ta da Alhaji dan Yaro, yake fadamin, wai Yusuf Maddibo ne yake neman ta,kasan Abokin Buba ne,shi kuma Buba kasan tare suke harkokinsu dashi,shine yake fada masa" "Ai kaji abunda nake fada maka,wallahi yarinyar matar manya ce,sosai amma in kaga zaka iya shiga bisimillah,amma fa zaka sha wulakanci, domin shi ma Yusuf din, dan kore ne a gurinta har yanzu bata karbe shi ba" "Duk wannan baya damuna,indai zan samu biyan bukata" Alhaji Musa ya fada, nan suka cigaba da tattauna maganar, Kafin ta shiga gurin nata sai da ta tsaya suka gaisa da Me kosai cikin mutumci, ta futo da dari biyar ta mika mata tace"gashi a rabawa yara kosai sadaka" Almajiran dake zaune gurin suka dinga murna da farin ciki, dama dakon zuwanta sukeyi sabuda sun saba kullum tana sawa a raba musu kosai, nan suka dinga godiya gami da fatan alkairi Anutse ta shiga ciki inda ta tarar da Su Hauwa'u suna ta kai wa da kawo wa komai tsaf duk wani costomas an bashi abunda yake bukata, sama-sama suka gaisa da su, fuskarta babu walwala, kullum haka takeyi sabuda bata son wani ya kawo wargi a cikinsu,can gefe guda ta hango Yusuf zaune cikin kujera, ya zuba mata ido,kamar zai cinye ta,fuskarsa dauke da wani kayataccan murmushi, da sauri ta dauke kanta, ta nai wa Hauwa magana, Reciptoin ta futo ta zauna kan kujerar ta, kamar ko da yaushe, tana kallon masu shige da fuce, a gurin. Ganin ta futa yasa Maddibo mikewa a nutse ya bi bayanta, mutanan dake gurin suka bishi da kallo, ganin dukaninsu a gurin suka taddashi,gashi ya mike ya futa batare da yaci komai ba. Zama yayi kujerar dake fuskantar ta fuskar shi dauke da murmushi har ila yau, yace"Ranki ya dade,barka da zuwa" Sakin fuskarta tayi tace"kai ma ranka ya dade,fatan ka tashi lafiya"? Bai yi tsammanin zata sakko da wuri haka ba, ganin yadda ranta ya ba'ci jiya, amma abin mamaki ko a fuska bata nuna masa ba,asali ma yau tafi kowane lokaci sakar masa jiki. Yace"Lafiya kalau, na tashi ke fa"? "Nima lafiya kalau" tafada tana yi masa wani kayataccan murmushi. "Hakuri nazo na bawa Gimbiya sarauniyar zuciya ta" Yafada yana wani karyar da kai, gwanin tausayi "Humm Yusuf kenan, wane hakuri zaka bani, ai kai ba kayi min laifin komai ba,wanda yayi laifi shi ya kamata yazo ya bada hakuri in ana so in huce, fushina" Ta karashe maganar tana wani fari da ido. Shiru yayi yana binta da kallo,cikin so da kauna, yace"Ayi masa afuwa,Gimbiya na ari bakinsa naci masa albasa, abunda yayi shi, shine yayi ni, A yafe masa" Girgiza kai tayi tana tabe baki tace"in kaga na hakura to sai dai idan ka dauko shi ka kawo min shi nan yazo gurina a karo na biyu,wannan zuwan nasa ya zama na bada hakuri ne, a gurinshi, shine kawai zai sa na hakura, Murmushi yayi yana gyada kai cikin zuciyar sa yace"lallai na kara tabbatar da cewar sarauta a jinin yarinyar nan yake,wato ta na nufi yaje ya dauko Sarki! a karo na biyu ya kawo mata cikin kasuwa, lallai lamarin Balaraba ya shallake tunanin sa, ko mutuwa zai yi baya tunanin Sarki! zai yadda yazo kasuwa gurin ta da zumar bata hakuri, sai dai idan zai rufe masa yaki fada masa gaskiya, amma domin ya nuna mata son ta dake cikin zuciyar sa na gaske ne, yasa yace"duk wannan me sauki ne, mutumi na zai iya zuwa ya baki hakuri kamar yadda kike bukata,sabuda dan uwana yana mutukar son abunda nake so" Harararsa tayi tana fari da ido tace"ni dashi wa kafi so"? Dariya yasa yana kallonta yace"matsayin ki daban, nashi daban, a zuciya ta, amma bari ki fara ganin naki matsayin a gurina" ya karashe maganar yana kokarin futo da wayarsa aljihu, A nutse tace"me zakayi naga ka futo da waya"? Kashe mata ido daya yayi ya sai ta Camara ta wayar shi ya hau daukar ta a hoto, Da sauri ta sanya hannu tana kare fuskar ta domin yayi mata bazata, "Kabari bana so dan Allah" tafada tana kauda fuskar ta. Sai da yai mata kusan goma sannan ya dai na Shan kunu! tayi tana dauke fuska tace"ka dauki hotana ba da yarda ta ba zakaje ka nunawa abokan ka su kalli munina ko"? Yana dariya kasa-kasa yace"babu wanda zan nunawa sai mutum daya" "Wanene shi" tafada cikin sigar tuhuma "Mutumin ki ne" Tabe baki tayi tace"har yanzu ban yadda da son da kake min ba har sai kaje ka kawo min shi nan sannan zan yarda da kai" Wayar shi yake latsawa yana murmushi yace"bari kiga Zahiri,kafin in kawo miki shi bari in kira shi a waya sai kuyi magana" Numbar Sarki! yafara lalube cikin wayar tasa Shiru tayi kawai tana kallon shi, duk layin da ya kira a kashe, na ukun ne ya shiga,sai da ta kusa katsewa sannan yaji an daga wayar, da sauri ya bude handsfree ya mika mata, Ta karbi wayar cikin basar wa Muryar shi taji kamar ta me bacci, yace"Assalamu alaikum" Gabanta ne ya fadi! jin muryar shi duk da kasa-kasa take bai hanata jin dadin ta ba, Cikin jarumta! tace"Amin wa'alaikassalamu" Jin muryar mace yasa shi sauri tashi zaune, dama a kwance yake a kan wata katuwar Sofa, Mamaki yake, me

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108