Chapter 91
Chapter 91
gudu tunda taga inda ya aje mukullin,, yanzu daga ita sai briz da wando, hawayen bak'in ciki take sharewa, tana tunanin yaya za tayi yanzu. Lullube jikinta tayi da bargo har fuskarta,, tana jin motsin futowar sa daga toilet d'in tayi shiru abunta har yanzu ba ta daina hawaye ba Shirya jikinsa yake yana satar kallonta ganin ta rufe fuskarta,, ko motsi ba tayi,, a tsakana ke ya shirya tsaf Cikin shigar sa ta ko da yaushe wato kayan su na sarauta, turaren shi ya fesa tas dashi kana kallon shi kasan yana cikin walwala da farin ciki,, har inda take ya k'ara ya tsaya a kanta kusan minti biyar yana nazarin ta. Duk da take lullub'e tasan da mutum a tsaye a kanta,, jikinta ne ya fara d'aukar zafi, gyaran murya yayi gami da fad'in"jimana" Banza tayi dashi ba tan ka masa ba Zama yayi kusa da ita yana Jan bargon, ta rik'e da kyau, "Wai meye haka kike ne ? Sai kace wata " yar k'auye uhumm? Ki tashi ki kimtsa jikin ki ni zan fita" K'in kula shi tayi, sai shashekar kukan ta da yaji,, yasa jikinsa yin sanyi yace"Kuka kike"? A sark'e tace"Ba dole nayi kuka ba haba wannan abun takaici duba fa yadda ka b'ata min jiki da kaya na, yanzu wane kayan zan sanya"? Fuskarta a lullub'e take maganar. Sai yanzu ya fahimci yayi kwab'a rigar ta ya d'auko yana dubawa,aikuwa duk ta b'aci,,, bai CE komai ba ya mike tsaye had'e da cire alkyabar dake jikinsa kai s.tsaye toilet ya nufa da ita, da kanshi ya bude injin wanki ya sanya rigar ya wanke mata tass ya busar da ita,, hannushi rik'e da rigar ya futo daga toilet din ya tsaya kanta yana fad'in "Tashi gashi na wanke miki" Cikin mamaki ta bud'e fuskarta tana kallon shi,, aikuwa rigar ta gani a hannushi da alama kuma a wanke take, hannu ta ziro ta karb'i rigar tana dubawa,, kallon ta yake fuskarsa babu yabo babu fallasa, ita kam mamaki take wai da kanshi ya wanke mata Riga,tarasa gane wane irin hali ne dashi,, K'asa-k'asa tace"Ka matsa daga kaina to zan sanya rigar" "Baki Isa ba" Yafad'a kai tsaye ya cigaba da cewa "Ki tashi kawai kije ki tsarkake jikin ki sannan. " Babu fa kaya. a jikina fa" Tafad'a jikin haushi. "Eh na sani" Yafad'a yana zama kusa da ita,, yana fad'in "Ko ki tashi ko nayi me gaba d'aya, babu abunda akai miki kin lanjare, ita Azima ai jaruma ce" Haushin abunda yace yasa ta mike a fusace daga ita sai k'aramin wando da briz ta nufi toilet d'in da gudu... .. Domin tana ganin ta tsaya sanya zai kalle mata jiki 😃 Ni ko nace Balaraba kenan yanzu ma ai ta kalle miki duk wayon ki Sarki! Ta fiki" Dariya yake sosai bayan shigar ta ya mike a nutse ya sauka k'asa.Lokacin da ta futo baya d'akin cikin sauri ta sanya kayan ta, ta sauka k'asa,, yana zaune kan kujera da waya a kunnen sa, da alama waya take, da sauri ta nufi k"ofar futa tun kafin ya gama wayar ya b'ullo mata da wata tsurfar,, ba zato taji yace"Jirani mana mu tafi tare zanje mu gaisa da Mama" Da sauri ta futa ba tare da taji karshen maganar tasa ba,yaya ma za'ayi ta jera dashi ga mutane da dama ai da kunya,, yanzu ma bata San abunda zata cewa Mama ba in ta koma. ******* Shamsiyya kuwa kullum tana tafe a hanyar gidan Arrama ba ta dawo wa sai dare, sai sun gama sha'aninsu kullum yana fad'a mata ta kwantar da hankalin ta, kamar ta auri Sarki ta gama ne,, Uwa