Skip to content

Chapter 81

Chapter 81

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,217 words 0 views Progress saved
Download Book

sauke wata irin zazzafar ajiyar zuciya, kwata-kwata a "yan kwana kin nan, yana yawan jinta a cikin zuciyarsa, duk sanda ya tuna da cewar tayi mu'amula da maza ta shiga cikin kasuwa ta saida abunci,sai yaji wata irin kibiyar kishi ta soke, ranar sai ya yini yana kwance duk ransa a b'ace! Yana kishinta sosai da sosai. Kasa daurewa yayi yasa yayi mata maganar. *********** *********** *********** Lantana na bayan mota duk tayi tsuru-tsuru sai zare ido take, burinta kawai ta isa gidan ta ganta gata ga Balaraba sai ta fara gudanar da aikinta. 👸🏻👸🏻👸🏻 _*GIMBIYA BALARABA*_ 👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻 _*NA*_ _BINTA UMAR ABBALE_ *®BINTUBATULA👄* ```MARUBUCIYAR``` *NANA KHADIJA* *YARO DA KUD'I* *GIMBIYA BALARABA* *TSANTSAR BUTULCI* _*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_ _________________________ ```We are here to educate, motivate and entertain aur Reades``` _________________________ _*DEDIGATED*_ _*TO*_ _RAHAMA ALIYU_ _*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR RAHIM*_ *🅿93* Kai tsaye shashen Mama Fulani suka nufa,, bayan Buba yayi parking d'in mota suka futo cikin nutsuwa, Buba ya bud'ewa Lantana k'ofa ta futo daga cikin motar sai zare ido takeyi ganin wasu irin mutane manya-manya a shashen Mama Suna kaiwa suna kawowa kuwanne jikinsa sanye da kaya jajaye da k'aton ta wani, gefanta ya kalla taga wani tsaye hannusa rik'e da k'atuwar bulala sai zare ido yake ga idanunsa sunji kwalli rabad'au, saurin d'auke kanta tayi tana k'ara damke abunda yake hannunta. Ganin suna ta zubewa k'asa suna gaidasu Shatima ne yasa ta shiga taitayinta, ta dunga bunsu a baya simi-simi har suka shiga falon a tare. Lantana ta tsorata da ganin irin had'uwar falon Mama Fulani ko ina ta kalla sai taga kalarshi daban, ga kayan alatu na jin dad'i da more ta yuwa, wani irin mugun kamshi me dad'i yana shiga hancin ta. Tun daga bakin Kofa ta zube tana gaida Mama. Cikin mamaki Mama Fulani tace"Bisimilah mana ki shigo daga ciki sai mu gaisa sosai" Da k'yar Lantana ta mike ta isa kusa da Mama Fulani ta zauna a k'asa sai washe baki take. Tana fad'in "Ranki shi Dade ashe ina da rabon ganin ki a duniyar nan, ashe jinina zai had'u da jininku,gaskiya nagode Allah nagode Muhammadu rasililahi" Mama tayi murmushi kawai tana kallonsu Shahid nan yayi mata bayanin Lantana Cike da farin ciki ta kalli Lantana tana fad'in "Gaskiya naji dad'in zuwanki sosai,dama nace aje a sanar daku halin da ake ciki,Gobe insha Allahu bayan d'aurin aure zan tura a d'auko sauran mutanan gida suma suzo ayi hidimar buki dasu" "Lantana tace" Ai naji dad'in wannan abu ranki ya Dade nace Ashe da rabonmu muma zamuci arziki mu bar shi inda yake, haihuwa tayi mana rana" Murmushi Mama tayi batace komai ba. Su Shahid suka mike. Inda Shatima yake tambayar Sarki! Mama tace"Ya koma Shashen sa. Sallama sukai mata suka wuce Shashen Sarki! Lantana ta dunga b'arin jiki sai zuba take tanaiwa Mama labari,tace"Ina angon namu yake ne yazo ya zab'a ko ni ko ita" Mama bata iya surutu ba saboda ba d'abi'arta b'ace,gashi bata San wulakanta mutum sai ta dunga biyewa Lantana kawai domin karrama ta. Jakadiya Shafa'atu ta shigo suka gaisa da Lantana, nan Mama take sanar da ita cewar kakar Balaraba CE,Jakadiya ta kara gaida Lantana cikin girmamawa, Mama tace, taje ta kira Balaraba dasu Sadiya su gaisa da kakarsu sannan Balaraba ta bata abunci, Sadiya da Usuman ne a gaba kafun Balaraba, da sauri suka ja tunga suka tsaya ganin Lantana a gurfane gaban Mama sai surutu