Skip to content

Chapter 76

Chapter 76

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,233 words 0 views Progress saved
Download Book

ido tace"Kice kawai Babanmu ya wulla kawai ki sha shagalin ki" Duka Uwa! Ta kai mata suka sa dariya tamkar wasu k'awaye,Allah yasa lokacin da suke wannan zancan Lantana ta tafi siyo kalanzir d'in futalar ta. Shamsiyya ta mik'e tana fad'in bari inje in kwanta wallahi duk jikina ciwo yake yi" Ganin tayi hanyar d'akin Balaraba na da yasa gaban Uwa! Ya fad'i tace"Ashe zakuyi rigima da Walidi domin wannan d'akin da kike k'okarin shiga ya dawo nasa. Shamsiyya tayi mata wani irin kallo tana fad'in aikuwa bai isa wallahi domin bazan iya shiga cikin zarni da warin kashi in kwana a ciki ba" Uwa! Tace"Mu da muke kwana a ciki me ya cimu, kin san halin Walidi sarai ba saurara miki zai ba" Shamsiyya ta juya tana bud'e Kofa tana fad'in "Sai kiyi kuma" Uwa! Tsoran fushin Walidi take domin yanzu kusan shine yake d'aukar nauyin gidan,Saboda ita yanzu duk jarinta babu ta karar dashi gurin Arrama, da siyawa Sallau magani, Sai Mabaruka ta dawo daga yawon tallanta watarar suke cin abunci da d'an abunda ta samo. Shamsiyya na bud'e d'akin Walidi ya shigo gidan cikin sallama...... https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*GIMBIYA BALARABA*_ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* ```MARUBUCIYAR``` *NANA KHADIJA* *YARO DA KUD'I* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* _*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_ _________________________ ```We are here to educate, motivate and entertain aur Reades``` _________________________ _*DEDIGATED*_ _*TO*_ _RAHAMA ALIYU_ ________________________ _Gaisuwar Ku daban ce, mutanan kirki, a gaskiya inajin dad'in addu'oin da kuke min Wallahi nagode sosai da sosai,Allah ya kara zumunci_ _______________________ *Takwara ta: Hajiya Binta Shitu* *Hajiya Indo Amadu* _Wannan pege d'in naku ne, kuyi yadda kuke so dashi, nice taku Binta Umar Abbale🤝🏻_ _______________________ _*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR RAHIM*_ *🅿88* Da sallama a bakinsa ya shigo gidan, ganin Shamsiyya yayi a k'ofar d'akinsa tana k'okarin bud'ewa. Da sauri ya k'arasa gurin yana fad'in "Ke mai zaki min a d'akina ne,? sai kace wacce kika bani ajiya zaki bud'e min d'aki,wai ni garin yaya akai ma na tafi na bar d'akin a bud'e? Ya k'arasa maganar tasa yana kallon Uwa! Cikin tuhuma. Diriricewa Uwa! tayi, baki na rawa tace" Yo in banda ka fad'a ma yanzu ni bansan a bud'e ka bar d'akin ba" Tsaki yaja ya juya yana kallon Shamsiyya cikin sigar rashin mutumci yace"Kinje kin gama yawon barbad'ar ki kin dawo gida zaki cigaba dai mana sace-sacen da kika fara ko" A hasale Shamsiyya ta juya kamar zata kai masa duka tace"Kayi k'arya in maka sata wallahi, Yo ina abun yake banza shashasha kawai Kai har wani kud'i ne da kai wanda za a sata d'aki duk kud'in cizo da kwarkwasa" "Kya k'araci sharrin ki dai ki matsa ki bamu guri banzaye masu mugun b'akin jini, duk sai an aurar da " yan matan unguwar nan kuna zaune a gida,saboda mugun bak'in halin ku" Tsabar bak'in ciki yasa Shamsiyya fashe da kuka tana kallon Uwa!tace"Kinajin irin cin mutuncin da yake min ko,kin ja bakin ki kinyi shiru" Uwa! Tace" Me zan ce miki ai na fad'a miki tun kafin ki tunkari k'ofar d'akin, kin san halin Walidi farin sani" Buge hannun ta yayi daga jikin k'ofar ya bud'e abunsa ya shiga yana fad'in, Balaraba dai ta huta da bala'in ku shegu sai ku k'araci bak'in cikin ku mutu" Rashin abunyi yasa Shamsiyya ta dunga k'unduma masa ashar! sai kace "yar maguzawa,yana jin ta yayi mata banza,ita kuwa sai sake fad'i take Cewar wallahi duk ranar da tayi aure Walidi