Skip to content

Chapter 75

Chapter 75

Gimbiya Balaraba Book One Complete Hausa Novel 1,224 words 0 views Progress saved
Download Book

ki zuba musu ruwa, gawa ba a zuba mata ruwa" Ihu! Kulu ta kurma ta mik'e tsaye a zabure! tace"Au! Ashe da gaske sun mutu? Wayyo na shiga uku na lalace ni Hauwa Kulu" Waziri ya tsuguna yana duba gawar su Fiddausi cikin zuciyarsa yana tunanin shi kuma a cikin "yayansa ko suwa Aljani Mak'asudu zai tsotsewa jini oho. Ihu kawai kake ji a b'angaran Hajiya Kulu babu me salati a cikin mutanan ta, lokacin k'ank'ani mutuwar su Fiddausi ta watsu a gidan, Ihun da Hajiya Kulu take ne ya b'atawa Sarki! rai kawai sai ya fuce daga shashan cike da b'akin ciki da damuwa. Wannan al'amari ya tayarwa da kowa hankali, Mussaman Sarki!, Cike da damuwa a kai wa su Fiddausi suttura aka kaisu makwancin su, bayan an dawo daga makabarta Waziri ya shige fada ya zauna kan kujera tare da jama'rshi,, kafin kace kwabo "yan zaman makoki suka fara gulma,har da masu zuwa inda Sarki! Yake zaune suna fad'a masa ga Waziri can a fada bayan kuma Governor yace" Kujerar ta shi ce. Sarki! Yace"Suyi hakuri su kyaleshi tukkuna a kwana biyu komai zai dai-dai ta, dama shi Galadima baya goyan bayan Waziri shiyasa basa shiri sosai, yanzu ma yana kusa da Sarki! Suna karb'ar gaisuwa. Bayan sadakar uku Hajiya Kulu Duniya sabuwa saboda a yanzu kud'i baya yanke mata motsi kad'an zata sa a kira mata Sarki! Tace zata ciri kud'i dole ya bata, ko yak'i ko ya so, watarana in ta umarshi da yayi Abu baya sab'awa umarnin ta,, Mama Fulani kuwa duk dan a zauna lafiya take k'ara tursasahi idan ya bujirewa bukatar Kulu wataran. ******* Sati biyu da rasuwar su Fiddausi, su Latifa da Iklas sauran "yan matan dake gaban Kulu kenan,suka fara rigimar dole a raba musu gado suna so su fara kasuwanci,nan Hajiya Kulu tasa ai mata kiran Sarki! kan buk'atar " yayanta. Bayan Sarki! Ya gama sauraron maganganun Hajiya Kulu kan rabon gado,sai yace mata ta kwantar da hankalin ta insha Allah za'a raba a cikin satin nan, yayi mata sallama ya tafi, yarasa me yasa idan yana gabanta baya iyayin katab'us. Limamai da shedu ya Tara kan rabon gadon akayi shi cikin adalci inda Sarki! Ya tashi da kusan rabin dukiyar me Martaba had'e da kadarorinsa, a matsayinsa na Namiji matan ma aka basu abunda Allah ya sharanta,, bak'in ciki kamar ya kashe Hajiya Kulu dan haka a daran ranar ta nufi gurin Tsito domin ta nemi shawarar yaya za'ayi. Tana zuwa Tsito ya bushe da dariya yana fad'in dama nasan kina tafe ai" Kulu ta zauna tana sauke nuffashi tace"Dole inzo gurinka domin ka had'ani da Mak'asudu yanzu anyi rabon gado komai yaron nan ya kwashe mu mun tashi a tutar babu" Tsito ya kece da wata mahaukaciyar dariya yana fad'in gaskiya Hajiya kina dan son kud'i sosai, Mak'asudu na jin ki kuma yanzu zan had'aki dashi" Ai kuwa Kulu ta gyara zamanta Mak'asudu ya hauro ya fara magana kamar haka" Kinzo kan wannan yaron Wanda ya tsaya miki a zuciya ko"? Kulu ta d'aga kai, yace"Kije kawai zaki samu yanda kike so akansa ko yau kuka karar da dukiyarku, daga zarar kin tambaye shi kud'i zai baki jikinsa na rawa" Kulu ta dunga godiya sosai Aljani Mak'asudu yace"Ki kawo min k'wai d'anye goma sha d'aya yanzu zan sha" Kulu ta mik'e da niyar tafiya tana fad'in "Yawwa yanzu kuwa zan aiko Ladi dashi, godiya nake Ubana" ****** Ina labarin su Shamsiyya ne? Satin Shamsiyya d'aya a gurin Arrama kullum ta Allah zai bata wannan rubutu yace ta shafa jikinta, sai yaga ta b'ingire