Chapter 107
Chapter 107
sai kice ni in zama silar shi." Kuka ya fara yi sosai harda sharb'ar majina." Yace." Meye abun kuka, kuma." Tace." Ina jin takaicin yadda wata zata fara haihuwa dakai bani ba." Tsaki yaja yana girgiza kai yace." Matsalata dake rashin wayo da dubara ni dake da balaraba babu Wanda ya Isa ya hana Allah ikonsa akanmu Balaraba zata fara haihuwa dani haka Allah ya tsara.'' Kuka sosai takeyi takasa cewa komai ta kwanta kan bed din tana Jan ajiyar zuciya, tausayinta ne ya kamashi,ya kashe futal dakin tare da aje k'aramin littafin hannunsa ya rungume ta yana fada mata daddadan kalamai, nan labari ya sha BABBAN, na futo na barsu ina fatan samun nasara da 'yaya masu albarka. To sarki! Ya biya Halisa domin dai jiya ya kashe ta da soyayyar sa mai wahalar mantawa lokaci kad'an ta manta da damuwar ta,ta cigaba da kyautatata masa. ****** Tsito ne ya dura a gidan kamar tsohon mahaukaci ya nufi b'angaran Hajiya Kulu me dakin kudu, yazo domin ya karb'i sauran kud'in aikin sa. Nan ya samu babu. Kowa a shashen nata sai hadiman ta, suka ce masa satin ta biyu bata gida,hakanan yaranta suma ba kullum suke kwana a gida ba, haka ya futo yana tunanin ina zashi,domin yanzu duk aljanun da suke kanshi sun dare sun gudu baya iya yin aikin komai watarana ma da yunwa yake kwana, ya tabbatar da cewa abunda suka aikata da Waziri ne ta shafe shi, zuciyarsa ta bashi shawarar kawai yaje ya nemi afuwar iyalin Waziri ko Allah zai sa ya gama da duniya lafiya, sannan suyi masa iso gurin Sarki! Almansur domin ya nemi gafarar sa Halin da yaga Waziri a ciki ya bashi tsoro bakinsa ya dinga rawa ya rasa abun cewa,Hajiya Kattime tace." Bawan Allah daga ina haka domin banga ne ka ba."? Tsito ya fashe da kuka yana fad'in." Yanzu haka Waziri ya koma oo ni Tsito." Kattime tace." Kayi min bayani mana, yace." Nine Tsito wanda nayi ma mijin ki aiki duk Dan yayi mulki nan ya warware mata duk abunda ya faru, yaran ta suka taso domin suyi masa duka ta hanasu, tace." Ku kyale shi shima zai ga karshen sa, nan Tsito yayi dasu su masa iso gurin me Martaba Kattime ta hana, haka suka tarkatashi suka futa dashi fadawa suka tasa keyarsa har waje, yana futa ya kasa gane hanya kawai sai ya dauki wata haya ta daban yana tafiya yana tsayawa bola-bola yana tsince-tsince duk ledar da ya gani sai ya d'auka ya sa a bakinsa yana taunawa. *Ubangiji Allah kasa muyi kyakyawan k'arshe* ******* Kwana biyu da Halisa tayi ta samu kulawa sosai a gurinsa ganin yanda ta kwantar masa da kai tana kula dashi komai sai tace idan BALARABA ta haihu za'ayi kaza da kaza, hakan ne yasa ya Sakar mata jiki suka sha soyayya. Azima ya ta karb'i girki sai girin gidishi take tasha magunguna mata kamar banza mararta sai kullewa take jira kawai take dare yayi ta shiga part din Yallab'ai a kashe boss. ***** Hajiya Kattime ce tayi sallama ta shiga a nutsue Mama ta amsa Jakadiya ta gyara mata gurin zama,sannan ta futa ta basu guri, Kattime ta gyara zama tana fadin ." Fulani magana nake tafe da ita." Mama tace." Ai tunda naga fuskar ki nasan akwai magana." Kattime tace." Wallahi kuwa, jiya na samu wani labari da bakin da ya fada min bazai k'arya kai asalima shine ya asassa al'amarin." Mama ta zuba mata ido, Kattime ta cigaba da cewa." Kin san Azima da ita aka had'a baki gurin cutar da Almansur." Mama ta mike zaune sosai tana kallon ta cikin mamaki! Kattime ta cigaba da cewa.' Jiya Tsito mashirikin da yayi aikin yazo ya warware min komai, saboda haka Nazo na fada miki auran Azima da Almansur dama da wata manufa aka had'a shi don haka ki umarce shi da ya rabu da ita tun wuri." Mama jikinta yayi sanyi sosai da sosai tace." Dama ni kaina banyi na'am da wannan hadin ba wallahi oh! Mugu bashi da kama yanzu Azima itace ta bawa yarona guba yaci domin ya nakasa."