yazo yace ya santa sai tasa and'aure shi, yana daga cikin d'akin yana mata dariya,domin shi yanzu d'aukar mahaukata yake musu ita da Mabaruka,ganin har yanzu sun kasa gane gaskiya, dama shi Iro ba'a sashi cikin lissafin mutane masu nagarta. Nan suka zauna har aka kira sallahar magariba mutan gidan suka fara dawo wa, Iya ta dawo daga gidan jikarta domin yanzu can take wuni saboda haihuwar da tayi,dake gidan babu nisa dasu. Ita kuma Sadiya Matar Kawu Maman, tana zuwa nany ne wata makaranta pravite tana d'aukar albashinta me tsoka, shiyasa bata da damuwa ta wanke goma ta tsoma biyar babu abunda ya dame ta. Uwa! Tayi tayi ta raba Sadiya da gurin aikinta Allah baiyi ba, ta k'ulla munafurcin da Sharrin duk Allah bai amsa ba,haka dai ta hakura amma tana bala'in jin haushin ace k'arshen wata yayi Sadiya ta shigo da kud'in ta, tayi cefane me kyau suci su sha ita da mijinta, ta zubo ko babu yawa ta kaiwa Lantana. Ita kuwa tai ya murna baki zai sauya abinci. Sai wajan goma da rabi Mabaruka ta dawo gidan hannunta nik'i-nik'e da manya-manyan ledoji, cike da fara'a ta zauna kusa da mahaifiyar tasu, wacce take ta washe baki tana k'okarin bud'e ledojin kana ganinta kasan tana cike da farin ciki yau zasuci kayan dad'i da alama Shamsiyya tayi sabon saurayi" Jin motsin Leda yayi yawa a tsakar gidan,yasa Lantana rarrafowa ta futo, domin taji sallamar Maburuka tabbas tasan ta kawo kayan dad'i, ilai kuwa tana futowa tayi arba da wata k'undumeniyar kaza gasashiya taji k'uli-kuli da tumatur da albasa,Uwa sai k'okarin kaiwa bakinta take. Lantana ta dunga washe baki tana fad'in Allah yasa banyi bacci kam,tun d'azu bacci yake so ya kwashe ni,Allah bai nufa ba" Zam tayi gefan Maburaka tana tai mata banbad'anci Mabaruka ta ciro cinya da hak'arkari ta bata, sannan ta bata robar yoghot guda d'aya, tace"Shikkenan na sallame. Ki tashi kije ki kwanta" Lantana ta mike tana. Fad'in "Ai ko baki fad'a 'yan nan, Allah ya bamu alkari" Babu wanda ya kulata a cikinsu duk suna can suna rubibin cin gasashiyar kaza me maik'o☺ Sai da suka kusa cinyewa sannan suka tuna da Sallau, Uwa! Tace"Wannan ragowar k'ashushuwan sai ku barwa babanku ki"? Shamsiyya tace"Wallahi ni har na manta ma dashi" Tab'e baki Uwa! Tayi ta mike tsaye tana niyar shiga d'akin take fad'in kin manta dashi ko na manta dashi, ummm". D'akin ta shiga,Mabaruka ta mik'e da Sauri,jiri yasa ta dafe bango sai da tayi minti biyu sannan ta d'an dawo dai-dai, cikin yanayin maye ta k'arasa bakin rijiya ta ja ruwa ta zuba a buta ta shiga band'aki. Lokacin da suka gama alfashansu da saurayin batayi wanka ba,ko da yake a cikin motarsa suka yi komai, babu gurin wanka dole sai ta dawo gida. *************** Yau sati biyu da rasuwar su Fiddausi mutuwar me Martaba kuma ta kasance sati uku,, Waziri ya saki jiki sosai kullum yana zama a fada sai dare yake tashi sosai ya jinjinawa Mak'asudu domin da yarjewarsa ya samu nasara, tun bayan mutuwar su Fiddausi Mak'asudu bai k'ara tsotsewa wani jini ba,ya bari ne k'ura ta lafa, amma yana sane da iya adadin mutanan da akai masa alk'awari. Komai yana tafiya dai-dai ta b'angaran Hajiya Kulu ita da yaranta, biyu daga cikinsu ma sun kaso auransu sun dawo gida, kullum sai su shirya su futa basa dawowa gida sai dare can,wani lokacin ma a can suke kwana. Hajiya Kulu kuwa kullum tana tare da k'awayenta "yan duniya sosai suke shek'e ayarsu Hajiya Kulu ta zama k'umgurmar " yar lesbian, sosai take jin dad'in harkar shiyasa take ganin babu wani dalili da zai sa ta tadaina more rayuwarta yanzu ta fara, k'awarta Hajiya ta Masu, itace take kawo mata "yan mata zuguda-zuguda. Sai ta biya ta kudi masu tsoka. Kuma

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108