yazo ya kwashi gara, ya wani murmure saboda yana samun biyan buk'ata yadda ya kamata yanzu tunaninsa yaya za'ayi ya kafe Shamsiyya s gidan,Ku kuma ta dunga kawo kanta gurinsa dole sai yayi aiki a kanta. Shamsiyya duk ta rame ta figale sai uban nonowa da suka cika k'irji ta futo daga k'aramin d'akin cikin shirin tafiya tunda dama tun daran jiya yace aiki ya fara ci, saboda haka zai sallame ta amma ta dunga zuwa lokaci zuwa lokaci domin a dunga dubawa. Godiya sosai take masa, yace"Kinanan zaune zai zo gurinki yace ke yake son aura ba waccan ba" Cikin rashin dabara da wayo Shamsiyya taita zabga godiya tayi masa sallama ta tafi, tana cike da farin ciki ganin bukatat ta takusa biya ******* Lantana ce ta tafi mak'abarta da kanta Ta samo k'asar sabon kabari ta kawo aka had'a maganin kamar yadda Arrama ya bada umarni, suna sauraron dawowar Shamsiyya Shamsiyya ta dawo gida cike da farin ciki da annushuwa domin ta gazgata maganar Arrama gani take kamar ta auri Sarki! ta gama, Uwa! Taga duk ta rame ba kamar ranar da suka tafi ba, amma labarin da Shamsiyya ta bata na samun nasara yasa bata wani damu ba, suka cigaba da kulla yadda al'amarin zai kasance. Sun yanke shawarar cewar Lantana ce zataje can gidan me Martaba domin ta gabatar da aikin nata,, Shamsiyya tace" Ai naji dad'in mutuwar me Martab wallahi ko babu komai zan sake kuma ina sa ran zan auri Sarki! Domin na san d'anshi ne zai gaje shi" "Bari ke dai " yar nan, ai bake kad'ai ce kikayi farin ciki ba har damu mun kusa hutawa dai da talauci mutukar kika auri Sarki! Ai kakarmu ta yanke sak'a" Shamsiyya ta washe baki cike da farin ciki tace"Lantana ke zan fara kaiwa aikin hajji,domin ina ganin in bata dalilina ba,har ki mutu baza kije maka ba" Lantana tace"Aikuwa dai ni kaina nakan fad'i haka,wallahi wannan bak'in talaucin namu ya ishe ni" Dariya Shamsiyya tasa,, tana fad'in wai ina Babanmu ne"? Tab'e baki Uwa! Tayi tace"Gashi can a kwance yau da lafiya gobe babu, sai kace me cutar farfad'iya kullum fad'uwa miyau na zuba" Shamsiyya ta lek'a d'akin da Sallau yake kwance ta ganshi kan tabarma ko fulo babu,miyau sai dulala yake. Yana ganin ta ya d'ago mata hannu wai tazo,Shamsiyya ta mak'e kafad'a tana fad'in "Wallahi bazan zo ba Tabb! Ji wani zarni da d'akin yake,aini yau bazan kwana a d'akin nan ba, d'akin Wacan shegiyar zan bud'e in shiga in kwanciya ta" Uwa!tace"Yo ba dole kiji zarni ba idan iskancin sa ya tashi nan yake sakar min futsari ke har guntin kashi sai ki gani a jikin wandonsa sai kace wani k'aramin yaro,duk yabi ya sakwarkwace aikin banza kawai" Dariya sosai Shamsiyya take harda hawaye tana fad'in Lallai ba, tsufan ka da kallo tabdijam harka fara kashi da futsari aiko zan hayo masu jinya, domin ni bazan yi aikin kashi ba" Uwa! Taja tsaki tana watsawa Sallau harara yana cikin daki yana kallon ta yana kuma jin duk abunda suke cewa bakin ciki kamar ya kashe shi,Uwa! Ta cigaba da cewa"Ai na kunshi takaici wallahi. da kike ji daga ni ko a gado wancan uban naku babu abunda yake iya tsinana min sai dai inyi kid'ana inyi rawa ta, solob'iyo kawai,, in banda shan taba babu abunda yasa a gaba" Cikin dariya Shamsiyya tace"Tab!! Uwa! A lokacin ki kin tsula tsiyar ki. yarda kike so,ai daga ni babu sauk'i waiiii'' Uwa tayi shewa tana fad'in "Ke rabu dani dan ubanki, ko yanzu garau nake ji na,zan iya da d'an shekara goma sha bakwai ma" Shamsiyya ta zare

Table of Contents

Chapters

108 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108