Skip to content

Chapter 27

Chapter 27

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,249 words 0 views Progress saved
Download Book

kusa Maddibo,ta dinga kurma masa zagi babu ji babu gani, sai da tayi mai isar ta sannan ta juya ta koma cikin gidan tana jan kafarta suka ci karo da Balaraba tana kokarin futowa, Kaucewa tayi ta bata hanya a karo na biyu,ganin tana nema ta bangaje ta, tsayawa tayi ta na mata wani dan banzan kallo tace" Haka zaki kare,karuwa kawai" Murmushi Balaraba tayi kawai ta raba ta gefenta ta wuce tabar ta tsaye a gurin,tana cizon ya tsa taso ta tanka mata suyi kokawa kamar yadda suka saba shekarun baya da suka wuce. Can gefe ta hango Walidi tsaye da Wani mutum a tsaye,sabuda haka kai tsaye inda suke ta nufa cikin nutsuwa. Tunda ta fito ya nemi nutsuwarsa ya rasa har sai da Walidi ya fuskanta yayi saurin waiwayawa yana kallon bayanshi sai yaga Balaraba, washe baki yayi yace"Yallabai dama nace maka yanzu zata futo wallahi" Fuska a sake Maddibo yace"nagode Abokina" hannu ya mika masa,Walidi ya saurin mika masa nasa sukayi musabaha yana mamakin mugun sauki kai irin na Mutumin, Tun kafin takaraso ta fahimci Yusuf ne, (dan anace) sunan da tasa masa kenan, sam bata taba zaton zai nemi gidansu ba, lallai ta yadda yana sonta da gaskiya kamar yadda yake fada, Fuskarta babu yabo babu fallasa ta karasa gurin. Walidi yayi saurin wuce yana fadin "Yallabai a sauka lafiya, mungode sosai" Hannu kawai Maddibo ya daga masa,duk ya rasa nutsuwarsa,dalilin futowar Mutuniyar tashi, Anutse ta gaida shi, ya amsa yana mata wani kayataccan murmushi "Ya akai ka kawo kanka gidanmu"? kai tsaye tayi masa wannan tambayar. Murmushi ne dauke a fuskarsa yace" ke kin dauka son da nake miki na gaibu ne? duk inda kike zan biki wannan shine soyayyar gaskiya" Murmushi ne a kwance a kayatacciyar fuskarta, tace"gaskiya kam yau na yadda da kai dari bisa dari" Wani dadi gami da farin ciki ne suke ratsa zuciyar Maddibo,jin abunda tace, sam bai yi tunanin zai shawo kanta da wuri haka ba, "Alhamdulillahi Gimbiya ta, yau ranar farin ciki ce a gurina,nagode da tarbar da kika yimin" Shiru kawai tayi tana sakar masa murmushi mai kayatarwa. Gyaran murya yayi yana kallonta yace"tare muke da dan uwana kuma abokina aminina, yana can cikin mota, kizo muje ku gaisa dashi" Wani irin kallo Balaraba tayi masa, tace"kamar yaya inzo muje mu gaisa,shi bai isa yazo nan din ba kamar yadda kazo har sai an bishi inda yake" A nutse yace"Mutumin nawa ne akwai tsirfa, baya son hayaniya, kinga yanayin unguwar taku" ya karashe maganar yana son boye mata abunda yake da akwai,dan a zahirin gaskiya bazai iya futowa ya fada mata kyamkyamin ne ya hanashi zuwa inda take. Shiru tayi tana nazari, a cikin zuciyarta, a yanzu Maddibo ya wuce wulakanci a gurinta,mutumin da ya tako yazo har inda take duk da tarin arzikin da yake dashi,ita sam bata san yana da alaka da sarauta ba tunda bai taba fada mata ba,wannan dalilin ne kawai zai sa taje har inda abokinsa su gaisa kamar yadda ya fada din, baya ga haka kuwa, bai isa ta taka taje har inda yake ba. A nutse ta kalli Maddibo tace"Muje kawai amma fa sabuda darajar ka, zani har mu gaisa dashi dan gaskiya ni babu wani mahalukin zai nuna min isa da mulki, idan ba mahalaccina ba" Fuskarahi a sake yace"godiya nake Gimbiya ta gidan Maddibo" Murmushi tayi tana wani fari da ido,suka jera a tare suna hira cikin fahintar juna, "yan yaran da Balaraba take rabawa naira biyar-biyar kullum in za tafita, suna zaune bakin hanya suna ta wasa, duk da dare ne kuma babu wadataccan haske,amma sai sa suka gane ta, nan suka rude," laaaaa Aunty Balarabamu, a dawo