take sai kace wata tsuhuwar redio, Sadiya ta juya da sauri zata koma suka ci karo da Balaraba tayi saurib tare ta tana tambayar ta menene"? Bakinta na rawa tace"Yayarmu Lantance" Da sauri ta kalli inda Sadiyar take nuna mata, Lantana ce, kuwa hankalinta na kan Mama basu ga futowar su ba, fad'uwar gaba taji, tana mamakin me ya kawo Lantana gidanan,, wata zuciyar tace mata kika sani ko Mama ce tasa aka d'auko ta. Da kuzari a jikinta ta nufi inda suke, Binta sukayi a baya suna cike da tsoran abunda zai faru Usuman addu'a kawai yake a cikin zuciyarsa Allah yasa Lantana kar ta gudu dasu shikam yaji dad'in zaman gidan nan. Lantana na hango Balaraba ta mike da sauri zaninta ya fad'i ta d'auka da sauri ta d'aura taje ta rungume Balaraba ta fashe da kuka tana fad'in "Ashe kina nan Balaraba, munyi neman duniya bamu ganki ba,Shima Sallau da k'yar ya koma gida ranar ashe alkairi ne a tartare dake Balaraba" Wasu irin sambatu Lanatana ta dunga yi Mamaki ya kama Balaraba sai ta rik'e ta ta zaunar da ita tana fad'in ki zauna mana, don Allah ki nutsu sosai sai muyi maganar. Ita dai Mama tana kallonsu cike da mamaki Jiki narawa ta zauna tana hawo hannun Usuman yana fuzgewa yana komawa bayan Balaraba, Tace"Zo nan Sadiya mu gaisa" k'in zuwa tayi yarinyar. Fashewa da kuka Lantana tayi cike da munafurci da kitifi tace"kinga abunda nake fad'a miki ko Balaraba, dubi wai jina ne yake guduna duniya kenan" Balaraba na jinta tasan dai makircin Lantana,, tace"Ki nutsu nu gaisa mana" Jikinta na rawa ta hau gaida Balaraba, amsawa tayi kawai tana kunshe dariyarta ita Abunda Lantana take ya soma bata mamaki wallahi. Mama kanta ta fuskanci rashin gaskiya gurin Lantana. Da k"yar ta hillace ta suka nufi gurin cin abunci Lantana taka tunga ta tsayawa wai baza ta hau kan daining ba, haka ta had'a mata ta kai ta aje mata can wani k'ebabtaccan gurin Cin abunci take kamar wata jaka babu kamun Kai babu komai, Mama Fulani na daga gurin zaman ta tana kallon ikon Allah, Balaraba kuwa wata irin kunya ce ta kamata, a hankali tace "Lantana kici a nutse mana" Ko saurarenta batayi ba,sai da ts cika Uwar hanjinta da kyau sannan ta tsame hannuta tana goge bakinta,,, Mik'ewa tayi ta koma falo kusa da Mama Fulani,,Tsaki Balaraba taja tana d'auke kanta,tanajin Lantana tana cewa Mama wai tana so ko bayan biki ta zata zauna anan" Mama Fulani tace"Ai babu komai sai ta zauna d'in. Mama Fulani dai shiru tayi musu ita da Jakadiya suke hira itama da tagaji sai tao shiru ta k'yaleta,, sai banbadanci takewa Fulani. Mintu ashiri Mama ta kara a gurin ta mike tsaye tana musu sallama domin zataje ta kwanta, nan sukai mata sai da safe, ta shige d'akinta, Jakadiya ma sallama tayiwa Lantana ta mike ta nufi dakin kwananta. Balaraba ta kalli Lantana da rai a b'ace tace" Ai sai ki tashi haka muje ki kwanta, wai don Allah meyasa kike haka ne"? Lantana ta hau yak'e tana fad'in "Me na aikata " yar nan, baki San su irin wannan mutane dole sai kana musu banbad'anci ba" Tsaki taja tana fad'in "To banda wannan masarautar ta masu hankali ce,don Allah ki dunga nutsuwa kar ki bani kunya gurin abokan zamana da mutanan gida" Lantana tace"To naji zan kiyaye ai kina da damar da zaki fad'a min duk irin maganar da kike so, saboda Kinga zaki auri Sarki! "Shiru kawai tayi mata tana surutai a cikin zuciyarta take fad'in ko wannan auren ya dama,ni a gurina sunan shi auran biyayya. *********** *********** *********** *Komai yayi farko yana da k'arshe* Cikin shiri sosai suka futo daga shashinsa gida ya cika ya tumbatsa baka jin komai sai busa da sarewa irin ta gidan sarauta, marok'a da magogo

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108