? Kattime tace." Kina mamakin wannan duniyar wallahi." Mama tace." Yanzu zan sanya ayi min kiran su ki zauna a gaban ki za'ayi komai, Jakadiya ta kira ta umarce ta ta kira mata Azima da Halisa BALARABA Wayar ta ta d'auka ta kira uban gayyar, suna tare da me girma governor suna shirye-shuiyen yanda za'a gudanar da nadin sarauta,domin an tsai da rana jama'azuwa ,Yaga kiran Mama a nutse ya d'auka tace." Kazo yanzu shashena." "Insha Allahu ganin zuwa." Ya fada yana kashe wayar. Sallama sukayi da governor suka futo tare me girma ya shiga mota tare da mutanansa shi kuma ya. Nufi shashen Maman shi tare da jama'ar sa, duk suna zaune suna jiran isowarsa yayi sallama ya shiga duk suka amsa, matansa na rige-rigen gaishe ya amsa mu a nutse ya zauna, yana gaida Maman shi tare da Hajiya Kattime, Fulani tace." Kattime yi musu bayani da bakin ki." Nan Kattime ta fara fada masa duk abunda ya faru tun daga farko har k'arshe da manufar Waziri akan auransa da Azima. Nan take Sarki! Ya tuno da ranar da ya shiga gurin Azima da daddare har yayi Tara da ita tunda lokacin nan ya tashi da wannan ciwo, Azima tayi tsuru-tsuru tuni hawaye ya soma ambaliya a fuskarta tayi da tasani yagi cikin kwando shikkenan yanzu tasan karshen zamanta dashi ya kare ganin yadda ransa yayi mugun b'aci, shiru farlo na minti biyar yayi gyaran murya yana goge gumn da ke tsatsafo masa, yace." Mama ki gafarce ni, da abunda zan aikata yanzu hak'ika zama da Azima babbar musiba ce saboda haka na sawwake mata igiya guda taje in ta samu miji tayi aure." Yana gama fadin haka ya mike ya futa zuciyarsa babu dad'i. Babu Wanda yace komai cikinsu,Azima ta dunga kuka tana rokan Mama ta sanya shi ya janye sakin Mama tayi shiru da rarrafe taje ta rike k'afafun Halisa tana rokonta Halisa ta fuzge kafarta tana maka mata harara tace." Wallahi na tsane ki Azima muguwar azzalima kawai." Cikin kuka Takarasa kusa da Balaraba tana rokonta wai tabawa Sarki hakuri Balaraba tayi shiru kawai tana Mamakin halin Dan Adam. Fadawan dake waje mama ta umarta tace su futa da Azima kuma su tsaya kanta ta had'a duk wani ko matsanta ta kama gabanta. Aikuwa haka akayi aka tasa Azima a gaba har garin su. ******** ππ£π£π£πππππ’π±π±π±π±π±πΆπΆπΆπΆπΆπΆπΆπΆπΆππππππππππ₯π₯π₯π₯π₯π₯π₯π₯π§πΌββπ€΄π»π€΄π»πΈπ»πΈπ»π€΄π»π€΄π»π€΄π»π€΄π»π€΄π»π€΄π»π€΄π»π€΄π»π€΄π»π€΄π»π§πΌββ *Rana bata karya* Yau juma'a uku ga watan uku, yau aka gudanar da shagalin nadin sarauta. Wannan nad'i ya samu halartar dubban mutane kama daga shugabanin kasa she,governor ni shahararun malamai da limamai da shahararun 'yan kasuwa duk sun samu damar halarta nad'in sarautar Sarki! Almansur YARO me dattako me halin manya me nagarta da sanin abunda takeyi kowa na masa fatan alkari tare da jagoranci me cikin adalci, lokacin da ake gudanar da wannan nad'i Waziri na kwance yana zurarar da hawaye duk an d'ad'e an barshi shi kadai kuka yake tukuro gami da nadamar abunda ya aikata,, labari ya riske cewar ga Almansur can an mik'a masa sandar mulki, ihu!!! Ya kurma yana buga kansa a bango nan take ya futa daga hayyacinsa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108