lafiya" "Allah yasa" Balaraba tabisu tana amsa wa babu kyara ballantana hantara! Wata katuwar Mota taga sun nufa, ga wanu mutum tsaye jikinta,jikinsa sanye da wasu jajayen kaya, irin na gidan Sarauta, cikin mamaki ta dinga bin Maddibo a nutse sam babu wata fargaba a tare da ita, Sarki! Yana zaune cikin mota yana danne-danne cikin waya ranshi yayi mugun baci! ganin yadda Maddibo ya bawa banza ajiyarshi yana can yana zance da budurwarsa ya manta tare suke,wato da ma dan ya wulakanta shi ne yasa yazo ya takurashi dole sai yayi masa rakiya,dole ya nuna masa bacin ransa,dan bazai yi zaman banza, cikin mota, sai kace mara abin yi" Kokarin bude motar yaji a nayi, sai ya gyara zama a nutse ya sanya hannushi ya bude motar ta ciki sabuda ya sanya mata sucurity dole sai shine zai bude, Shan kunu! yayi domin yasan Maddibo ne, ya bude motar kawai ya dauke kansa, ya mayar da hankalinshi kan wayar dake hannusa Balaraba na tsaye a bayan Maddibo duk taga abunda yayi, so take ta kalli fuskarsa, sosai babu haske sai hasken wayar hannunshi, Cikin Dariya Maddibo yace"Mutumina kaji ni shiru ko, kasan halin Gimbiya tawa sai a hankali" A fusace! Sarki! ya dago kanshi ya watsa masa wani kallo,kana yace"kaga Malam abunda ya dame ka ne wannan, dan tsabar rashin mutunci ka tafi kabar mutane zaune a cikin mota kamar wasu marasa abunyi, dubi time fa" Yafada yana kallon haddadan agogon dake daure a hannushi, ya cigaba da cewa"tun misalin takwas da kwata duba fa sai yanzu ka dawo tara da minti ashirin da biyar, duk irin zancan da zakuyi da kai da "yar towo-towon naka ai yaci a ce ka tuna dani,tunda dai ni ba banza bane da zaka shanya ni kamar wani shashasha" Ya karashe maganar cikin masiba! Tunda Ya fara magana gabanta ya dinga faduwa! ko cikin mafarki taji wannan muryar baza ta taba mance da me ita ba, Sarki! ne Yariman Sarki Almustapah Maimarta ba sarkin garin nasu mai adalci, gabanta ya cigaba da dukan uku-uku jin sunan da yake kiranta dashi, wai "yar towo-towo. *Muje zuwa* *Comment* *Vote and Share* [05/07, 12:57] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† _*GIMBIYA BALARABA*_ βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ†βˆ† πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ»πŸ‘ΈπŸ» _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *MARUBCIYAR* ```Nana khadija``` ```Yaro da kudi``` ```Gimbiya Balaraba``` _*Zamani Writes Association*_🀝🏻 ```Bisimillahir-rahamanir-rahim``` *πŸ…Ώ38* *Real Bintu Batula*πŸ‘„ Rai a bace Maddibo yake kallonsa, jikinsa duk yayi sanyi jin irin bak'aken maganganun da Sarki! yake ya wa Balaraba, kwata-kwata ya rasa me zai ce masa, kallon Balaraba yayi jiki a sanyaye ya bude baki zai yi magana, tayi saurin tararsa,fuskarta babu yabo babu fallasa ta kalleshi a nutse tace"Kar ka bata ranka a kan abunda abokin ka ya fada a kaina, tabbas kamar yadda ya fada cewa ni "yar bakin kasuwa ce,haka abun yake, duk da nake " yar towo-towo ban taba nema a gurin uban kowa sabuda haka babu wani mahalukin mutum da ya isa yazo har kofar gidanmu yace zai ci mun mutumchi in kyaleshi komai kudinshi da mulkinshi wallahi" A nutse ta kalli Sarki! dake zaune cikin mota yana jin duk abunda take cewa kwata-kwata bai yi mamakin jin abunda tace, Sabuda tun da tafara magana ya gane ko wacece, tabbas muryarta baza ta taba bace masa ba. Wayarshi ya ke dubawa amma hankalinshi na kanta, duk da cewa a kwai duhu a gurin hakan bai hanashi kare mata kallo ba, ta kasan idonshi. Cikin isa da gadara Balaraba ta kalleshi shekeke! tace"Idan ka isa kai wani ne ka aje wayar muyi magana da kai, bari kaji

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108