yau da bakin ciki ta tashi a gidan kasancewar ko ina ta juya babu dad'i gashi bata da ko kwabo yanzu bata sai dai komai duk jarin NATA ya k'are gurin bin malamai da bokaye,, Tsarkar gida ta futo tana ta surfa bala'i ta zauna kan kujera sai durawa Lantana ashar take tana fad'in"Ban tab'a ganin tsohowar najadu ba irin wannan matar kiri-kiri ta gudu ta barni da wahalar jiyyar danta shegiya munafuka Ashe da ta karb'i asirin domin taje ta aiwatar ba abunda ya kai ta bane, to Wallahi yau sai naje na tona mata asiri a gidan,wai ni zata munafurta shigiya tsohuwar najadu" Sallau na daki yana jin Uwa na zagin mahaifiyar shi bakin ciki kamar ya kashe shi,,, cike da taikaci yace"Uwa!! Yanzu Lantana kike zagi? itama fa a matsayin mahaifiyar ki take"" Cikin masifa tace"Rufe min baki mutsiya ci kawai Uwata ko uwarka ni wannan munafukar matar bata haife ni me halin "yan wuta" Wani mugun tari ne ya sark'e Sallau yana daga hannusa guda yana son yayi magana ya kasa da k'yar yace"Uwa!ke ba matar rufin asiri bace kije na sake ki saki uku tunda kika zagi mahaifiya ta" "Ahayye nanaye"!!! Ayurrrrrr" Yau Allah ya raba ni da k'aya mutan gida Ku futo Ku taya ni murna" Sadiya da Iya duk suna jin abunda ya faru sukayi shiru suna mamakin abunda dama ya kai Lantana gidan sarauta duk Dan ta cutar da Balaraba ne, Allah yasa Allah ya tona mata asiri.. Iya bata tsinke da al'amarin ba sai da taji Sallau na fad'in ya saki Uwa saki uku sannan ta futo daga daki tana salati gami da fad'in "Assha Sallau ka yanke hukuncin da bai dace ba, Sallau ba a saki cikin fushi" Sallau ya fashe da kuka yana fad'in "Dole In rabu da Wannan bak'ar dagar matar Atika kina ji fa tana zagin Lantana duk lalacewar ta mahaifiyar ta CE kuma itama ta haife ta tunda dai yar uwarta ce" Iya tace"Duk da haka dai, hukuncin da ka yanke bai dace ba" Uwa! Ta futo daga daki Cikin shiri tana fad'in "Duk naji abunda kake cewa munafuki me kashi a kwance akwai bak'ar daga irin uwarka me muguwar zuciya kawai wallahi yau sai na tona mata asiri a gidan Sarki yanda ka ganni nan a shirye nake" Waje ta futa kamar sabuwar mahaukaciya sai surutai take, Iya da Sadiya suka bita da kallo cikin mamaki. Tana futa Sallau ya dunga wani irin tari Wanda I n yayi sai wata majina ne kauri bak'ak'irin ta futo daga bakin sa, ga wani uban wari da take,, DA k'yar ya bud'e bakin sa yace"Atika ki yafe mun abubuwan da nayi muku ke da "yan uwanki Wanda na sani da Wanda ban sani ba ki yafe min Wannan ciwon nawa bana tashi bane, hak'ika na aikata abubwa Mara kyau don Allah ki nema min gafara gurin Balaraba da duk Wanda na batawa jikina na bani mutuwa zanyi" Iya ta fara share hawaye tana cewa"cuta ba mutawa ba Sallau Insha Allahu zaka tashi kayi hakuri ka daina wannan maganar" Sallau yace"Kayya Atika ni nasan abunda nake ji hak'ika na zalinci Ayuba da matar shi da yarsu Balaraba don Allah ko na mutu Ku Bini da addu'a" Kuka iya take tana bashi hakuri gami da yi masa addu'a ta kalli Sadiya dake tsaye hawaye na zuba tace"Ki kira Maman a waya yazo su gana" Cikin dauriya tace"Kin manta "yau kwanan shi biyu da tafiya sun tafi Jalingo,zasu sauke kaya" Iya tace"Hakane kuma kira Walidi yazo ya kai shi asibiti jikin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108